HausaTv:
2025-12-10@18:49:08 GMT

Hamas : tattaunawa ce kawai mafita ta sakin wadanda ake garkuwa dasu

Published: 11th, March 2025 GMT

Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta yi imanin cewa barazanar da Isra’ila ke yi na sake dawo da yaki a zirin Gaza ba ta da amfani, tana mai cewa tattaunawar tsagaita bude wuta ce hanya daya tilo da Isra’ila za ta iya ceto rayukan ‘yan kasarta da take garkuwa

ranar Litinin 10 ga watan Maris, kungiyar ta ce Firaministan Isra’ila Benyamin Netanyahu na kawo cikas ga aiwatar da yarjejeniyar saboda wasu dalilai na rajin kansa da kuma na siyasa kawai.

Hamas ta kuma kara jaddada aniyar ta na aiwatar da yarjejeniyar, inda ta bayyana aniyar ta na kaddamar da shirin tsagaita wuta a mataki na biyu ba tare da bata lokaci ba.

Har ila yau kungiyar ta ce gwamnatin Isra’ila tana ci gaba da karya yarjejeniyar tare da kin shiga mataki na biyu, tana mai cewa wannan “jinkirin” ya kara mayar da ita saniyar ware a duniya.

Hamas ta jaddada cewa, masu shiga tsakani na kasa da kasa ne suka yi shawarwari da ita, kuma kasashen duniya sun amince da ita, don haka ta jaddada bukatar tabbatar da aiwatar da ita yadda ya kamata daga gwamnatin kasar don tabbatar da sako mutanen da ta kama.

Tun da farko kakakin kungiyar Hamas Abdul Latif al-Qanou ya bayyana sassaucin da kungiyar ta nuna a lokacin tattaunawar baya-bayan nan da masu shiga tsakani na Masar da Qatar, da kuma wakilin shugaban Amurka Donald Trump a birnin Doha, ya kuma jaddada fatansu na cimma nasarar kammala wannan shawarwarin da Isra’ila.

Ya kara da cewa tattaunawar ta Doha ta shafi kawo karshen yakin, janyewar Isra’ila da sake gina yankin Zirin Gaza.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

ASUU-SSU Ta Zargi VC Da KaryDokokin Jami’ar Jihar Sakkwato

Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta Nijeriya (ASUU), reshen Jami’ar Jihar Sakkwato (ASUU-SSU), ta zargi Mataimakin Shugaban Jami’ar (Vice-Chancellor) da kin bin umarnin Gwamnan Jihar Sakkwato game da sauke Bursar da ya kai lokacin ritaya.

A cikin wata sanarwa da ta fitar a Sakkwato a ranar Litinin, 8 ga Disamba 2025, ƙungiyar ta ce Gwamna Dr. Ahmed Aliyu Sakkwato, wanda shi ne Visitor na Jami’ar, ya amince da buƙatarsu na tabbatar da bin dokokin Jami’ar ta hanyar amincewa da ritayar Bursar ɗin.

ASUU-SSU ta bayyana cewa Ofishin Shugaban Ma’aikatan Gwamnatin Jihar Sakkwato ya aika da takardar umarni mai lamba HS/ADM/101/VOL-1, ɗauke da kwanan wata 18 ga Nuwamba 2025, wadda ta umurci Bursar ya miƙa ragamar ofis ga jami’in da ya fi kowa girma a sashen Bursary, har sai an naɗa sabon Bursar bisa tanadin dokar Jami’ar Jihar Sakkwato ta 2009.

Sai dai ƙungiyar ta ce kusan wata guda ke nan VC ɗin bai aiwatar da umarnin ba.

Shugaban reshen ASUU-SSU, Kwamared Bello Musa, ya bayyana cewa sun rubuta wa VC takardar tunatarwa da wata takarda ta biyu, amma ba su samu amsa ba.

Haka kuma, sun gudanar da taro biyu da shi, amma ya dage cewa akwai wata amincewa da Ma’aikatar Ilimi Mai Zurfi ta jihar ta bayar a 2024 game da matsayin Bursar.

Sai dai ASUU ta ce wannan hujja “ba ta da tushe”, domin sabon umarnin Gwamna “ya fi ƙarfi kuma ya shafe duk wani tsohon matsayi”, musamman ma ganin cewa Bursar ya kai lokacin ritaya tun 3 ga Oktoba 2024.

A cewarta, Ma’aikatar Kula Da Ma’aikata ta riga ta aika masa da takardar ritaya ta hannun Ma’aikatar Kudi ta jihar.

Ƙungiyar ta ce ci gaba da bari tsohon ma’aikaci ya rattaɓa hannu kan muhimman takardun Jami’a “na karya doka, kuma na tauye ikon Jami’a (University Autonomy).”

ASUU-SSU ta yaba wa Gwamnan jihar bisa “ƙarin nuna biyayya ga doka da buɗe ƙofar sauraron ƙorafe-ƙorafe”, tare da buƙatar ya tabbatar da cewa ba a katse hanyoyin isar da sahihan koke-koke zuwa gare shi ba.

Ƙungiyar ta ce zanga-zangar lumana da ta gudanar a Jami’ar na nufin matsa wa VC lamba ya aiwatar da umarnin Gwamna ba tare da ɓata lokaci ba, domin tabbatar da zaman lafiya da daidaiton aiki.

Ta kuma sha alwashin ɗaukar “mataki mafi tsauri” idan ba a aiwatar da umarnin ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hamas Ta yi Tir Da Sabbin Matsugunan Yahudawa Da Isra’ila Ke yi A Yankunan Da Ta Mamaye
  • Antoni Gutress Ya Yi Allawadai Da Kutsen Da “Isra’ila” Ta Yi A Cibiyar Unrwa
  • Iran da Saudiyya sun sake jaddada fadada dangantakarsu
  • An cire Tony Blair daga jerin wadanda zasu jagoranci Gaza
  • Isra’ila ta sake kai hare-haren a kudancin Lebanon
  • Trump Ya Yi Gefe Da Kasashen Turai Dangane Da Tattaunawa Kan Rikicin Ukraine
  • Iran Ta Gudanar Da Taro Kan Yadda Manzon Allah (s) Ya Yi Mu’amala Da Wadanda Ba Musulmi Ba
  •  Talauci Yana Karuwa A “Isra’ila” Bayan 7 Ga Watan Oktoba
  • ASUU-SSU Ta Zargi VC Da KaryDokokin Jami’ar Jihar Sakkwato
  • Kungiyar AU Ta yi Tir Da Harin Da RSF  Takai A Makarantar Kananan Yara Da Ya Kashe Mutane 80