FERMA Ta Sake Jaddada Sadaukarwar Da Take Yi Na Kula Da Hanyoyin Tarayya
Published: 13th, March 2025 GMT
Hukumar kula da tituna ta tarayya (FERMA) ta jaddada kudirinta na kula da titunan gwamnatin tarayya da inganta ababen more rayuwa a fadin kasar nan.
Daraktan hukumar ta FERMA, Injiniya Kabiru Iliyasu Dan-Mulki ne ya bayyana haka a lokacin da ya karbi bakuncin shugabannin kungiyar ‘yan jarida ta kasa (NUJ) daga gidan rediyon tarayya (FRCN) da kuma gidan talabijin na Najeriya (NTA) Kaduna a ofishinsa da ke Kaduna.
Injiniya Dan-Mulki ya jaddada babban nauyin da ya rataya a wuyan hukumar ta FERMA na tabbatar da cewa titunan gwamnatin tarayya sun kasance masu kyau domin saukaka zirga-zirga a fadin kasar nan. Ya bayyana muhimmancin hada hannu da masu ruwa da tsaki, musamman kafafen yada labarai, domin wayar da kan jama’a game da ayyukan hukumar da kuma muhimmiyar rawar da take takawa wajen ci gaban kasa.
A nasu jawabin, shugaban kungiyar ta NUJ FRCN na Kaduna, Kwamared Umar Sarkin Fada, da sakataren kungiyar ta NUJ NTA Kaduna, Haruna Mohammed, sun jaddada bukatar hada kai wajen inganta ayyukan FERMA. Sun bayyana cewa ziyarar na da nufin karfafa hadin gwiwa wajen tallata ayyukan hukumar da karfafa gwiwar ‘yan kasar da su bayar da tasu gudummawar wajen kiyaye ababen more rayuwa.
Shugabannin kungiyar ta NUJ sun kuma bayyana damuwarsu kan rashin kyawun wasu hanyoyin gwamnatin tarayya da kuma harabar manyan cibiyoyin gwamnatin tarayya da suka hada da FRCN da NTA Kaduna. Sun bukaci FERMA da ta magance wadannan matsalolin a matsayin wani bangare na alhakinta na zamantakewa (CSR).
Sun yabawa hukumar ta FERMA bisa jajircewarta na kula da tituna tare da bada tabbacin hukumar na cigaba da bayar da goyon bayan kafafen yada labarai wajen sanar da ‘yan Najeriya kokarin da take yi na inganta ababen more rayuwa a fadin kasar.
Shamsuddeen Mannir Atiku
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: gwamnatin tarayya
এছাড়াও পড়ুন:
Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Karfin Tsaro Da Makamansu Masu Linzami Ne Suka Hana Makiya Kai Musu Hari
Ministan Harkokin Wajen Iran ya jaddada cewa: Ƙarfin tsaron Iran da makamanta masu linzami suna ba su ƙarfin gwiwa
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya bayyana cewa, da a ce Amurka za ta iya lalata cibiyoyin makamashin nukiliyar Iran, da ba za ta shiga zaman tattaunawa ba, yana mai jaddada cewa: Iran ta dogara da karfin sojanta, kuma shi ne ya tilasta wa makiya zaman tattaunawa da ita.
A ziyarar da ya kai wajen baje kolin littafai na birnin Tehran, Araqchi ya ce dangane da tattaunawa wand aba na kai tsaye ba da Amurka: Idan da a ce Amurka na da karfin lalata cibiyoyin makamashin nukiliyar Iran, da ba ta shiga tattaunawa ita ba.
Araqcgi ya kara da cewa: Iran ta dogara da karfinta na soji ne lamarin da ya tilastawa makiya zama kan teburin tattaunawa da ita, yana mai cewa karfin kariya da makamai masu linzami na Iran yasu bai wa masu shiga tsakani na Iran damar yin shawarwari domin suna hana bangaren da ke makiya gudanar da duk wata kasada ta soja.