Hauhawar Farashi ya ƙaru a watan Maris — NBS
Published: 15th, April 2025 GMT
Hukumar Ƙididdiga ta Nijeriya NBS ta ce hauhawar farashi ya ƙaru a ƙasar zuwa kashi 24.23 cikin 100 a watan Maris.
Alƙaluman da hukumar ta fitar sun nuna an samu ƙarin kashi 1.05 daga kashi 23.18 cikin ɗari da aka samu a watan Fabrairu.
EFCC ta gaza tabbatar da tuhumar Murja kan zargin wulaƙanta takardun kuɗi ’Yan Najeriya sun koka kan rashin ingancin shinkafar Gwamantin TarayyaWannan ne karon farko da aka samu ƙarin hauhawar farashin tun bayan da hukumar ta NBS ta soma fitar da rahoton bisa sabon tsarin tattara alƙaluma da ta fara amfani da shi a farkon shekarar nan.
Sai dai bayan soma amfanin da sabon tsarin fitar da ƙididdigar a watan jiya, NBS ta ce da wuya a iya gane haƙiƙanin raguwa ko hauhawa a yanzu.
A wani jawabi da ya yi manema labarai tun a watan da ya gabata, shugaban hukumar, Prince Adeyemi Adeniran, ya bayyana cewa sun sauya tsarin ne saboda “daidaita shi da irin na sauran ƙasashen duniya.”
Ya ce karo na ƙarshe da Nijeriya ta sauya tsarin ƙididdigar shi ne a shekarar 2009, inda ake ƙididdige farashin kayan da aka fi amfani da su a wannan tsakanin.
Hakan na nufin yanzu za a riƙa kwatanta farashin kayayyakin da aka ƙididdige daga shekarar 2024, maimakon 2009 da aka riƙa amfani da ita a baya.
A sabbin alƙaluman da NBS ta fitar, ta alaƙanta hauhawar farashin da tashin kayayyaki irinsu citta, garin rogo, shinkafa, zuma, dankali, barkono da sauransu.
Aminiya ta ruwaito cewa, Hukumar NBS ta ce alƙaluman hauhawar farashi sun koma kashi 24.48 daga 34.8 cikin 100 a watan Janairun da ya gabata.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Hauhawar Farashi Maris Nijeriya
এছাড়াও পড়ুন:
An dakatar da Shugaban Karamar Hukumar Lafia
Majalisar Dokokin Jihar Nasarawa ta dakatar da Shugaban Karamar Hukumar Lafia, Mohammed Haliru Arabo, na tsawon wata uku, kan rikicin shugabanci.
Shugaban Majalisar, Danladi Jatau, ne ya sanar da hakan a ranar Talata a Lafia, bayan Shugaban Kwamitin Majalisar kan Harkokin Kananan Hukumomi da Masarautu, Musa Ibrahim Abubakar, ya gabatar da korafi kan rikicin mulki da ke faruwa a karamar hukumar.
Jatau ya ce matakin ya zama dole domin ba da damar gudanar da bincike kan yadda ake tafiyar da mulkin karamar hukumar, wanda ya ce yana shafar zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar.
Ya bayyana cewa dakatarwar ta yi daidai da sashe na 7 da na 128 na kundin tsarin mulkin 1999 da aka yi wa kwaskwarima, wanda ya ba majalisa ikon sanya ido kan harkokin mulki.
Juyin Mulki: ECOWAS ta ayyana dokar ta-baci a kasashenta Sojoji sun kashe ’yan bindiga 13, sun ceto ’yan kasuwa a SakkwatoA cewarsa: “Domin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a Lafia, dole ne mu gudanar da bincike kan abin da ke faruwa. Bisa ikon da kundin tsarin mulki ya ba mu, shugaban karamar hukumar Lafia ya dakata na tsawon wata uku. Za a ci gaba da gudanar da harkokin karamar hukumar har sai an kammala bincike.”
Kwamitin harkokin kananan hukumomi da masarautu ya samu umarni da ya gudanar da binciken cikin wannan lokaci. A yayin dakatarwar, mataimakin shugaban karamar hukumar, Uba Arikya, zai rike ragamar mulki.
Tun da farko, Musa Ibrahim Abubakar ya gabatar da kudiri a matsayin gaggawa, inda ya nuna damuwa kan yadda aka dakatar da shugaban karamar hukumar na tsawon wata shida ba tare da bin ka’ida ba. Ya ce hakan ya saba wa kundin tsarin mulki, kuma yana haifar da rashin tabbas a siyasar yankin.
Ya jaddada bukatar majalisar jihar ta shiga tsakani domin tabbatar da gaskiya da rikon amana a harkokin kudi da mulkin karamar hukumar.
Kwamitin ya kuma bukaci majalisar ta yi nazari sosai kan lamarin domin kawo karshen rashin tabbas da rikicin da ya kunno kai a Lafia.