Aminiya:
2025-11-23@14:05:19 GMT

‘Tell Your Papa’: NBC ta haramta amfani da waƙar da ke sukar Tinubu

Published: 12th, April 2025 GMT

Gwamnatin Tarayya ta haramta amfani da wata sabuwar waƙar da ke sukar Shugaba Bola Tinubu a dukkanin kafofin labarai na rediyo da talabijin a faɗin ƙasar.

Waƙar da mawaƙi Eedris Abdulkareem ya fitar a baya-bayan nan mai suna“ Tell Your Papa”, ta soki yadda Shugaba Tinubu ke gudanar da tattalin arzikin Nijeriyar.

An kashe ƙasurgumin ɗan bindiga Gwaska da mayaƙa 100 a Katsina An kama mutum 8 kan faɗan daba a Kano

The lyrics are addressed to Tinubu’s son, calling on him to let his father know “people are dying” from economic hardship as well as continued insecurity from armed groups.

Baitocin waƙar da ke ɗauke da kira ga ɗan shugaban ƙasar, Seyi Tinubu, sun buƙaci ya isar wa mahaifinsa saƙon cewa ’yan Nijeriya na fama da matsanancin ƙunci na tattalin arziki da kuma matsalar tsaro.

Sai dai Hukumar Kula da Kafafen Watsa Labarai a Najeriya NBC, ta shaida wa kafofin labaran ƙasar cewa waƙar ta saɓa ƙa’ida da ma taɓa “mutuncin gwamnati.”

Tuni dai mawaƙi, Eedris Abdulkarim, ya mayar da martani, inda ya buƙaci magoya bayansa su saurari waƙar ta hanyoyin da kafar Intanet ta bayar da dama.

Abdulkareem ya wallafa a shafinsa na zumunta cewa, faɗa wa gwamnati gaskiya ko sukar gyara kayanka a kullum laifi ne a Nijeriya.

Shekaru biyu na mulkin Bola Tinubu a ƙasar dai sun gamu da zanga-zanga musamman kan tsadar rayuwa da man fetur.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Eedris Abdulkarim

এছাড়াও পড়ুন:

CORET, ECOWAS Sun Hada Matasa Da Wasu Abokan Hulda Don Inganta Kiwo Da Madara

 

Kungiyar Haɗin Kan Masu Kiwo na Gargajiya ta Afirka (CORET) tare da haɗin gwiwar ECOWAS sun hada matasan da aka horar da su da manyan abokan holda don bunkasa kiyo da bunkasa yawan madara a jihohin Kaduna da Jigawa.

 

A yayin zaman karawa juna sani a Kaduna, Koodinetan Aikin na CORET Dr. Umar Ardo Abdul, ya ce an shirya wannan zama ne domin haɗa matasan da aka horar da su da masu ruwa da tsaki a harkan kiyo da bunkasa yawan madara na gwamnati da masu zaman kansu, domin a horas da su hanyoyin samun aikin yi da kuma bunkasa yawan madara.

 

Wannan shiri na daga cikin Aikin ECOWAS na karfafa samar da ayyukan yi ga matasa da kuma bunkasa darajar madara, wanda yake ɗaukar tsawon shekaru uku, kuma an kaddamar da shi ne domin koya wa matasa ƙwarewar aiki tare da samar musu damar samun kuɗin shiga a cikin fannin kiwo.

 

Koodinetan Aikin, Dr. Umar Ardo Abdul, ya bayyana cewa an yi wa matasa 1,350 rajista a Kaduna da Jigawa.

 

A cewarsa, matasa 26 daga jihohin Kaduna da Jigawa yanzu an haɗa su da masana waɗanda za su tallafa musu a ayyukan yin allurar rigakafi da taimakon lafiyar dabbobi da aikin yaɗa ilimi, da kuma samar da kayan kiwo.

 

Ya yi bayani cewa zaman ya haɗa kwararrun likitocin dabbobi, ma’aikatan yaɗa ilimin kiwo, masu yin dasa ramin maniyyi da masu sarrafa abincin dabbobi da sauran masu ruwa da tsaki a kiwo domin gina ƙaƙƙarfan cibiyar ayyuka.

