Gwamnatin Jigawa Za Ta Hada Gwiwa Da Jami’ar Azman Don Inganta Ilimi A Jihar
Published: 13th, March 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Jigawa za ta kulla haɗin gwiwa mai muhimmanci da Jami’ar Azman domin faɗaɗa damar ilimi da inganta ci gaban al’ummar jihar.
An bayyana hakan ne lokacin da shugabannin Jami’ar Azman, karkashin jagorancin Shugabar Jami’ar, Farfesa Fatima Batul Mukhtar, suka kai ziyarar ban girma ga Gwamna Umar Namadi a Fadar Gwamnati da ke Dutse.
Wannan haɗin gwiwa yana da nufin tallafawa sabbin hanyoyin koyarwa, da daukar nauyin dalibai a wasu shirye-shirye na musamman, da kuma inganta basirar matasa a muhimman fannoni kamar lissafi da kwamfuta, da kimiyyar bayanai, da sarrafa harkokin jiragen sama, da sauransu.
Yayin da take jawabi, Shugabar Jami’ar ta nuna godiya ga jajircewar gwamnatin jihar wajen bunkasa ilimi, tare da jaddada aniyar jami’ar wajen samar da inganci da kirkire-kirkire.
Ta kuma yi kira ga gwamnatin jihar da ta hada kai da jami’ar wajen shirye-shiryen horar da matasa da ba su takardun shaidar ƙwarewa, musamman a bangaren shirye-shiryen kwamfuta, tare da manyan kamfanoni irin su Cisco, Huawei, da Oracle Academy.
“Mai Girma Gwamna, Jami’ar Azman ta riga ta samu ci gaba a shirye-shiryen kwamfuta, domin mun yi rijista da Cisco, Huawei, da Oracle Academy, kuma muna da malamai da ke da takardar shaidar koyarwa daga Huawei. Saboda haka, muna rokon ku da ku duba yiwuwar yin haɗin gwiwa da mu a shirye-shiryen takardun shaidar ƙwarewa a bangaren shirye-shiryen kwamfuta.”
Shugabar Jami’ar ta kuma yaba wa gwamnatin jihar bisa jajircewarta a fannin ilimi, musamman ware kaso 32 bisa dari na kasafin kudin 2024 ga bangaren ilimi da kuma ƙarin naira biliyan uku da aka ƙara wa Hukumar Tallafin Karatu ta Jihar Jigawa.
A nasa martanin, Gwamna Namadi ya nuna matuƙar godiya ga ƙoƙarin Jami’ar Azman tare da yabawa shugabancin Farfesa Fatima Batul Mukhtar.
Gwamnan ya kuma jaddada muhimmancin shirye-shiryen musamman da jami’ar ke bayarwa, tare da tabbatar da cewa gwamnatin jihar tana da shirin daukar nauyin wasu dalibanta domin su yi karantu a bangarorin da babu a sauran makarantu a jihar.
“Sabbin kwasa-kwasan da kuka kirkiro suna da kyau, kuma hakan zai jawo hankalin dalibai da malamai zuwa jami’ar.
Wannan na daga cikin dalilan da suka sa na ga babbar dama a wannan jami’a. Kwasa-kwasan da kuka ambata suna da matukar muhimmanci, musamman a yankunan da basu dawannan taarin karatu.”
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jami ar Azman Jigawa gwamnatin jihar shirye shiryen Jami ar Azman shirye shirye
এছাড়াও পড়ুন:
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (2)
Tsarin ilimin da ba sai an je makaranta ba
Irin wannan nau’in ilmin shi ba tsara shi ake yi ba, hakanan ma ba yana bin wani abinda aka shirya bane dangane da koyarwar. Irin wannan ilimin baya bukatar wani adoI wato ilimin da a ciukin ajin dake makaranta ake koyon shi ba. A waje n eake koyon shi wato manufa ba a wata makaranta ba wadda ake koyarwa domin a samu shi ilimin. Wannan kuma yana faruwa ne idan mutane suka samu karuwa da wasu dabaru ko ilimi daga gida, dakin karatu, ko kum wata kafar sadarwa ta na’urar waya da duk wani abinda za’a iya amfani da shi domin hakan.Bugu da kari irin wannan ilimin ana iya samun shi daga wurin Shugabannin al’umma.
Kasancewa cikn al’umma ta wannan hanya ko waccan irin hakan ma wata hanya ce da mutum yake karuwa da nau’in ilimin da ba sai an je makaranta ba an zauna, a aji. Irin wadancan Malaman ai Iyaye ne, ‘yan’uwa, da kuma makwabta, da wasu al’umma wadanda su sun koya ne daga irin dabarun da suka koya a rayuwa,daga iri yadda mutum zai sa kaya/sutura da anau’oin Bukukuwa ko wasu raturruka, yadda za a sayo abubuwan hadawa ayi abinci,da kuma yadda za’a lura da tsaftar jiki.
Sai dai kuma akwai wasu abubuwan da suke nasaba da yadda al’adu suke yaduwa,yayin da abin kan faru ta wani yanayin da ba ayi tsammani ba,yana iya kasancewa irin ilimin a ake karuwa da shi ba sai an je makaranta ba.Ya dangata ko dogara da yadda al’umma suke tafiyar da al’adunsu,yadda suke yi na’am da su,da kuma yadda halayen zamantakewa suke.
Ilimin da ya hada da nau’oin ilimi biyu
Shi iri wannan nau’in ilimin ya sha bamban da guda biyun domin abin ya danganta ne da irin salon da yake tafe da ita koyarwar ta kunsa.Shi yana da irin na shi tsarin kai tsaye kuma,amma shi ma ba a makaranta ba ake iya koyon shi ba.Akwai tsarin yadda yake wanda ba mai rikitarwa ba,babu kuma wani lamarin kayyade shekaru.
Alal misali akwai irin wuraren da ake koyon shi wadanda suka bambanta da guda biyun, koyon sana’oi wuraren da ake koyar da su, tsarin horarwa mai gajeren zango,irin na Shugabannin Kamfanoni wadanda ba wai sai kwararru ba wadanda suka samu ilimin ta irin nau’in ilimin da ake koyar da shi a cikin aji.
Me yasa ilimi yake da muhimmanci?
Me yasa ilimi yake da muhimmanci?Ilimi yana da muhimmanci saboda dalilai masu yawa. Ta hanyar ilimi mutane/ al’umma suna koyon yadda za suyi karatu, rubutu, da kuma saurare. Gaba daya lamarin ilim har ya kunshi rayuwar abubuwan da mutum yake son cimmawa a gaba.Mutanen da suke da ilimi mai zurfi irin sune ake rubibinsu a wuraren da ake daukar ma’aikata inda kuma albashinsu ya kan kasance mai tsoka. (Abulencia, 2021) Hakananma shi ilimi yana maganin fatara, da yunwa, inda yake bada damar yadda mutum zai samu ci gaba. Irin hakan ce ta sa Iyaye suke kokarin sai ‘ya’yansu sun je makaranta, yayin da ita kuma gwamnati take taimakawa ta hanyoyin da za su sa dukkanin yara da manya sun samu da karuwa da ilimin. (UNESCO, 2011)
Bayan haka ma ilimi yana taimakawa ‘yanmata da mata wajen samun dama wadda ba za a samu rata mai yaw aba tsakaninsu da maza.Ta haka ne aka samu rage yawan yaran mata kanana ke daukar ciki da kashi 6 cikin 100, saboda karun shekarun da ‘ya’ya mata suke yi wajen karatu kamar yadda Bankin duniya ya bayyana.Ita ma Hukumar dake karkashin majalisar dinkin duniya da ake kira UNESCO,mai kula da lamurran ilimi, kimiyya, da kuma al’adu ta gano cewa jaririn da mahaifiyarsa ta iya karatu yana kashi 50 na yiyuwar samun damar kaiwa har zuwa shekara biyar,wannan ya nuna ilimi ya taimaka wajen irin yadda kananan yara suke mutuwa kafin su kai shekara biyar.
Sai dai kuma wani nazarin da aka yi ya nuna an samu koma- baya wajen samun amsar tambayar me yasa ilimi yake da muhimmanci ga samun nasara? A wani rubutu mai taken “Amfanin abokantaka /’yan’uwantaka tsakanin ilimi da tattalin arziki,halayya da kuma matsayin abin a siyasance wanda”International Journal of Social and Management Studies,Deak and Tanama ya wallafa, a shekarar(2021)ya bayyana cewa “Idan aka samu matsalar rashin yin shiri da tsarin ilimi wanda ya kamata yana sanadiyar haifar da manyan matsalolin da suke da amfani idan tun farko an yi su saboda kaucewa aukuwar irin hakan: rashin aikin yi,aikata laifuka,shan muggan kwayoyi,idan ana maganar ci gaban gwamati ne ta bangaren tattalin arziki,a hanyoyi da dama hakan ya ta’allaka ne kan taimakon da take samu daga kimiyya da kuma fasaha.’’Don haka shi yasa ilimi yake da amfani/ muhimmanci ga ko wadanne al’umma,da daidaikun mutane’’.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp