Aminiya:
2025-11-27@13:25:53 GMT

Hauhawar Farashi ya ƙaru a watan Maris — NBS

Published: 15th, April 2025 GMT

Hukumar Ƙididdiga ta Nijeriya NBS ta ce hauhawar farashi ya ƙaru a ƙasar zuwa kashi 24.23 cikin 100 a watan Maris.

Alƙaluman da hukumar ta fitar sun nuna an samu ƙarin kashi 1.05 daga kashi 23.18 cikin ɗari da aka samu a watan Fabrairu.

EFCC ta gaza tabbatar da tuhumar Murja kan zargin wulaƙanta takardun kuɗi ’Yan Najeriya sun koka kan rashin ingancin shinkafar Gwamantin Tarayya

Wannan ne karon farko da aka samu ƙarin hauhawar farashin tun bayan da hukumar ta NBS ta soma fitar da rahoton bisa sabon tsarin tattara alƙaluma da ta fara amfani da shi a farkon shekarar nan.

Sai dai bayan soma amfanin da sabon tsarin fitar da ƙididdigar a watan jiya, NBS ta ce da wuya a iya gane haƙiƙanin raguwa ko hauhawa a yanzu.

A wani jawabi da ya yi manema labarai tun a watan da ya gabata, shugaban hukumar, Prince Adeyemi Adeniran, ya bayyana cewa sun sauya tsarin ne saboda “daidaita shi da irin na sauran ƙasashen duniya.”

Ya ce karo na ƙarshe da Nijeriya ta sauya tsarin ƙididdigar shi ne a shekarar 2009, inda ake ƙididdige farashin kayan da aka fi amfani da su a wannan tsakanin.

Hakan na nufin yanzu za a riƙa kwatanta farashin kayayyakin da aka ƙididdige daga shekarar 2024, maimakon 2009 da aka riƙa amfani da ita a baya.

A sabbin alƙaluman da NBS ta fitar, ta alaƙanta hauhawar farashin da tashin kayayyaki irinsu citta, garin rogo, shinkafa, zuma, dankali, barkono da sauransu.

Aminiya ta ruwaito cewa, Hukumar NBS ta ce alƙaluman hauhawar farashi sun koma kashi 24.48 daga 34.8 cikin 100 a watan Janairun da ya gabata.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hauhawar Farashi Maris Nijeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Jihar Jigawa Za Ta Rufe Karbar Kudaden Aikin Hajjin 2026 Ranar 24 Ga Watan Disamba

Daga Usman Muhammad Zaria

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta bukaci maniyyatan aikin hajjin 2026 da su gaggauta biyan kudin kujerun su kafin ranar 24 ga watan gobe.

Darekta Janar na hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo ya bayyana haka jim kadan bayan kammala taro da shugabannin sassa na hukumar da shugabannin shiyya da sauran ma’aikatan hukumar a Dutse babban birnin jihar.

Yana mai cewar, hukumar aikin hajji ta kasa wato NAHCON ta bayyana ranar 5 ga watan Disamba da ta kayyade a matsayin ranar rufe biyan kudin kujerun aikin Hajjin 2026 a fadin kasar nan.

Ya bayyana cewar ranar itace ranar karshe da hukumar aikin Hajji da Umrah ta kasar Saudiyya ta kayyade na biyan kudin kujerun domin maniyyatan da za su sauke farali.

Alhaji Ahmed Umar Labbo, yayi nuni da cewar, a duk fadin kasar nan jihar Jigawa ce kadai ta sami ranar 24 ga watan gobe sakamakon karamci da Gwamna Umar Namadi ya yiwa hukumar na bada lamunin sama da naira miliyan dubu 3 domin kebe kujerun jihar a aikin Hajjin 2026.

Kazalika, ya kara da cewar babu wata jihar da ta sami karamci da tagomashi wajen alkinta kujerun maniyyata fiye da jihar Jigawa.

A don haka, Labbo ya bukaci maniyyata da su gaggauta biyan kudin kujerun su ta hannun shugabannin shiyya ko kuma a shelkwatar hukumar dake Dutse nan da makwanni 4.

Ya kuma kara jaddada kudurinsa na rike kambun hukumar wajen tabbatar da kula da jin dadin alhazai da walwalar su tun daga gida Najeriya har zuwa kasa mai tsarki.

Ahmed Umar Labbo ya yabawa Gwamna Umar Namadi bisa karamcin da yake yiwa hukumar na bada lamunin kudi domin tare kujerun alhazan jihar da sauran ayyukan hukumar domin gudanar da aikin Hajji ingantacce.

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Abubuwa 20 da ya kamata ku sani game da Sheikh Dahiru Bauchi
  • Jihar Jigawa Za Ta Rufe Karbar Kudaden Aikin Hajjin 2026 Ranar 24 Ga Watan Disamba
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Yi Wa Yara Miliyan 1.5 Rigakafin Cutar Shan Inna
  • Gwamna Namadi Ya Gabatar da Kasafin Naira Biliyan 900 ga Majalisa
  • Jarumin fina-finan Indiya Dharmendra ya rasu
  • Najeriya Ta Cimma Sabon Tsarin Hadin Gwiwa Kan Sha’anin Tsaro da Amurka