Yara mata kimanin 74,452 ne suka amfana da tallafin kudi karkashin shirin Adolescent Girls Initiative for Learning and Empowerment (AGILE) a kananan hukumomi 19 na jihar Kano, wanda ya kunshi rukuni na farko da na biyu.

AGILE wani shiri ne na Bankin Duniya tare da hadin gwiwar Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya, wanda aka kirkira don inganta damar samun ilimin sakandare ga yara mata masu shekaru tsakanin 10 zuwa 20.

Shirin yana daukar matakai da dama domin tabbatar da samun ingantaccen ilimi ga yara mata, ciki har da gina da gyara makarantu, da bayar da tallafin kudi ga iyalai masu karamin karfi, da yakar al’adu da ke hana ‘yan mata zuwa makaranta, da karfafa yara mata  fasahar zamani, da kasuwanci, da kuma dabarun rayuwa.

a ziyarar da tawagar Kano AGILE (Component 2.1) ta kai zuwa wasu makarantun sakandare a karamar hukumar Makoda, wato GGSS Maitsid, da GGSS Koguna da GGSS Sabon Ruwa, wadanda suka amfana da shirin, sun bayyana cewa tallafin kudi na AGILE  ya taka muhimmiyar rawa wajen bunkasa iliminsu.

Daliban sun ce sun yi amfani da kudin ne wajen koyon sana’o’in hannu kamar su siyar da kayan kamshi da alewa, da kuma sayen kaya na makaranta kamar uniform, da  takalma, da littattafai, da jakunkunan makaranta.

Sun godewa shirin bisa irin tallafin da suka samu.

A nata jawabin, Mataimakiyar Shugaban Tawagar Component 2.1, Hajiya Abu Umar Muhammad, ta bayyana cewa sun kai ziyara Koguna a Makoda domin gano matsalolin da ‘yan mata ke fuskanta wajen karbar kudin tallafi.

Ta ce wasu suna fuskantar matsala da katin ATM, wasu suna samun matsala da sunayensu, da dai sauran matsaloli.

Ta kara da cewa an shigar da ‘yan mata 74,452 a rukuni na farko da na biyu, yayin da 39,000 suka shiga mataki na uku na shirin.

Shugaban karamar hukumar Makoda, Alhaji Auwal Isah Jibga, ya jaddada cewa shirin ya taimaka sosai wajen rage yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a fadin karamar hukumar da jihar baki daya.

Ya bukaci a ci gaba da shirin kuma ya shawarci dalibai da su yi amfani da kudin ta hanya mafi dacewa da yadda aka tsara.

Wakiliyar Radio Nigeria ta bayyana cewa kafin hakan, tawagar AGILE Component 2.1 ta kai ziyara karamar hukumar Bebeji, inda suka tattauna da dalibai, da malamai da masu ruwa da tsaki domin tabbatar da nasarar shirin.

Daga Khadija Aliyu 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: karamar hukumar

এছাড়াও পড়ুন:

Trump ya jaddada shirin Amurka na kai hari a Najeriya

Shugaba Donald Trump, ya jaddada cewa Amurka na iya tura sojoji ko ƙaddamar da hare-hare a kan Najeriya idan har kashe-kashen da ya ce ana yi wa Kiristoci suka ci gaba.

A yayin tattaunawa da manema labarai da kuma saƙonnin da ya wallafa a shafukan sada zumunta, Mista Trump ya ce ba zai zauna yana kallo ba. “Ana kashe Kiristoci da dama a Najeriya; ba zan bari a ci gaba ba,” in ji shi.

A sakon da ya wallafa a dandamalin Truth a ranar Asabar, Trump ya ce Washington na iya shiga Najeriya da ƙarfin soji domin “kakkaɓe” abin da ya kira ƙungiyoyin ƴan ta’adda masu kishin addinin Islama.

Haka kuma ya yi barazanar dakatar da duk wani taimakon Amurka zuwa Najeriya idan wannan har ya ci gaba.

Matar aure ta yanka wuyan mijinta, ta fasa masa ido da wuƙa a Neja Yadda matata ta ɓace a Abuja aka tsince ta a Sakkwato

Wannan batu ya biyo bayan matakin da Amurka ta ɗauka a baya-bayan nan, inda ta saka Najeriya cikin jerin ƙasashen da take nuna damuwa game da take ’yancin addini.

Sai dai fadar gwamnatin Najeriya ta ce za ta yi maraba da duk wani haɗin gwiwa daga Amurka wajen yak6i da masu tsattsauran ra’ayi, amma ta musanta zargin cewa mayakan sun fi kashe Kiristoci kawai.

Hukumomin Najeriya sun jaddada cewa rikice-rikicen tsaro a ƙasar sun shafi duka al’ummomin — Kiristoci da Musulmai — ba tare da bambanci ba.

Tun a ranar Juma’a, Trump ya riƙa wallafa zarge-zargen cewa “ana kashe dubban Kiristoci a Najeriya” kuma masu tsattsauran ra’ayin Islama ne ke aikata hakan — bayanin da bai kawo hujjoji masu ƙarfi ba.

Wani ɓangare na siyasar Amurka ma ya ƙara ƙarfafa wannan muhawara: a watan Maris ɗan majalisar wakilai Chris Smith ya yi kira a saka Najeriya a jerin ƙasashen da ake damuwa da su; yayin da a watan Oktoba Sanata Ted Cruz da ɗan majalisar Riley Moore — dukkansu ’yan Republican ne — suka zargi gwamnatin Najeriya da yin shiru ko yin watsi da batun.

Wannan zargi ya ƙara ƙarfafa masu jaddada cewa ana kashe Kiristoci a Najeriya, tare da sake tada muhawara kan yadda za a magance matsalolin tsaro a ƙasar.

Masana tsaro da dama sun lura cewa Najeriya ta daɗe tana haɗuwa da rikice-rikice daban-daban — na ƙabilanci, na addini da na ‘yan ta’adda — inda mafi yawan raunuka da asarar rai ke faruwa a fannoni daban-daban na al’umma.

Hakan na nuna bukatar a yi nazari mai zurfi kafin ɗaukar matakai masu tsanani irin su tura dakarun ƙasashen waje.

Fadar gwamnatin Najeriya ta ce za ta marabci duk wani taimako daga Amurka wajen yaki da mayaka masu tsattsauran ra’ayi, amma ta musanta zargin cewa mayakan sun fi kashe Kiristoci kaɗai. Hukumomin Najeriya sun jaddada cewa rikice-rikicen tsaro a ƙasar sun shafi kowa — Kiristoci da Musulmai — kuma batun yana buƙatar a duba shi cikin natsuwa.

Mene ne ƙarfin ikon Amurka?

Trump ya jawo hankalin jama’a da cewa a wa’adinsa na farko ya saka Najeriya cikin jerin ƙasashen da take da damuwa da su, amma gwamnatin da ta gaje shi, Joe Biden, ta cire Najeriya daga wannan jerin a 2021.

A kan aiwatar da irin wannan mataki na amfani da soji, masana suna ta muhawara: Kundin Tsarin Mulkin Amurka, sashe na 8, yana ba Majalisar Dokokin Amurka ikon ayyana yaƙi da kuma tsara dokokin da suka shafi mamaye ƙasa da teku.

Sai dai a aikace, kundin ya tanadi cewa majalisar ne ke da ƙarfin yanke shawara mai ƙarfi kan irin matakin da za a ɗauka — wato Shugaban ƙasa ba shi kaɗai zai iya yanke hukunci mai zurfi ba tare da goyon bayan dokokin ƙasa ba.

A bangaren dokokin duniya, Majalisar Ɗinkin Duniya ta jaddada cewa amfani da ƙarfin ƙasa kan wata ƙasa ba abu ne da za a lamunta ba sai dai a cikin yanayin kare kai ko kan wata hujja ta doka da ta amince.

 

Me doka ta ce a kan kutse?

A hira da BBC, Barista Audu Bulama Bukarti, masani kan shari’a da tsaro a Afirka, ya bayyana cewa Amurka ba ta da hurumin kutsawa Najeriya domin yakar ta’addanci sai da izinin Najeriya da kuma tsarin doka na kasa da kasa.

“Amurka ba ta da ikon afka wa Najeriya domin Najeriya ƙasa ce mai zaman kanta wadda take da cikakken ‘yanci,” in ji shi.

Ya ce doka ta kasa da kasa, ciki har da wasu dokoki da bayyanannun ƙa’idojin Majalisar Dinkin Duniya, sun haramta aikata kutse kai tsaye ba tare da izini ba.

A cewar sa, haramun ne ga wata ƙasa ta shigo sararin samaniyar Najeriya ko ta yi kutse cikin ƙasar ba tare da amincewar gwamnati ba.

Makomar muhawara

Duk da zarge-zargen da wasu ’yan siyasa da masu ra’ayin kishin addini a ƙasashen waje suka yi, masana tsaro da lauyoyi na nan suna jaddada cewa duk wani mataki na soja da za a ɗauka a ƙasa ta waje yana buƙatar cikakken bin doka — na cikin gida da na duniya.

Hakan na nuna cewa kafin a ɗauki mataki mai tsanani irin turawa ko amfani da soji, dole ne a yi nazari mai zurfi, a nemi izini daga hukumomin Najeriya, ko a bi hanyoyin doka na ƙasa da ƙasa.

A ƙarshe, gwamnatin Najeriya ta ce za ta amince da taimako na gaskiya daga ƙawance amma ba za ta lamunci wata ƙasa ta yi amfani da ƙarfin soja a kan ƙasar ba sai an bi doka da tsarin da ya dace.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Karuwanci da zubar da cikin ’yan mata ’yan gudun hijira ya karu a Maiduguri
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Yayi Maraba Da Kalaman Da Hukumar IAEA Ta yi Kan Shirin Nukuliyarta
  • Gwamna Namadi Ya Yaba Da Tasirin Shirin NG-CARES A Jihar Jigawa
  • Gidan rediyo ya ɗauki nauyin sanya yara 40 a makaranta a Kano
  • Uwargidan Gwamnan  Zamfara Ta Yaba Wa  Karamar Hukumar Gusau Bisa Shirin Tallafawa Jama’a
  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Yabawa Gwamna Namadi Bisa Ayyukan Hanyoyi A Fadin Jihar
  • Trump ya jaddada shirin Amurka na kai hari a Najeriya
  • Ministar Jin Dadin Jama’a ta Sudan: Mayakan RSF Sun Kashe Mata 300 Da Yi Wa 25 Fyade A El Fasher
  • Majalisar Karamar Hukumar Bubura Ta Kai Tallafin Kayayyakin Abinci Cibiyar Gyaran Hali
  • Gidauniyar IRM Da KADCHMA, Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna