Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-03-28@08:59:26 GMT

Tambuwal Ya Raba Shinkafa Ga Gidaje Dubu 30 A Sokoto

Published: 13th, March 2025 GMT

Tambuwal Ya Raba Shinkafa Ga Gidaje Dubu 30 A Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto, Sanata Aminu Waziri Tambuwal ya kaddamar da rabon shinkafa da sauran kayayyaki ga gidaje sama da 30,000 dake fadin kananan hukumomi 23 na jihar.

 

Da yake kaddamar da rabon a Sokoto, Sanata Tambuwal ya nuna godiya ga Allah Madaukakin Sarki da ya sake ganin watan Azumin Ramadan tare da tabbatar da ganin an gudanar da Ramadan cikin kwanciyar hankali.

 

Ya jaddada mahimmancin tunani, karamci da addu’o’in ci gaba da lafiya da wadata.

 

Tambuwal wanda shi ne Sanata mai wakiltar Sokoto ta Kudu a jam’iyyar PDP ya ce wannan shiri na kara jaddada kudurin jam’iyyar na hadin kai, tausayi da goyon bayan al’umma a cikin wannan wata mai alfarma.

 

Ya yaba da jajircewar da jagororin jam’iyyar PDP a jihar Sakkwato suke yi, inda ya bayyana irin kokarin da suke yi na tsari, hada kai da kuma karfafa jam’iyyar.

 

Sanata Tambuwal ya jaddada kudirin sa na hadin kan jam’iyyar, inda ya bayyana aniyarsa ta dawo da aikinsu bayan zabukan da suka gabata.

 

Tsohon Gwamna Tambuwal ya kara yabawa ‘yan majalisar da aka zaba karkashin jam’iyyar PDP bisa jajircewarsu wajen yi wa mazabarsu hidima.

 

Ya yaba da yadda suke tafiyar da harkokinsu na gaskiya da kuma jagoranci na gaskiya, wanda ke nuna jajircewarsu na tabbatar da romon dimokuradiyya ga jama’arsu.

 

 

Ya kuma bukaci wadanda ke da alhakin rabon tallafin da su tabbatar da cewa tallafin ya isa ga wadanda suka amfana, kamar yadda aka tsara.

 

Tun da farko, shugaban jam’iyyar PDP na jihar, Bello Muhammad Goronyo, ya godewa Sanata Tambuwal bisa wannan karimcin da ya ce zai taimaka matuka wajen rage wahalhalun da ke tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar a jihar.

 

Goronyo ya kara neman hadin kai a tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar domin ganin an samu gagarumin rinjaye a zaben 2027 a dukkan matakai.

 

 

 

NASIR MALALI

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Tambuwal jam iyyar PDP Tambuwal ya Tambuwal Ya

এছাড়াও পড়ুন:

Ribas: Za mu ɗauki matakan da za su shafi tattalin arzikin Nijeriya — ’Yan ƙwadago

Ƙungiyoyin ƙwadago reshen Jihar Ribas sun yi barazanar ɗaukar mataki muddin gwamnatin Nijeriya ba ta janye dokar-ta-ɓacin da ta ayyana a jihar ba.

Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwar gamayya da ƙungiyoyin ƙwadagon na NLC, TUC da JNC suka fitar a ranar 24 ga watan Maris.

Ban sani ba ko zan tsaya takara a 2027 — Atiku Kwamishinan Abba ya yi murabus bayan watanni 7 da naɗinsa

Shugabannin ƙungiyoyin ƙwadago na jihar sun nuna damuwa kan tasirin dokar-ta-ɓacin a kan tattalin arzikin jihar da kuma nuna rashin dacewar ta a hukumance.

A cewarsu, wannan matakin ya sanya an kasa biyan albashin ma’aikatan ƙananan hukumomi a jihar.

’Yan ƙwadagon sun bayyana cewa dakatar da zaɓaɓɓun jami’an gwamnatin jihar da rashin biyan albashin ma’aikatan keta haƙƙin bil’adama ne da ka iya ta’azzara matsalar tsaro da na tattalin arziki a jihar.

Sanarwar da ƙungiyoyin suka sanya wa hannun ta yi kira ga Tinubu da majalisar dokoki da kuma ɓangaren shari’a da su ɗauki matakan janye dokar nan take tare da mayar da gwamnan jihar da mataimakiyarsa da kuma ’yan majalisar jihar.

A cewar ’yan kwadagon, muddin ba a yi hakan ba nan da wani lokaci, za su ɗauki matakan da ka iya shafar tattalin arzikin ƙasa baki ɗaya.

Aminiya ta ruwaito cewa wannan sanarwa na ƙunshe da sa hannun shugaban NLC na Ribas, Alex Agwanwor da takwaransa na TUC, Ikechukwu Onyefuru da kuma shugaban JNC, Chuku Emecheta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gobara Ta Ƙone Sabon Ginin Ɗakunan Kwanan Ɗalibai Mata Na Jami’ar Sokoto 
  • Iran, Lebanon, Iraki, Yemen sun fara atisayen hadin gwiwa na goyan bayan Gaza
  • Za a Fara Cin Moriyar Shirin BEAR III Na UNESCO da Koria Ta Kudu Jihar Kano
  • Ranar Kudus: al’ummar Iran zasu nuna hadin kan su ga duniya_ Pezeshkian
  • Ahmad Lawan ya raba tallafin N27m da buhun shinkafa 300 a Yobe
  • JIBWIS Ta Raba Kayan Abinci Na Kimanin Naira Miliyan 9 Ga Marayu
  • Majalisa Ta Yi Watsi Da Kara Akan Akpabio Kan Zargin Neman Yin Lalata Da Natasha
  • Ribas: Za mu ɗauki matakan da za su shafi tattalin arzikin Nijeriya — ’Yan ƙwadago
  • DAGA LARABA: Yadda Farashin Kayan Masarufi Suke Gabanin Sallah
  • Gidauniyar Zakkah ta raba wa marayu 100 kayan sallah a Gombe