Kasancewar “Taiwan A Matsayin Lardin Kasar Sin” Shi Ne Matsayin MDD A Ko Yaushe
Published: 10th, March 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Sin, Wang Yi ya bayyana a wajen taron manema labaru na ministan harkokin waje da aka shirya a harabar manyan tarukan kasar Sin guda biyu, lokacin da yake magana kan batun Taiwan cewa: suna daya tilo na Taiwan a Majalisar Dinkin Duniya shi ne “Lardin Taiwan na kasar Sin”.
Da take mayar da jawabi game da wannan batu, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Mao Ning, ta bayyana a wani taron manema labarai da aka saba gudanarwa da ya gudana yau 10 ga wata cewa, wannan shi ne daidaitaccen matsayin MDD a ko yaushe kuma haka abun yake a tarihi.
Mao Ning ta jaddada cewa, a ko da yaushe kasar Sin tana bin ka’idar kasancewar Sin daya tak, da kuma ra’ayi daya da aka samu na shekarar 1992, kana tana matukar son yin kokari don ganin an samu damar dinkuwar kasar Sin cikin lumana da gaskiya da sa himma. A sa’i daya kuma, kasar Sin za ta dauki dukkan matakan da suka dace don kare ikon mallakar kasarta da cikakken ‘yancin yankinta, da kuma fitowa da kakkausan harshe wajen nuna adawa da ayyukan ‘yan aware na neman ‘yancin kai na Taiwan da tsoma baki daga waje. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Matashi ya rasu yayin rikici a wajen radin suna a Bauchi
Wani matashi mai shekaru 20, Haruna Haruna, ya rasa ransa bayan fada ya barke a lokacin bikin radin suna a ƙauyen Kwata da ke Karamar Hukumar Warji ta Jihar Bauchi.
Bayanai sun ce lamarin ya faru ne a ranar Talata lokacin da sa’insa ta barke tsakanin wasu matasa ta rikide ta zama fada, wanda ya bar Haruna cikin rashin hayyacinsa.
Tinubu ya naɗa tsohon kantoman Ribas da Dambazau a matsayin Jakadun Najeriya ’Yan sandan Borno sun kama matashin da ake zargi da kashe makwabciyarsa da wuƙa“Wani matashi mai shekaru 20, Haruna Haruna na ƙauyen Kwata, Karamar Hukumar Warji, Jihar Bauchi, ya riga mu gidan gaskiya bayan rikici mai tsanani da ya barke a bikin radin suna a ranar 2 ga watan Disamba, 2025,” in ji Zagazola Makama, masani kan harkokin tsaro a yankin arewa maso gabas.
Ya kara da cewa rashin jituwa tsakanin wasu matasa a wajen bikin ta rikide zuwa fada, lamarin da ya bar wanda abin ya shafa ya suma nan take.
An ce an garzaya da Haruna zuwa Asibitin Gwamnati na Warji, amma ya rasu a yayin da ake masa jinya.
Da aka tuntubi mai magana da yawun ’yan sanda na jihar, Ahmed Wakili, ya ce yana cikin taro kuma ya yi alƙawarin dawowa da bayani, sai dai bai yi hakan ba har zuwa lokacin da aka kammala wannan rahoto.