HausaTv:
2025-11-15@01:24:02 GMT

Hamas : tattaunawa ce kawai mafita ta sakin wadanda ake garkuwa dasu

Published: 11th, March 2025 GMT

Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta yi imanin cewa barazanar da Isra’ila ke yi na sake dawo da yaki a zirin Gaza ba ta da amfani, tana mai cewa tattaunawar tsagaita bude wuta ce hanya daya tilo da Isra’ila za ta iya ceto rayukan ‘yan kasarta da take garkuwa

ranar Litinin 10 ga watan Maris, kungiyar ta ce Firaministan Isra’ila Benyamin Netanyahu na kawo cikas ga aiwatar da yarjejeniyar saboda wasu dalilai na rajin kansa da kuma na siyasa kawai.

Hamas ta kuma kara jaddada aniyar ta na aiwatar da yarjejeniyar, inda ta bayyana aniyar ta na kaddamar da shirin tsagaita wuta a mataki na biyu ba tare da bata lokaci ba.

Har ila yau kungiyar ta ce gwamnatin Isra’ila tana ci gaba da karya yarjejeniyar tare da kin shiga mataki na biyu, tana mai cewa wannan “jinkirin” ya kara mayar da ita saniyar ware a duniya.

Hamas ta jaddada cewa, masu shiga tsakani na kasa da kasa ne suka yi shawarwari da ita, kuma kasashen duniya sun amince da ita, don haka ta jaddada bukatar tabbatar da aiwatar da ita yadda ya kamata daga gwamnatin kasar don tabbatar da sako mutanen da ta kama.

Tun da farko kakakin kungiyar Hamas Abdul Latif al-Qanou ya bayyana sassaucin da kungiyar ta nuna a lokacin tattaunawar baya-bayan nan da masu shiga tsakani na Masar da Qatar, da kuma wakilin shugaban Amurka Donald Trump a birnin Doha, ya kuma jaddada fatansu na cimma nasarar kammala wannan shawarwarin da Isra’ila.

Ya kara da cewa tattaunawar ta Doha ta shafi kawo karshen yakin, janyewar Isra’ila da sake gina yankin Zirin Gaza.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki

Amurka ta dakatar da ka’idar fadada jerin wadanda kasar ta takaita fitar wa kayayyaki a kwanan nan, wani muhimmin mataki ne da Amurkan ta dauka a fannin cimma matsayar da aka amincewa, yayin tattaunawar tattalin arziki da cinikayya da aka yi tsakanin Sin da Amurka a Kuala Lumpur. Kuma kasashen biyu za su ci gaba da tattaunawa kan shirye-shirye bayan dakatarwar shekara guda.

Kakakin ma’aikatar kasuwanci ta Sin ya bayyana hakan ne kan tambayar da ’yan jarida suka yi masa game da matakin na Amurka na dakatar da ka’idar fadada jerin wadanda kasar ta takaita fitar wa kayayyaki, a yayin taron manema labarai na jiya Talata.

Kakakin ya kara da cewa, Sin tana son yin aiki tare da Amurka, ta hanyar bin ka’idojin girmama juna, da kuma gudanar da shawarwari bisa daidaito, don karfafa tattaunawa da musayar ra’ayi, da warware sabanin ra’ayin ta hanyar da ta dace, da kuma samar da yanayi mai kyau na inganta hadin gwiwa tsakanin kamfanonin kasashen biyu, da kuma tabbatar da tsaro, da kwanciyar hankali na tsarin masana’antun samar da kayayyaki na duniya.

ADVERTISEMENT

Amurka ta sanar da dakatar da ka’idar ne tun daga ranar 10 ga watan Nuwamban 2025 zuwa ranar 9 ga watan Nuwamba na 2026. Kuma a wa’adin, kamfanonin da Amurka ta ayyana a “Jerin Sunayen Kamfanoni” da ta kakabawa takunkumi, da kamfanonin da suka yi alaka da su, masu rike da fiye da kashi 50% na hannun jari, ba za su fuskanci karin takunkumin fitar da kayayyaki ba. (Safiyah Ma)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Xi Ya Gana Da Sarkin Sifaniya A Birnin Beijing November 12, 2025 Daga Birnin Sin Sin Ta Yi Kira Da A Inganta Mika Mulki Cikin Kwanciyar Hankali A Sudan Ta Kudu November 12, 2025 Daga Birnin Sin Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam November 11, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe
  • Jihar Kwara Ta Jaddada Kudirin Tallafa wa Wadanda Suka Tsira Daga Cin Zarafin Jinsi
  • Gaza: Hamas Ta Nemi Kawo Karshen Kisan Kiyashi Da Lamunce  Shigar Da Taimako
  • MURIC ta buƙaci Tinubu ya sauke Amupitan daga shugabancin INEC
  • Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki
  • Iran Ta Zama Memba A Kungiyar Tattara Bayanai Na  Ilimomi Da Kere-kere Ta Duniya ( ISKO)
  • Kungiyar Wamban Shinkafi Ta Amince Da Tinubu a 2027
  • Sheikh Qassem: Kawar Da Hizbullah Ne Babban Burin Isra’ila A Lebanon
  • Masar Da Sudan Sun Jaddada Wajabcin Tabbatar Da Zaman Lafiya A Yankin
  • UNICEF ta ce Isra’ila ta hana allurar rigakafin yara masu mahimmanci shiga Gaza