Kasancewar “Taiwan A Matsayin Lardin Kasar Sin” Shi Ne Matsayin MDD A Ko Yaushe
Published: 10th, March 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Sin, Wang Yi ya bayyana a wajen taron manema labaru na ministan harkokin waje da aka shirya a harabar manyan tarukan kasar Sin guda biyu, lokacin da yake magana kan batun Taiwan cewa: suna daya tilo na Taiwan a Majalisar Dinkin Duniya shi ne “Lardin Taiwan na kasar Sin”.
Da take mayar da jawabi game da wannan batu, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Mao Ning, ta bayyana a wani taron manema labarai da aka saba gudanarwa da ya gudana yau 10 ga wata cewa, wannan shi ne daidaitaccen matsayin MDD a ko yaushe kuma haka abun yake a tarihi.
Mao Ning ta jaddada cewa, a ko da yaushe kasar Sin tana bin ka’idar kasancewar Sin daya tak, da kuma ra’ayi daya da aka samu na shekarar 1992, kana tana matukar son yin kokari don ganin an samu damar dinkuwar kasar Sin cikin lumana da gaskiya da sa himma. A sa’i daya kuma, kasar Sin za ta dauki dukkan matakan da suka dace don kare ikon mallakar kasarta da cikakken ‘yancin yankinta, da kuma fitowa da kakkausan harshe wajen nuna adawa da ayyukan ‘yan aware na neman ‘yancin kai na Taiwan da tsoma baki daga waje. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Yadda aka yi bikin naɗa Rarara sarkin wakar ƙasar Hausa a Daura
Sarkin Daura, Mai Martaba Alhaji Faruk Umar Faruk, ya naɗa fitaccen mawaƙin siyasar nan na Hausa, Dauda Kahutu Rarara, a matsayin Sarkin Waƙar Ƙasar Hausa.
An yi bikin naɗin sarautar ne a garin Daura a ranar Asabar 13 ga watan Disamba, 2025 domin karrama rawar da Rarara yake takawa wajen haɓaka waƙoƙin Hausa da kuma tasirin da yake da shi a fagen nishaɗi da al’adu.
Jirgin sama ya yi hatsari yayin sauka a Kano Tsaro: Abba ya kafa runduna ta musamman da za ta ke tsaron tashoshin mota a KanoTun da farko mawaƙin da kansa ya wallafa goron gayyatar naɗin sauratar da za a yi masa a shafinsa na Facebook, a ranar 9 ga watan Disamba, 2025.
Rarara ya ce: “Ina gayyatar kowa da kowa zuwa wajen naɗin sarautata, mai taken ‘Sarkin Waƙar Ƙasar Hausa’ sarautar da mai Alfarma Sarkin Daura ya yi min.
“Za a yi naɗin a fadar Mai Martaba Sarkin Daura a ranar Asabar, 13 ga watan Disamba, 2025, insha’Allah Allah.”
Bikin naɗin sarautar ya samu halartar manyan mutane, mawaƙa, jarumai, ciki har da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibirin, Ali Nuhu da sauransu, inda masoya da magoya bayan mawaƙin suka nuna farin cikinsu.
Masoyan mawaƙin sun bayyana cewa wannan karramawa ta dace da gudunmawar da Rarara ya bayar ga al’adun Hausawa.
Rarara, wanda ya shahara wajen yin waƙoƙin siyasa da na zamantakewa, ya daɗe ana damawa da shi kuma yana daga cikin manyan mawaƙa a Arewacin Najeriya.
Sabuwar sarautar da aka yi masa na nuni da amincewa da gudunmawarsa wajen bunƙasa waƙa a harshen Hausa da kuma tasirinsa a cikin al’umma.