Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-11-03@03:00:07 GMT

Tambuwal Ya Raba Shinkafa Ga Gidaje Dubu 30 A Sokoto

Published: 13th, March 2025 GMT

Tambuwal Ya Raba Shinkafa Ga Gidaje Dubu 30 A Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto, Sanata Aminu Waziri Tambuwal ya kaddamar da rabon shinkafa da sauran kayayyaki ga gidaje sama da 30,000 dake fadin kananan hukumomi 23 na jihar.

 

Da yake kaddamar da rabon a Sokoto, Sanata Tambuwal ya nuna godiya ga Allah Madaukakin Sarki da ya sake ganin watan Azumin Ramadan tare da tabbatar da ganin an gudanar da Ramadan cikin kwanciyar hankali.

 

Ya jaddada mahimmancin tunani, karamci da addu’o’in ci gaba da lafiya da wadata.

 

Tambuwal wanda shi ne Sanata mai wakiltar Sokoto ta Kudu a jam’iyyar PDP ya ce wannan shiri na kara jaddada kudurin jam’iyyar na hadin kai, tausayi da goyon bayan al’umma a cikin wannan wata mai alfarma.

 

Ya yaba da jajircewar da jagororin jam’iyyar PDP a jihar Sakkwato suke yi, inda ya bayyana irin kokarin da suke yi na tsari, hada kai da kuma karfafa jam’iyyar.

 

Sanata Tambuwal ya jaddada kudirin sa na hadin kan jam’iyyar, inda ya bayyana aniyarsa ta dawo da aikinsu bayan zabukan da suka gabata.

 

Tsohon Gwamna Tambuwal ya kara yabawa ‘yan majalisar da aka zaba karkashin jam’iyyar PDP bisa jajircewarsu wajen yi wa mazabarsu hidima.

 

Ya yaba da yadda suke tafiyar da harkokinsu na gaskiya da kuma jagoranci na gaskiya, wanda ke nuna jajircewarsu na tabbatar da romon dimokuradiyya ga jama’arsu.

 

 

Ya kuma bukaci wadanda ke da alhakin rabon tallafin da su tabbatar da cewa tallafin ya isa ga wadanda suka amfana, kamar yadda aka tsara.

 

Tun da farko, shugaban jam’iyyar PDP na jihar, Bello Muhammad Goronyo, ya godewa Sanata Tambuwal bisa wannan karimcin da ya ce zai taimaka matuka wajen rage wahalhalun da ke tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar a jihar.

 

Goronyo ya kara neman hadin kai a tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar domin ganin an samu gagarumin rinjaye a zaben 2027 a dukkan matakai.

 

 

 

NASIR MALALI

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Tambuwal jam iyyar PDP Tambuwal ya Tambuwal Ya

এছাড়াও পড়ুন:

An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m

Rundunar ’yan sandan Jihar Borno ta raba zunzurutun kuɗi naira miliyan 63.4 ga iyalan jami’anta 84 da suka rasa rayukansu a bakin aiki.

Rundunar ta raba kudin ne a ƙarƙashin tsarin inshorar rayuwa da kuma tsarin kula da lafiyar iyali na Sufeto Janar na ’yan sanda.

 

An gudanar da rabon kuɗin ne a ranar Alhamis a Maiduguri babban birnin jihar kamar yadda Kakakin rundunar a jihar, ASP Nahum Kenneth Daso, ya bayyana a cikin wata sanarwa.

A cewar sanarwar, Kwamishinan ‘yan sanda na jihar, CP Naziru Abdulmajid, wanda ya wakilci Sufeto Janar na ‘yan sanda, IGP Kayode Egbetokun, shi ne ya gabatar da takardun cakin kudin ga iyalan waɗanda suka ci gajiyar tallafin.

“Harkokin da suka shafi jami’anmu da iyalansu ya kasance babban fifiko ga rundunar,” in ji CP Abdulmajid yayin taron.

Ya ce wannan shiri na nuna tausayi da rikon amana, da kuma jagoranci mai nagarta daga Sufeto Janar wajen girmama jaruman da suka sadaukar da rayukansu domin tabbatar da zaman lafiya da tsaron ƙasa.

Kwamishinan ya kuma yi kira ga iyalan da suka amfana da tallafin da su yi amfani da kuɗaɗen yadda ya dace, musamman wajen tallafa wa ilimi, kiwon lafiya, da jin daɗin rayuwar iyalansu gaba ɗaya.

Ya yaba wa Sufeto Janar bisa ci gaba da tsare-tsaren jin daɗin jami’an rundunar, yana mai bayyana su a matsayin muhimman hanyoyin da ke samar da agaji da kwanciyar hankali ga iyalan waɗanda suka rasa masoyansu.

A nata jawabin a madadin iyalan da suka amfana, Misis Nana Goni ta nuna godiya ga Sufeto Janar bisa goyon bayan da ya bayar, tana mai tabbatar da cewa za su yi amfani da kuɗaɗen yadda ya kamata don inganta rayuwar iyalansu.

Rundunar ta bayyana cewa wannan rabon tallafi ya sake tabbatar da jajircewarta wajen kula da walwala da mutuncin jami’anta da iyalansu, musamman waɗanda suka sadaukar da rayukansu wajen kare al’umma.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik
  • Araqchi: Da Hadin Bakin Amurka, Gwamnatin Isra’ila ta kaddamar Da Hari Kan Kasar Iran
  • Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
  • Rikicin PDP: Tsagin Wike ya dakatar da Damagum
  • Dan Majalisar Jema’a/Sanga, Daniel Amos, Ya Koma Jam’iyyar APC
  • Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC
  • An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m