‘Tell Your Papa’: NBC ta haramta amfani da waƙar da ke sukar Tinubu
Published: 12th, April 2025 GMT
Gwamnatin Tarayya ta haramta amfani da wata sabuwar waƙar da ke sukar Shugaba Bola Tinubu a dukkanin kafofin labarai na rediyo da talabijin a faɗin ƙasar.
Waƙar da mawaƙi Eedris Abdulkareem ya fitar a baya-bayan nan mai suna“ Tell Your Papa”, ta soki yadda Shugaba Tinubu ke gudanar da tattalin arzikin Nijeriyar.
The lyrics are addressed to Tinubu’s son, calling on him to let his father know “people are dying” from economic hardship as well as continued insecurity from armed groups.
Baitocin waƙar da ke ɗauke da kira ga ɗan shugaban ƙasar, Seyi Tinubu, sun buƙaci ya isar wa mahaifinsa saƙon cewa ’yan Nijeriya na fama da matsanancin ƙunci na tattalin arziki da kuma matsalar tsaro.
Sai dai Hukumar Kula da Kafafen Watsa Labarai a Najeriya NBC, ta shaida wa kafofin labaran ƙasar cewa waƙar ta saɓa ƙa’ida da ma taɓa “mutuncin gwamnati.”
Tuni dai mawaƙi, Eedris Abdulkarim, ya mayar da martani, inda ya buƙaci magoya bayansa su saurari waƙar ta hanyoyin da kafar Intanet ta bayar da dama.
Abdulkareem ya wallafa a shafinsa na zumunta cewa, faɗa wa gwamnati gaskiya ko sukar gyara kayanka a kullum laifi ne a Nijeriya.
Shekaru biyu na mulkin Bola Tinubu a ƙasar dai sun gamu da zanga-zanga musamman kan tsadar rayuwa da man fetur.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Eedris Abdulkarim
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu ya fasa zuwa taron G20 saboda matsalar tsaro a Najeriya
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ya dakatar da tafiyarsa zuwa Birnin Johannesburg na Afrika ta Kudu, da Luanda na Angola, sakamakon sace ɗalibai a Jihar Kebbi da kuma harin da aka kai wa masu ibada a wata coci da ke yankin Eruku a Jihar Kwara.
Tinubu, shirya barin Abuja a ranar Laraba domin halartar taron G20 karo na 20 da kuma Taron AU-EU karo na bakwai.
Sanatan Enugu ya mutu a Birtaniya ‘Yadda aka harbe mijina a gabana lokacin sace daliban Kebbi’Wannan na cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Laraba.
“Shugaban ƙasa ya umarci sojoji da ’yan sanda da su aike ƙarin jami’ai zuwa waɗannan yankuna domin a tabbatar an bi diddigin ’yan bindigar da suka kai wa masu ibada hari.”
Shugaban ya ɗage tafiyar domin samun ƙarin bayanan tsaro da ɗaukar matakan gaggawa.
Bayan neman agaji da Gwamnan Jihar Kwara ya yi, Shugaba Tinubu ya umurci jami’an tsaro da su tura ƙarin dakaru da ’yan sanda zuwa Eruku da dukkanin yankin Ƙaramar Hukumar Ekiti domin inganta tsaro.
Idan ba a manta ba ’yan bindiga sun kai wa masu ibada hari a Cocin Christ Apostolic Church a ranar Litinin.
Shugaba Tinubu na jiran cikakken rahoto daga Mataimakinsa Kashim Shettima, wanda ya kai wa al’ummar Jihar Kebbi ziyarar jaje kan sace ɗalibai mata da wasu mahara suka yi.
Hakazalika, yana jiran rahotan ’yan sanda da Hukumar DSS game da harin da aka kai a Jihar Kwara.
Onanuga, ya ƙara da cewa Shugaban Ƙasa ya damu matuƙa kan sace ɗaliban da aka yi a Jihar Kebbi.
“Shugaba Tinubu ya bayyana a fili cewa dole ne a yi duk mai yiwuwa domin ceto ɗalibai 24 da aka sace tare da dawo da su gida lafiya,” in ji shi.
Fadar Shugaban Ƙasa ta ce kiyaye rayukan ’yan Najeriya shi ne babban abin da shugaban ƙasa ya fi mayar da hankali a kai.
A cewar fadar wannan ne dalilin da ya sa ya ɗage tafiyarsa don mayar da hankali kan inganta tsaro a yankunan da abin ya shafa.