Yara mata kimanin 74,452 ne suka amfana da tallafin kudi karkashin shirin Adolescent Girls Initiative for Learning and Empowerment (AGILE) a kananan hukumomi 19 na jihar Kano, wanda ya kunshi rukuni na farko da na biyu.

AGILE wani shiri ne na Bankin Duniya tare da hadin gwiwar Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya, wanda aka kirkira don inganta damar samun ilimin sakandare ga yara mata masu shekaru tsakanin 10 zuwa 20.

Shirin yana daukar matakai da dama domin tabbatar da samun ingantaccen ilimi ga yara mata, ciki har da gina da gyara makarantu, da bayar da tallafin kudi ga iyalai masu karamin karfi, da yakar al’adu da ke hana ‘yan mata zuwa makaranta, da karfafa yara mata  fasahar zamani, da kasuwanci, da kuma dabarun rayuwa.

a ziyarar da tawagar Kano AGILE (Component 2.1) ta kai zuwa wasu makarantun sakandare a karamar hukumar Makoda, wato GGSS Maitsid, da GGSS Koguna da GGSS Sabon Ruwa, wadanda suka amfana da shirin, sun bayyana cewa tallafin kudi na AGILE  ya taka muhimmiyar rawa wajen bunkasa iliminsu.

Daliban sun ce sun yi amfani da kudin ne wajen koyon sana’o’in hannu kamar su siyar da kayan kamshi da alewa, da kuma sayen kaya na makaranta kamar uniform, da  takalma, da littattafai, da jakunkunan makaranta.

Sun godewa shirin bisa irin tallafin da suka samu.

A nata jawabin, Mataimakiyar Shugaban Tawagar Component 2.1, Hajiya Abu Umar Muhammad, ta bayyana cewa sun kai ziyara Koguna a Makoda domin gano matsalolin da ‘yan mata ke fuskanta wajen karbar kudin tallafi.

Ta ce wasu suna fuskantar matsala da katin ATM, wasu suna samun matsala da sunayensu, da dai sauran matsaloli.

Ta kara da cewa an shigar da ‘yan mata 74,452 a rukuni na farko da na biyu, yayin da 39,000 suka shiga mataki na uku na shirin.

Shugaban karamar hukumar Makoda, Alhaji Auwal Isah Jibga, ya jaddada cewa shirin ya taimaka sosai wajen rage yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a fadin karamar hukumar da jihar baki daya.

Ya bukaci a ci gaba da shirin kuma ya shawarci dalibai da su yi amfani da kudin ta hanya mafi dacewa da yadda aka tsara.

Wakiliyar Radio Nigeria ta bayyana cewa kafin hakan, tawagar AGILE Component 2.1 ta kai ziyara karamar hukumar Bebeji, inda suka tattauna da dalibai, da malamai da masu ruwa da tsaki domin tabbatar da nasarar shirin.

Daga Khadija Aliyu 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: karamar hukumar

এছাড়াও পড়ুন:

Za mu ɗauki mataki kan mambobinmu da ke shirin shiga haɗakar ADC — PDP

Babbar jam’iyyar hamayya a Nijeriya, PDP ta ce za ta ɗauki tsattsauran mataki kan mambobinta da ke ƙoƙarin shiga sabuwar haɗaka da jam’iyyar ADC.

Yayin da yake jawabi ga manema labarai bayan taron kwamitin amintattun jam’iyyar, shugaban jam’iyyar na ƙasa Ambasada Iliya Damagum ya ce jam’iyyar tana gargaɗi ’yan’yanta da ke shirin shiga sabuwar haɗakar ADC.

Damagum ya ce ƙoƙarin da haɗakar ke shirin yi ba zai yi tasiri ba, yana mai cewa da dama daga cikin mambobin haɗakar za su koma jam’iyyunsu.

“Yana da kyau su sani cewa babu inda ya kamata a haɗu domin tunkarar gwamnatin APC da ya wuce jam’iyyar PDP, amma in suna ganin ba haka ba, to su je su gwada su gani, amma dai na san dole za su dawo”, in ji shi.

Shugaban riƙon ya kuma gargaɗi ’yan PDP da ya ce suna ƙoƙarin “sayar da jam’iyyar”.

Kawo yanzu dai akwai jiga-jigan PDP cikin sabuwar haɗakar ta ADC, ciki har da tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar a zaɓen da ya gabata, Atiku Abubakar.

A farkon makon nan ne dai jam’iyyar PDP ta gudanar da taronta na Kwamitin Zartaswa da a ciki ta ce ta ɗinke ɓarakar da ta ɗauki tsawon lokacin tana fama da ita a cikin jam’iyyar.

Mun shirya fito-na-fito da APC — Malami

Shi ma dai tsohon Ministan Shari’a, Abubakar Malami ya ce a shirye haɗakar ADC take wajen yaƙi da gwamnatin APC domin kawo “gyara kan yadda ake tafiyar da gwamnati.”

Malami —wanda ya kasance minista a zamanin gwamnatin tsohon shugaban Nijeriya, Mumammadu Buhari — ya ce ukuɓar da gwamnati Tinubu ta sanya talakawan Nijerya a ciki ba za ta misaltu ba.

A hirarsa da BBC, Abubakar Malami ya ce sun fito fili ne domin su yaƙi jam’iyyar APC mai mulki, musamman yadda ta bar abubuwa da dama sun tabarbare a ƙasar, ciki har da tsaro da tattalin arziki da kuma sauran dangogin wahalhalu da gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta jefa talakawa.

“A duk lokacin da wata tarayya ta zo da wasu tsare-tsare na ƙuntata wa al’umma, da sanya su cikin halin wahala to wajibi a taru wuri guda su dauki mataki domin kawo sauyi ta hanyar maido da kaykkyawan tsari, da zai ɗaɗa wa mutane”, in ji shi.

“Mun yanke hukuncin ɗaukar mataki domin yaƙi da rashin tsaro da ynuwa domin maido da Nijeriya kan turba mai kyau da tsari”, in ji Malami.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Jigawa Ta Isa Roni A Ci Gaba Da Rangadin Kananan Hukumomi
  • Ambaliya da iska sun rushe gidaje 171 a watanni biyu a Gombe – SEMA
  • Baltasar: Mutumin da ya fitar da bidiyon lalatarsa da mata sama da 400 ya gurfana a kotu
  • Za mu ɗauki mataki kan mambobinmu da ke shirin shiga haɗakar ADC — PDP
  • Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano
  • Karamar Hukumar Maru Ta Bukaci A Dauki Matakan Kariya Kan Cutar Kwalaraci
  • Aragchi: Iran Ba zata Taba Daina Tace Makamashin Uranium A Cikin Gida Ba
  • Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma
  • Uwargidar Gwamnan Kaduna Ta Kaddamar Da Rabon Kayan Noma Ga Mata Manoma
  • Laftanar Kanar Shikarci: Sojojin Iran Suna Cikin Shirin Ko-Ta-Kwana Fiye Da Kowane Lokaci