Gwamnatin Jigawa Za Ta Hada Gwiwa Da Jami’ar Azman Don Inganta Ilimi A Jihar
Published: 13th, March 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Jigawa za ta kulla haɗin gwiwa mai muhimmanci da Jami’ar Azman domin faɗaɗa damar ilimi da inganta ci gaban al’ummar jihar.
An bayyana hakan ne lokacin da shugabannin Jami’ar Azman, karkashin jagorancin Shugabar Jami’ar, Farfesa Fatima Batul Mukhtar, suka kai ziyarar ban girma ga Gwamna Umar Namadi a Fadar Gwamnati da ke Dutse.
Wannan haɗin gwiwa yana da nufin tallafawa sabbin hanyoyin koyarwa, da daukar nauyin dalibai a wasu shirye-shirye na musamman, da kuma inganta basirar matasa a muhimman fannoni kamar lissafi da kwamfuta, da kimiyyar bayanai, da sarrafa harkokin jiragen sama, da sauransu.
Yayin da take jawabi, Shugabar Jami’ar ta nuna godiya ga jajircewar gwamnatin jihar wajen bunkasa ilimi, tare da jaddada aniyar jami’ar wajen samar da inganci da kirkire-kirkire.
Ta kuma yi kira ga gwamnatin jihar da ta hada kai da jami’ar wajen shirye-shiryen horar da matasa da ba su takardun shaidar ƙwarewa, musamman a bangaren shirye-shiryen kwamfuta, tare da manyan kamfanoni irin su Cisco, Huawei, da Oracle Academy.
“Mai Girma Gwamna, Jami’ar Azman ta riga ta samu ci gaba a shirye-shiryen kwamfuta, domin mun yi rijista da Cisco, Huawei, da Oracle Academy, kuma muna da malamai da ke da takardar shaidar koyarwa daga Huawei. Saboda haka, muna rokon ku da ku duba yiwuwar yin haɗin gwiwa da mu a shirye-shiryen takardun shaidar ƙwarewa a bangaren shirye-shiryen kwamfuta.”
Shugabar Jami’ar ta kuma yaba wa gwamnatin jihar bisa jajircewarta a fannin ilimi, musamman ware kaso 32 bisa dari na kasafin kudin 2024 ga bangaren ilimi da kuma ƙarin naira biliyan uku da aka ƙara wa Hukumar Tallafin Karatu ta Jihar Jigawa.
A nasa martanin, Gwamna Namadi ya nuna matuƙar godiya ga ƙoƙarin Jami’ar Azman tare da yabawa shugabancin Farfesa Fatima Batul Mukhtar.
Gwamnan ya kuma jaddada muhimmancin shirye-shiryen musamman da jami’ar ke bayarwa, tare da tabbatar da cewa gwamnatin jihar tana da shirin daukar nauyin wasu dalibanta domin su yi karantu a bangarorin da babu a sauran makarantu a jihar.
“Sabbin kwasa-kwasan da kuka kirkiro suna da kyau, kuma hakan zai jawo hankalin dalibai da malamai zuwa jami’ar.
Wannan na daga cikin dalilan da suka sa na ga babbar dama a wannan jami’a. Kwasa-kwasan da kuka ambata suna da matukar muhimmanci, musamman a yankunan da basu dawannan taarin karatu.”
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jami ar Azman Jigawa gwamnatin jihar shirye shiryen Jami ar Azman shirye shirye
এছাড়াও পড়ুন:
Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Kashe Sama da Naira Miliyan 5 Don Tallafawa Shirin AGILE
Daga Usman Muhammad Zaria
Shugaban ƙaramar hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dr. Builder Muhammad Uba, ya aiwatar da wani aiki na da naira miliyan biyar domin tallafa wa aiwatar da Shirin Tallafawa Yara Mata (AGILE) a yankin.
Aikin ya hada da gyaran ajujuwa biyu da samar da muhimman kayan aiki, ciki har da injunan dinki, injin yin surfani wato (monogram) da shirin AGILE ya bayar kyauta wanda Dr. Uba ya shirya, ya taimaka wajen ganin an fara amfani da shi, tare da samar da janareta da tabarmi domin inganta koyarwa da horo.
Wannan ci gaban ya biyo bayan wani bincike da tawagar AGILE ta jihar Jigawa ta gudanar a baya, inda ta bayyana cewa wuraren koyon sana’o’in na bukatar gyara.
Shirin AGILE, wani shiri ne na Gwamnatin Tarayya tare da hadin gwiwar Gwamnatin Jihar Jigawa, wanda aka ƙirƙira domin bai wa matasa mata ƙwarewar da za su dogara da kansu, inda ake sa ran mutum 50 za su amfana a horon da ke tafe.
A lokacin ƙaddamar da aikin, Mai kula da shirin AGILE a Birnin Kudu, Hajiya Maryam Hassan Jibrin, ta yaba da jajircewar Dr. Builder Uba ga ci gaban al’umma, tana jinjinawa kokarinsa tare da yi masa addu’ar ci gaba da jagoranci mai tasiri.
Da yake tabbatar da jajircewar gwamnatinsa wajen ci gaban matasa, Muhammad Uba ya yi alƙawarin bayar da gagarumin tallafi ga mahalarta bayan kammala shirin cikin nasara.