 

Dr. Umar Ardo ya ce manufar ita ce a tabbatar matasan sun yi amfani da ƙwarewar da suka samu wajen ba da muhimman ayyukan kiwo, samun kuɗin shiga, da kuma tallafawa makiyaya da manoma a yankunansu.

 

Yace ma’aikatar aikin gona ta Jihar Kaduna da Cibiyar Binciken Samar da Dabbobi ta Ƙasa (NAPRI) a matsayin muhimman abokan aikin gwamnati, yana mai cewa NAPRI cibiyar bincike ce da a ke dogaro da ita wajen binciken kiwo, samar da rigakafin dabbobi da kuma kayayyakin kiwo.

 

Koodinetan ya ce gwamnati na da muhimmiyar rawa ta tsare-tsare a fannin kiwon lafiya na dabbobi, rigakafi da kuma samar da kaji, yayin da kamfanonin masu zaman kansu ke taka rawa wajen samar da magungunan dabbobi da kayan kiwo, waɗanda suka zama ginshiƙai ga masu cin gajiyar shirin.

 

Dr. Umar Ardo ya jaddada cewa CORET, a matsayinta na ƙungiyar haɗin kan masu kiwo ta nahiyar Afirka, ta kuduri aniyar cike gibin da ke tsakanin hukumomin gwamnati, cibiyoyin bincike, kamfanoni masu zaman kansu da matasan da aka horar domin inganta harkar kiwo da bunkasa madara.

 

A nasa jawabin, wakilin Hukumar Ilimin Makiyaya ta Ƙasa, Abubakar Lawal Boro, ya ce tsarin PPP (Haɗin Gwiwar Gwamnati da Masu Zaman Kansu) shi ne ginshiƙin cigaban kiwo mai ɗorewa, domin gwamnati na samar da tsarin aiki da jagoranci, yayin da kamfanoni ke samar da muhimman kayayyaki.

Ya yi kira ga iyalan makiyaya su bai wa ilimi muhimmanci ta hanyar mayar da ‘ya’yansu makaranta, yana nuna damuwa kan yawaitar yaran da ba sa zuwa makaranta da tasirin rashin tsaro ga yunkurin wayar da kai.

 

Ɗaya daga cikin mahalarta, Anas Ibrahim, ya bayyana wannan horo a matsayin mai matuƙar amfani kuma ya zo a kan lokaci.

 

Ya ce zaman ya kasance cikin tsari kuma yana ɗaya daga cikin mafi inganci da suka halarta, inda ya faɗaɗa musu fahimtar lafiyar dabbobi, kula da abincin kiwo, da hulɗa da masu samar da ayyukan kiwo.

 

Wani mahalarta kuma, Rabiu Adamu daga Ladugga, ya yaba wa CORET da abokan aikinta bisa samar da dandalin da ya bai wa masu kiwo damar samun damar magungunan dabbobi masu inganci, abincin kiwo, da iri na kiwo da za su inganta kiwon madara.

COV: Adamu Yusuf

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ribadu Ya Gana da Sakataren Yakin Amurka Kan Batun Kashe Kiristoci A Nijeriya
  • Majalisar Dattawa A Najeriya Ta Bukaci shugaba Tinubu Ya Dauki Sojoji 100,000
  • Gwamnatin Katsina Ta Umurci a Gaggauta Rufe Dukkan Makarantun Jihar
  • Gwamnati ta ba da umarnin rufe makarantun kwana 47 a faɗin Najeriya
  • Zaman Majalisar Amurka Kan Zargin Kisan Kiristoci A Najeriya
  • CORET, ECOWAS Sun Hada Matasa Da Wasu Abokan Hulda Don Inganta Kiwo Da Madara
  • Shugabar Tanzania ta Naɗa ‘Yarta da Surikinta Ministoci a Ƙasar
  • Babu wani addini da matsalar tsaron Nijeriya ta ƙyale — Fafaroma
  • Muna roƙon Tinubu ya ƙawo ƙarshen taƙaddamar gwamnati da ASUU — Ɗalibai
  • IAEA ta buƙaci Iran ta bayyana yawan makamashin nukiliyar da ta mallaka