Kasancewar “Taiwan A Matsayin Lardin Kasar Sin” Shi Ne Matsayin MDD A Ko Yaushe
Published: 10th, March 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Sin, Wang Yi ya bayyana a wajen taron manema labaru na ministan harkokin waje da aka shirya a harabar manyan tarukan kasar Sin guda biyu, lokacin da yake magana kan batun Taiwan cewa: suna daya tilo na Taiwan a Majalisar Dinkin Duniya shi ne “Lardin Taiwan na kasar Sin”.
Da take mayar da jawabi game da wannan batu, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Mao Ning, ta bayyana a wani taron manema labarai da aka saba gudanarwa da ya gudana yau 10 ga wata cewa, wannan shi ne daidaitaccen matsayin MDD a ko yaushe kuma haka abun yake a tarihi.
Mao Ning ta jaddada cewa, a ko da yaushe kasar Sin tana bin ka’idar kasancewar Sin daya tak, da kuma ra’ayi daya da aka samu na shekarar 1992, kana tana matukar son yin kokari don ganin an samu damar dinkuwar kasar Sin cikin lumana da gaskiya da sa himma. A sa’i daya kuma, kasar Sin za ta dauki dukkan matakan da suka dace don kare ikon mallakar kasarta da cikakken ‘yancin yankinta, da kuma fitowa da kakkausan harshe wajen nuna adawa da ayyukan ‘yan aware na neman ‘yancin kai na Taiwan da tsoma baki daga waje. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Gobara ta ƙone kasuwar katako a Abuja
Wata gobara ta tashi a ranar Laraba ta ƙone kasuwar katako da ke kusa da Jabi Masallaci a Abuja.
Gobarar ta lalata kaya da kayan gini na miliyoyin kuɗi, amma ba a yi asarar rai ba.
CBN ya kara yawan kudin da mutum zai iya cirewa a mako zuwa N500,000 Gobara ta kashe mata da miji da ’ya’yansu 3 a KatsinaKawo yanzu dak ba a san musababbin tashin gobarar ba.
Sai dai wasu rahotanni na cewa gobarar na iya farawa ne sakamakon matsalar wutar lantarki, wanda wani lokacin wayoyin wuta na faɗowa kan rumfunan kasuwa.
’Yan kasuwa da mazauna yankin sun yi ƙoƙarin kashe wutar, amma ta yaɗo cikin sauri saboda katako da sauran kayayyakin gini na da saurin kamawa da wuta.
Wasu gine-gine da ke kusa da kasuwar sun lalace, lamarin da ya tilasta wa jama’a gudu domin tsira da rayukansu.
Daga baya jami’an Hukumar Kashe Gobara ta Tarayya sun isa wajen tare da kashe wutar.
Mutanen da abin ya shafa sun roƙi gwamnati ta taimaka musu, domin sun rasa duk abin da suka dogaro da shi wajen kula da rayuwarsu.