‘Tell Your Papa’: NBC ta haramta amfani da waƙar da ke sukar Tinubu
Published: 12th, April 2025 GMT
Gwamnatin Tarayya ta haramta amfani da wata sabuwar waƙar da ke sukar Shugaba Bola Tinubu a dukkanin kafofin labarai na rediyo da talabijin a faɗin ƙasar.
Waƙar da mawaƙi Eedris Abdulkareem ya fitar a baya-bayan nan mai suna“ Tell Your Papa”, ta soki yadda Shugaba Tinubu ke gudanar da tattalin arzikin Nijeriyar.
The lyrics are addressed to Tinubu’s son, calling on him to let his father know “people are dying” from economic hardship as well as continued insecurity from armed groups.
Baitocin waƙar da ke ɗauke da kira ga ɗan shugaban ƙasar, Seyi Tinubu, sun buƙaci ya isar wa mahaifinsa saƙon cewa ’yan Nijeriya na fama da matsanancin ƙunci na tattalin arziki da kuma matsalar tsaro.
Sai dai Hukumar Kula da Kafafen Watsa Labarai a Najeriya NBC, ta shaida wa kafofin labaran ƙasar cewa waƙar ta saɓa ƙa’ida da ma taɓa “mutuncin gwamnati.”
Tuni dai mawaƙi, Eedris Abdulkarim, ya mayar da martani, inda ya buƙaci magoya bayansa su saurari waƙar ta hanyoyin da kafar Intanet ta bayar da dama.
Abdulkareem ya wallafa a shafinsa na zumunta cewa, faɗa wa gwamnati gaskiya ko sukar gyara kayanka a kullum laifi ne a Nijeriya.
Shekaru biyu na mulkin Bola Tinubu a ƙasar dai sun gamu da zanga-zanga musamman kan tsadar rayuwa da man fetur.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Eedris Abdulkarim
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji sun yi juyin mulki a Guinea-Bissau
Sojoji a Guinea-Bissau sun ce sun yi juyin mulki tare da karɓe ragamar mulkin ƙasar.
Sun kuma sanar da dakatar da zaɓukan ƙasar tare da rufe iyakokinta nan take.
’Yan sanda sun kama masu laifi 34 a Kaduna Tukur Mamu ya karbi N50m daga kuɗin fansar harin jirgin kasan Kaduna – DSSWannan na zuwa ne kwana uku bayan ƙasar ta gudanar da zaɓen ’yan majalisa da na shugaban ƙasa.
A yau ne aka wayi gari ana ji. harbe-harbe a kusa da fadar shugaban ƙasa, lamarin da ya tashi hankalin mutane.
Daga bisani kuma dakarun soji suka rufe babban titin da ke zuwa fadar shugaban ƙasar.
A cewar majiyar AFP, sojojin sun karanta sanarwar ƙwace mulkin ƙasar a hedikwatar rundunar da ke babban birnin ƙasar, Bissau.
Cikakken rahoto na tafe…