Sa’adatu Ali JC ta raba wa mata 150 injinan markaɗe a Gombe
Published: 9th, March 2025 GMT
A yayin bikin Ranar Mata ta Duniya, Hajiya Sa’adatu Ali Isa JC, matar Ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar Balanga da Billiri, ta tallafa wa mata 150 da injinan markaɗe domin su samu hanyar dogaro da kai.
Da ta ke jawabi yayin rabon kayan, Hajiya Sa’adatu ta ce manufar wannan tallafi ita ce taimaka wa mata su samu sana’a da za ta rage musu dogaro da wasu.
“Wannan tallafi yana da muhimmanci domin zai taimaka wa mata su kula da kansu da iyalansu ba tare da jira komai daga mazajensu ba.
“Wannan kuma wani yunƙuri ne na taimakon jama’a kamar yadda maigidana, Hon. Ali Isa JC, ke yi a kodayaushe,” in ji ta.
Ta bayyana cewa mijinta ya tallafa wa mutum sama da 2,000 da kayan abinci da na noman rani don rage yunwa a cikin al’umma.
Haka kuma, ta taɓa koyawa wasu mata sana’ar yin takalma, wanda har takalmansu ke zuwa ƙasashen waje saboda ingancinsu.
Hajiya Sa’adatu ta ja hankalin matan da suka amfana da injinan da ka da su sayar da su, sai dai su yi amfani da su don amfanin kansu da iyalansu.
“Idan kuka yi amfani da wannan tallafi yadda ya kamata, zai zamo muku wata babbar hanya ta samun riba kamar yadda waɗanda suka koyi sana’ar takalma suka samu nasara,” inji ta.
Sannan ta yi kira ga masu hali da su taimaka wa jama’a, ba sai ‘yan siyasa kaɗai ba, domin hakan zai rage zaman banza da talauci a cikin al’umma.
Wasu daga cikin matan da suka amfana sun jinjina mata, inda suka ce ta zama abin koyi a cikin mata.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɗan Majalisa Injinan Markaɗe Matar Ali JC Rage Talauci
এছাড়াও পড়ুন:
Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya
A halin yanzu, sama da mata da yarinya miliyan 600 a duniya suna cikin rikici da yaki, sannan mata da ‘yan mata biliyan 2 ba su da tabbacin tsaron zamantakewa. Kamar yadda babban sakataren MDD Antonio Guterres ya bayyana, cewar har yanzu ci gaban mata a duniya yana fuskantar “kalubale da ba a taba ganin irinsa ba”, kasashe suna bukatar kuduri da hikima don magance matsalolin mata. A lokacin kaka na shekara ta 2025, daga Beijing za a sake samun ci gaba, wato Sin tana fatan ta kara hada kai da sauran bangarori, don hanzarta cikakken ci gaban mata, da kuma ba da gudummawar mata don ciyar da ci gaban bil’adama gaba. (Amina Xu)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA