Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-09-17@23:17:25 GMT

Tambuwal Ya Raba Shinkafa Ga Gidaje Dubu 30 A Sokoto

Published: 13th, March 2025 GMT

Tambuwal Ya Raba Shinkafa Ga Gidaje Dubu 30 A Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto, Sanata Aminu Waziri Tambuwal ya kaddamar da rabon shinkafa da sauran kayayyaki ga gidaje sama da 30,000 dake fadin kananan hukumomi 23 na jihar.

 

Da yake kaddamar da rabon a Sokoto, Sanata Tambuwal ya nuna godiya ga Allah Madaukakin Sarki da ya sake ganin watan Azumin Ramadan tare da tabbatar da ganin an gudanar da Ramadan cikin kwanciyar hankali.

 

Ya jaddada mahimmancin tunani, karamci da addu’o’in ci gaba da lafiya da wadata.

 

Tambuwal wanda shi ne Sanata mai wakiltar Sokoto ta Kudu a jam’iyyar PDP ya ce wannan shiri na kara jaddada kudurin jam’iyyar na hadin kai, tausayi da goyon bayan al’umma a cikin wannan wata mai alfarma.

 

Ya yaba da jajircewar da jagororin jam’iyyar PDP a jihar Sakkwato suke yi, inda ya bayyana irin kokarin da suke yi na tsari, hada kai da kuma karfafa jam’iyyar.

 

Sanata Tambuwal ya jaddada kudirin sa na hadin kan jam’iyyar, inda ya bayyana aniyarsa ta dawo da aikinsu bayan zabukan da suka gabata.

 

Tsohon Gwamna Tambuwal ya kara yabawa ‘yan majalisar da aka zaba karkashin jam’iyyar PDP bisa jajircewarsu wajen yi wa mazabarsu hidima.

 

Ya yaba da yadda suke tafiyar da harkokinsu na gaskiya da kuma jagoranci na gaskiya, wanda ke nuna jajircewarsu na tabbatar da romon dimokuradiyya ga jama’arsu.

 

 

Ya kuma bukaci wadanda ke da alhakin rabon tallafin da su tabbatar da cewa tallafin ya isa ga wadanda suka amfana, kamar yadda aka tsara.

 

Tun da farko, shugaban jam’iyyar PDP na jihar, Bello Muhammad Goronyo, ya godewa Sanata Tambuwal bisa wannan karimcin da ya ce zai taimaka matuka wajen rage wahalhalun da ke tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar a jihar.

 

Goronyo ya kara neman hadin kai a tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar domin ganin an samu gagarumin rinjaye a zaben 2027 a dukkan matakai.

 

 

 

NASIR MALALI

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Tambuwal jam iyyar PDP Tambuwal ya Tambuwal Ya

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Ambaliyar ruwa na cigaba da salwantar da dukiyoyi da rayukan al’ummomi da dama a sassa daban-daban na Najeriya.

 

Ko a farkon makon nan, hukumomi sun yi gargadin cewa akwai yiwuwar samun ambaliyar a jihohi akalla 11.

Sai dai wasu alummomin tuni suka dauki matakai don rage barnar da ambaliyar ka iya yi musu.

NAJERIYA A YAU: Masu Nau’in Jinin AS Sun Fi Masu Nau’in AA Lafiya DAGA LARABA: Dalilan Da Suka Sa Nayi Yunkurin Kashe Kaina Har Sau Uku

A kan wadannan matakai shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Za A Kada Kuri’ar Raba Gardama Akan Sabon Tsarin Mulki A Kasar Guinea
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • Iran Ta Bayyana Abubuwan Da Bata Amince Da Su Ba A Jawabin Bayan Taro Na Kungiyar OIC A Birnin Doha
  • Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu
  • ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa
  • Kundin Bajinta na Guinness ya taya Hilda Baci murna
  • KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa