Fiye Da Mutane 20 Ne Su Ka Yi Shahada Sanadiyyar Hare-haren Amurka Da Birtaniya Akan Kasar Yemen
Published: 16th, March 2025 GMT
Da safiyar yau Lahadi, sojojin Amurka da Birtaniya sun ci gaba da kai wa kasar Yemen hare-hare, inda a bayan nan su kai wasu jerin hare-hare guda uku.
Yankunan da hare-haren na Amurka da Birtaniya su ka shafa a cikin Yemen sun hada “ali Sabba”, dake gundumar Sahhar, da hakan ya yi sanadiyyar kashe daruruwan dabbobi.
Haka nan kuma sojojin na Amurka sun kai wasu hare-haren a gabashin Majzar, dake gundunar “Ma’arib”.
Tun da marecen Asabar ne dai sojojin na Amurka su ka shelanta kai wa Yemen hare-hare a biranen San’aa,Sa’adah, da Zammar.
A birnin Sa’adah, kananan yara 4 sun yi shahada sai kuma wata mace, yayin da wasu mutane fiye da 10 su ka jikkata.
Wasu yankunan da hare-haren na Amurka su ka shafa sun hada da yankunan Mikra da kuraishiyya a gundumar Baidha’a.
A yankin Jarf, dake birnin San’aa mutane 9 ne su ka yi shahada.
Tashar talabijin din ‘almasirah’ ta kasar Yemen ta bayar da labarin dake cewa jumillar wadanda su ka yi shahada sun kai 24, 14 daga cikinsu a birnin Sanaa,sai kuma 10 a Sa’adah. Haka nan wani adadin da ya kai 23 sun jikkata.
Kungiyar Ansarullah ta Yemen ta jaddada ci gaba da kai wa jiragen ruwan HKI hare-hare a ruwan “Red sea” har zuwa lokacind a za a kawo karshen hana shigar da kayan agaji ga mutanen Gaza masu azumin Ramadan.
Daga marecen jiya Asabar zuwa tsakar dare, sau 30 Amurka da Birntaniyan su ka kai wa Yemen hare-hare.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Makaman ‘Drons’ Na Yemen Sun Fada Kan Wurare Masu Muhimmanci A HKI
Jaragen yaki wadanda ake sarrafasu daga nesa wato Drones sun fada kan wurare masu muhimmanci a kudancin kasar Falasdinu da aka mamaye, yan sa’o’in da suka gabata.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto kakakin sojojin kasar Yemen Burgediya Janar Yahyah Saree yana fadar haka a dazo-dazon nan .Ya kumakara da cewa. hare-haren sun hada da Drons guda 4, 3 daga cikinsu sun fada kan tashar jiragen sama na Ramon da ke kusa da Ummu Rash-rash ko Ilat kamar yaddayahudawan suke kiransa. Sannan guda kumaya fada kan sansanin sojojin HKI na Negev duk a kudancin kasar.
Ya ce an kai hare-haren ne don goyon bayan Falasdinawa wadanda HKI take kashewa tunkimani shekaru biyu da suka gabata. Sannan sanarwan ta kara da cewa hare-haren zasucigaba matukar an ci gaba da yaki a Gaza.
Ya zuwa yanzudai sojojinyahudawan sun kashe Falasdinawa kimani 65,000. Tun daga cikin watan octonan shekara ta 2023.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila September 16, 2025 Ministan Tsaron Venezuela Ya Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Juyin Mulki A Kasar September 16, 2025 Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya September 16, 2025 Bayanin Bayan Taron Doha Ya Yi Kira Da A Kafa Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kare Kai September 15, 2025 Fira Ministan Spain: Bai Kamata A Rika Barin “Isr’ila” Tana Shiga Gasar September 15, 2025 Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Sarkin Kasar Qatar A Birnin Doha September 15, 2025 Dan Kasar Iran Mai Kirkira Ya Sami Kyautar Yabo A Kasar China September 15, 2025 Fizishkiyan: Wajibi Ne Musulmi Su Hada Kai Domin Dakatar Da Laifukan HKI September 15, 2025 Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha September 15, 2025 Kwamitin Kolin Tsron Kasar Iran Ya Amince Da Yarjejeniyar Da Aka Cimma Da Hukumar IAEA September 15, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci