Yara mata kimanin 74,452 ne suka amfana da tallafin kudi karkashin shirin Adolescent Girls Initiative for Learning and Empowerment (AGILE) a kananan hukumomi 19 na jihar Kano, wanda ya kunshi rukuni na farko da na biyu.

AGILE wani shiri ne na Bankin Duniya tare da hadin gwiwar Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya, wanda aka kirkira don inganta damar samun ilimin sakandare ga yara mata masu shekaru tsakanin 10 zuwa 20.

Shirin yana daukar matakai da dama domin tabbatar da samun ingantaccen ilimi ga yara mata, ciki har da gina da gyara makarantu, da bayar da tallafin kudi ga iyalai masu karamin karfi, da yakar al’adu da ke hana ‘yan mata zuwa makaranta, da karfafa yara mata  fasahar zamani, da kasuwanci, da kuma dabarun rayuwa.

a ziyarar da tawagar Kano AGILE (Component 2.1) ta kai zuwa wasu makarantun sakandare a karamar hukumar Makoda, wato GGSS Maitsid, da GGSS Koguna da GGSS Sabon Ruwa, wadanda suka amfana da shirin, sun bayyana cewa tallafin kudi na AGILE  ya taka muhimmiyar rawa wajen bunkasa iliminsu.

Daliban sun ce sun yi amfani da kudin ne wajen koyon sana’o’in hannu kamar su siyar da kayan kamshi da alewa, da kuma sayen kaya na makaranta kamar uniform, da  takalma, da littattafai, da jakunkunan makaranta.

Sun godewa shirin bisa irin tallafin da suka samu.

A nata jawabin, Mataimakiyar Shugaban Tawagar Component 2.1, Hajiya Abu Umar Muhammad, ta bayyana cewa sun kai ziyara Koguna a Makoda domin gano matsalolin da ‘yan mata ke fuskanta wajen karbar kudin tallafi.

Ta ce wasu suna fuskantar matsala da katin ATM, wasu suna samun matsala da sunayensu, da dai sauran matsaloli.

Ta kara da cewa an shigar da ‘yan mata 74,452 a rukuni na farko da na biyu, yayin da 39,000 suka shiga mataki na uku na shirin.

Shugaban karamar hukumar Makoda, Alhaji Auwal Isah Jibga, ya jaddada cewa shirin ya taimaka sosai wajen rage yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a fadin karamar hukumar da jihar baki daya.

Ya bukaci a ci gaba da shirin kuma ya shawarci dalibai da su yi amfani da kudin ta hanya mafi dacewa da yadda aka tsara.

Wakiliyar Radio Nigeria ta bayyana cewa kafin hakan, tawagar AGILE Component 2.1 ta kai ziyara karamar hukumar Bebeji, inda suka tattauna da dalibai, da malamai da masu ruwa da tsaki domin tabbatar da nasarar shirin.

Daga Khadija Aliyu 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: karamar hukumar

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Tattauana Da Shugaban Hukumar IAEA

Shugaban hukumar makamshin Nujkliya ta MDD ya zanda da ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi kan al-amuran da suka shafi shirin nukliyar kasar Iran da kuma tattaunawar da ake gudana tsakanin ta da Amurka.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa a tattaunawa ta wayar tarho tsakanin jami’an guda biyu a jiya Lahadi, Grossi shugaban IAEA ya bayyana cewa ya ji dadin yadda JMI ta zabi tattaunawa da AMurka dangane da shirinta na makamashin Nukliya. Ya kuma bayyana cewa hukumarsa a shirye take ta gabatar da duk wani taimakon da JMI take bukata a yayin tattaunawar.

A nashi bangaren Abbas Araqchi ya bayyana cewa kasar Iran a shirye take ta bada hadin kai ga hukumar ta IAEA kamar yadda yarjeniyar NPT take bukata da kuma dokokin kasa da kasa.

Abbas ya fada masa inda aka kai ya zuwa yanzu a tattaunawa ba kai tsaye ba tsakanin Iran da Amurka, a biranen Mascat na kasar Omman da kuma Roma na kasar Italiya.

Ya zuwa yanzu dai kasashen biyu sun gudanar da taro har sau uku dangane da shirin Nukliyar kasar ta Iran, kuma bangarorin biyu sun bayyana amincewarsu da yadda tattaunawar take tafiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Xi Ya Jaddada Muhimmancin Tsara Nagartaccen Shirin Raya Tattalin Arziki Da Zamantakewar Al’umma Tsakanin 2026-2030
  • Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga , Sun Ceto Fasinjoji 6 A Taraba
  • DAGA LARABA: Asarar Da Hausawa Ke Tafkawa Sakamakon Bacewar Tatsuniya
  • Da Alamu Amurka Ta Fara Dandana Kudarta
  • Za A Yi Allurar Rigakafi Ga Dabbobi Sama Da Miliyan Daya A Babura
  • NAJERIYA A YAU: Dalilin karyewar farashin shinkafa a kasuwannin Najeriya
  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Jaddada Wajabcin Komawa Kan Shirin Tsagaita Bude Wuta A Gaza
  • Yadda matar gwamna ta sa mata gasar haihuwar ’yan uku
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Tattauana Da Shugaban Hukumar IAEA
  • NAJERIYA A YAU: “Dalilin da muke sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki”