Hamas : tattaunawa ce kawai mafita ta sakin wadanda ake garkuwa dasu
Published: 11th, March 2025 GMT
Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta yi imanin cewa barazanar da Isra’ila ke yi na sake dawo da yaki a zirin Gaza ba ta da amfani, tana mai cewa tattaunawar tsagaita bude wuta ce hanya daya tilo da Isra’ila za ta iya ceto rayukan ‘yan kasarta da take garkuwa
ranar Litinin 10 ga watan Maris, kungiyar ta ce Firaministan Isra’ila Benyamin Netanyahu na kawo cikas ga aiwatar da yarjejeniyar saboda wasu dalilai na rajin kansa da kuma na siyasa kawai.
Hamas ta kuma kara jaddada aniyar ta na aiwatar da yarjejeniyar, inda ta bayyana aniyar ta na kaddamar da shirin tsagaita wuta a mataki na biyu ba tare da bata lokaci ba.
Har ila yau kungiyar ta ce gwamnatin Isra’ila tana ci gaba da karya yarjejeniyar tare da kin shiga mataki na biyu, tana mai cewa wannan “jinkirin” ya kara mayar da ita saniyar ware a duniya.
Hamas ta jaddada cewa, masu shiga tsakani na kasa da kasa ne suka yi shawarwari da ita, kuma kasashen duniya sun amince da ita, don haka ta jaddada bukatar tabbatar da aiwatar da ita yadda ya kamata daga gwamnatin kasar don tabbatar da sako mutanen da ta kama.
Tun da farko kakakin kungiyar Hamas Abdul Latif al-Qanou ya bayyana sassaucin da kungiyar ta nuna a lokacin tattaunawar baya-bayan nan da masu shiga tsakani na Masar da Qatar, da kuma wakilin shugaban Amurka Donald Trump a birnin Doha, ya kuma jaddada fatansu na cimma nasarar kammala wannan shawarwarin da Isra’ila.
Ya kara da cewa tattaunawar ta Doha ta shafi kawo karshen yakin, janyewar Isra’ila da sake gina yankin Zirin Gaza.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kungiyar Abokan Yarjejeniyar M.D.D Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ke Kai Wa Kan Iran
Kungiyar ‘Abokan Yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya’ ta yi Allah wadai da harin da haramtacciyar kasar Isra’ila ta kai kan Iran
Kasashe mambobin kungiyar aminan yarjejeniyoyin Majalisar Dinkin Duniya sun fitar da wata sanarwa ta musamman inda suka yi kakkausar suka kan wuce gona da irin haramtacciyar kasar Isra’ila ke yi kan Jamhuriyar Musulunci ta Iran.
Sanarwar ta yi la’akari da harin hadin gwiwa ta sama da haramtacciyar kasar Isra’ila ta kaddamar a ranar 13 ga watan Yuni a kan wasu wurare da dama a Iran, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane da jikkata wasu daruruwa da suka hada da mata da kananan yara da masana kimiyya, matakin da ya saba wa Yarjejeniya ta Majalisar Dinkin Duniya da muhimman ka’idojin dokokin kasa da kasa.
‘Yan kungiyar sun kuma yi Allah wadai da harin ganganci kan fararen hula, da wuraren zaman jama’a, da kuma cibiyoyin nukiliyar na zaman lafiya, suna masu gargadin cewa irin wadannan ayyuka na iya haifar da watsuwar kayan aikin kimiyya da zai zama babbar barazana ga rayuwar fararen hula da muhalli.
Kungiyar ta yi kira da a tsaya tsayin daka kan amfani da karfi a kan Iran, tana mai jaddada nauyin da ke wuyan babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya na kiyaye manufofi da ka’idojin Yarjejeniyar Majalisar.
Har ila yau, ta jaddada aikin babban daraktan hukumar ta IAEA na yin Allah wadai da hare-haren da haramtacciyar kasar Isra’ila ke kaiwa kan cibiyoyin nukiliyar Iran.