Hamas : tattaunawa ce kawai mafita ta sakin wadanda ake garkuwa dasu
Published: 11th, March 2025 GMT
Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta yi imanin cewa barazanar da Isra’ila ke yi na sake dawo da yaki a zirin Gaza ba ta da amfani, tana mai cewa tattaunawar tsagaita bude wuta ce hanya daya tilo da Isra’ila za ta iya ceto rayukan ‘yan kasarta da take garkuwa
ranar Litinin 10 ga watan Maris, kungiyar ta ce Firaministan Isra’ila Benyamin Netanyahu na kawo cikas ga aiwatar da yarjejeniyar saboda wasu dalilai na rajin kansa da kuma na siyasa kawai.
Hamas ta kuma kara jaddada aniyar ta na aiwatar da yarjejeniyar, inda ta bayyana aniyar ta na kaddamar da shirin tsagaita wuta a mataki na biyu ba tare da bata lokaci ba.
Har ila yau kungiyar ta ce gwamnatin Isra’ila tana ci gaba da karya yarjejeniyar tare da kin shiga mataki na biyu, tana mai cewa wannan “jinkirin” ya kara mayar da ita saniyar ware a duniya.
Hamas ta jaddada cewa, masu shiga tsakani na kasa da kasa ne suka yi shawarwari da ita, kuma kasashen duniya sun amince da ita, don haka ta jaddada bukatar tabbatar da aiwatar da ita yadda ya kamata daga gwamnatin kasar don tabbatar da sako mutanen da ta kama.
Tun da farko kakakin kungiyar Hamas Abdul Latif al-Qanou ya bayyana sassaucin da kungiyar ta nuna a lokacin tattaunawar baya-bayan nan da masu shiga tsakani na Masar da Qatar, da kuma wakilin shugaban Amurka Donald Trump a birnin Doha, ya kuma jaddada fatansu na cimma nasarar kammala wannan shawarwarin da Isra’ila.
Ya kara da cewa tattaunawar ta Doha ta shafi kawo karshen yakin, janyewar Isra’ila da sake gina yankin Zirin Gaza.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
An kama wani mutum a Abuja yana ƙoƙarin kai harsasai ga ’yan bindiga a Zamfara
Rundunar ’yan sandan yankin Babban Birnin Tarayya Abuja ta kama wani mutum mai suna Ahmed Abubakar mai shekara 32, bisa zargin ƙoƙarin kai harsasai 1,000 ga ’yan bindiga a Jihar Zamfara.
Kwamishinan ’yan sanda na birnin, Miller G. Dantawaye, ne ya bayyana hakan ga ’yan jarida a hedikwatar rundunar a Abuja ranar Laraba.
Sakkwatawa na murnar kisan da sojoji suka yi wa mataimakin Bello Turji Dalibin jami’a ya rasu a hatsarin motar murnar kammala jarabawaDantawaye ya ce an kama wanda ake zargin ne a ranar Litinin da misalin ƙarfe 3:30 na yamma, kuma tawagar musamman ta rundunar ce ta kama shi bayan samun sahihin bayanan sirri a Unguwar Dodo da ke ƙaramar hukumar Gwagwalada.
Ya ce binciken farko ya nuna cewa wanda ake zargin yana mu’amala da wani abokinsa da aka gano sunansa Yusuf Mohammed, inda aka gano cewa yana shirin sayo harsasai 1,000 domin kai wa ’yan bindiga da ke cikin daji a Zamfara.
“Bincikenmu ya ƙara nuna cewa wani ɗan uwansa, Ahmed Yakubu, ne ya turo shi kuma yanzu ya cika wandonsa da iska, domin ya sayo ya kuma kai wa ’yan ta’adda da ke aiki a yankin su na Zamfara,” in ji CP Dantawaye.
Ya ce wanda ake zargin yana hannun ’yan sanda a halin yanzu, yayin da ake ci gaba da ƙoƙarin kama abokin aikin nasa da ya tsere.
Kwamishinan ya jaddada kudirin rundunar na kawar da masu aikata laifuka a Abuja da kewaye, tare da tabbatar da tsaron mazauna yankin.
Ya yi kira ga jama’a da su ci gaba da tallafa wa ’yan sanda ta hanyar bayar da rahoton duk wani abin da ake zargin laifi ta layukan gaggawa na rundunar.