‘Tell Your Papa’: NBC ta haramta amfani da waƙar da ke sukar Tinubu
Published: 12th, April 2025 GMT
Gwamnatin Tarayya ta haramta amfani da wata sabuwar waƙar da ke sukar Shugaba Bola Tinubu a dukkanin kafofin labarai na rediyo da talabijin a faɗin ƙasar.
Waƙar da mawaƙi Eedris Abdulkareem ya fitar a baya-bayan nan mai suna“ Tell Your Papa”, ta soki yadda Shugaba Tinubu ke gudanar da tattalin arzikin Nijeriyar.
The lyrics are addressed to Tinubu’s son, calling on him to let his father know “people are dying” from economic hardship as well as continued insecurity from armed groups.
Baitocin waƙar da ke ɗauke da kira ga ɗan shugaban ƙasar, Seyi Tinubu, sun buƙaci ya isar wa mahaifinsa saƙon cewa ’yan Nijeriya na fama da matsanancin ƙunci na tattalin arziki da kuma matsalar tsaro.
Sai dai Hukumar Kula da Kafafen Watsa Labarai a Najeriya NBC, ta shaida wa kafofin labaran ƙasar cewa waƙar ta saɓa ƙa’ida da ma taɓa “mutuncin gwamnati.”
Tuni dai mawaƙi, Eedris Abdulkarim, ya mayar da martani, inda ya buƙaci magoya bayansa su saurari waƙar ta hanyoyin da kafar Intanet ta bayar da dama.
Abdulkareem ya wallafa a shafinsa na zumunta cewa, faɗa wa gwamnati gaskiya ko sukar gyara kayanka a kullum laifi ne a Nijeriya.
Shekaru biyu na mulkin Bola Tinubu a ƙasar dai sun gamu da zanga-zanga musamman kan tsadar rayuwa da man fetur.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Eedris Abdulkarim
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisar Mali ta ƙara wa Goita wa’adin mulkin shekara biyar
Majalisar riƙon ƙwarya ta Gwamnatin Mali ta bai wa Shugaban Mulkin Sojin ƙasar, Janar Assimi Goita, wa’adin mulki na shekara biyar, wanda za a iya sabunta shi fiye da sau daya ba tare da zaɓe ba.
A bara ne Janar Goita ya yi alƙawarin maido da mulkin dimokuradiyya a ƙasar, sai dai hakan ba ta samu ba.
Tsohon golan Super Eagles, Peter Rufai ya mutu Buhari ba ya cikin mawuyacin hali — Bashir AhmadWannan matakin ya bude hanya ga Janar Goita ya ci gaba da jagorantar kasar ta yammacin Afirka har zuwa aƙalla shekarar 2030, duk da alƙawarin da gwamnatin sojan ta yi na komawa mulkin farar hula a watan Maris na shekarar 2024.
Sai dai sabon ƙudirin dokar ya yi tanadin cewa Goita zai ci gaba da mulki har zuwa lokacin da ƙasar za ta daidaita.
Majalisar riƙon ƙwaryar wadda ke da mambobi 147, ce ta amince da ƙudirin, kuma yanzu yana jiran Janar Goita da kansa ya sa hannu domin ya zama doka.
A 2021 ne Janar Goita ya hau karagar mulkin ƙasar a wani juyin mulkin soji, inda ya alƙawarta magance tashe-tashen hankulan masu iƙirarin jihadi.
Sai dai har yanzu mayaƙan na ci gaba da ƙaddamar da hare-hare, inda a baya-bayan nan ma suka kai hare-hare kan sansanonin sojin ƙasar tare da kashe sojoji masu yawa ciki har da sojojin hayar Rasha