Gwamnatin Jigawa Za Ta Hada Gwiwa Da Jami’ar Azman Don Inganta Ilimi A Jihar
Published: 13th, March 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Jigawa za ta kulla haɗin gwiwa mai muhimmanci da Jami’ar Azman domin faɗaɗa damar ilimi da inganta ci gaban al’ummar jihar.
An bayyana hakan ne lokacin da shugabannin Jami’ar Azman, karkashin jagorancin Shugabar Jami’ar, Farfesa Fatima Batul Mukhtar, suka kai ziyarar ban girma ga Gwamna Umar Namadi a Fadar Gwamnati da ke Dutse.
Wannan haɗin gwiwa yana da nufin tallafawa sabbin hanyoyin koyarwa, da daukar nauyin dalibai a wasu shirye-shirye na musamman, da kuma inganta basirar matasa a muhimman fannoni kamar lissafi da kwamfuta, da kimiyyar bayanai, da sarrafa harkokin jiragen sama, da sauransu.
Yayin da take jawabi, Shugabar Jami’ar ta nuna godiya ga jajircewar gwamnatin jihar wajen bunkasa ilimi, tare da jaddada aniyar jami’ar wajen samar da inganci da kirkire-kirkire.
Ta kuma yi kira ga gwamnatin jihar da ta hada kai da jami’ar wajen shirye-shiryen horar da matasa da ba su takardun shaidar ƙwarewa, musamman a bangaren shirye-shiryen kwamfuta, tare da manyan kamfanoni irin su Cisco, Huawei, da Oracle Academy.
“Mai Girma Gwamna, Jami’ar Azman ta riga ta samu ci gaba a shirye-shiryen kwamfuta, domin mun yi rijista da Cisco, Huawei, da Oracle Academy, kuma muna da malamai da ke da takardar shaidar koyarwa daga Huawei. Saboda haka, muna rokon ku da ku duba yiwuwar yin haɗin gwiwa da mu a shirye-shiryen takardun shaidar ƙwarewa a bangaren shirye-shiryen kwamfuta.”
Shugabar Jami’ar ta kuma yaba wa gwamnatin jihar bisa jajircewarta a fannin ilimi, musamman ware kaso 32 bisa dari na kasafin kudin 2024 ga bangaren ilimi da kuma ƙarin naira biliyan uku da aka ƙara wa Hukumar Tallafin Karatu ta Jihar Jigawa.
A nasa martanin, Gwamna Namadi ya nuna matuƙar godiya ga ƙoƙarin Jami’ar Azman tare da yabawa shugabancin Farfesa Fatima Batul Mukhtar.
Gwamnan ya kuma jaddada muhimmancin shirye-shiryen musamman da jami’ar ke bayarwa, tare da tabbatar da cewa gwamnatin jihar tana da shirin daukar nauyin wasu dalibanta domin su yi karantu a bangarorin da babu a sauran makarantu a jihar.
“Sabbin kwasa-kwasan da kuka kirkiro suna da kyau, kuma hakan zai jawo hankalin dalibai da malamai zuwa jami’ar.
Wannan na daga cikin dalilan da suka sa na ga babbar dama a wannan jami’a. Kwasa-kwasan da kuka ambata suna da matukar muhimmanci, musamman a yankunan da basu dawannan taarin karatu.”
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jami ar Azman Jigawa gwamnatin jihar shirye shiryen Jami ar Azman shirye shirye
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 6, sun raunata wasu a Kwara
Aƙalla jami’an tsaro shida ne suka rasu bayan wata arangama da suka yi da ’yan bindiga a yankin Gada Woro a kan hanyar Patigi da ke Ƙaramar Hukumar Edu a Jihar Kwara.
Waɗanda suka rasu sun haɗa da ’yan banga guda biyar da ɗan sanda ɗaya.
‘Mutum 600 da suka bace a ambaliyar Mokwa sun mutu’ Lakurawa sun kashe mutum 15 a harin ramuwar gayya a SakkwatoWasu sojoji biyu, ’yan sanda biyu sun samu raunin harbin bindiga a fafatawar da ta faru a ranar Litinin.
Waɗanda suka rasu sun haɗa da Mohammed Nma Dsuru daga Kokodo, Yanda daga Lafiagi, da Ndagi Saraka daga Edogi.
Rahotanni sun ce ’yan bindigar da yawansu ya kai ɗaruruwa sun kai wa tawagar jami’an tsaro farmaki a cikin daji, inda aka yi ta musayar wuta.
Wasu daga cikin waɗanda suka jikkata an kai su Asibitin Koyarwa na Jami’ar Ilorin (UITH) domin samun kulawa.
Wani bidiyo da ya karaɗe shafukan sada zumunta ya nuna yadda aka fafata a dajin.
Wasu mazauna yankin sun ce lamarin ya fara ne a ranar Asabar, lokacin da aka sace wani fitaccen mai sayar da magungunan gona wanda ya dawo daga aikin Hajji.
’Yan bindigar sun shigo da babura, suka shiga gidansa da ke unguwar Taiwo da misalin ƙarfe 1 na dare sannan suka tafi da shi.
A ranar Lahadi, sun sake kai wani hari inda suka sace ɗan kasuwa mai sana’ar POS, Alhaji Yaman da wani mutum mai suna Usman.
’Yan banga sun samu nasarar ceto mutum ɗaya daga cikinsu.
Wasu daga cikin al’ummar yankin na zargin cewa wasu mazauna garin na taimaka wa ’yan bindigar a ɓoye, duba da cewa yawancin waɗanda aka sace matasa ne kuma fitattun ’yan kasuwa a yankin.
An yi ƙoƙarin jin ta bakin kakakin ’yan sandan jihar, Adetoun Ejire Adeyemi, amma ba ta ɗauki waya ko amsa saƙon da aka aike mata ba.