Aminiya:
2025-12-13@14:03:38 GMT

Sa’adatu Ali JC ta raba wa mata 150 injinan markaɗe a Gombe

Published: 9th, March 2025 GMT

A yayin bikin Ranar Mata ta Duniya, Hajiya Sa’adatu Ali Isa JC, matar Ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar Balanga da Billiri, ta tallafa wa mata 150 da injinan markaɗe domin su samu hanyar dogaro da kai.

Da ta ke jawabi yayin rabon kayan, Hajiya Sa’adatu ta ce manufar wannan tallafi ita ce taimaka wa mata su samu sana’a da za ta rage musu dogaro da wasu.

PDP ta sake ɗage babban taronta zuwa Mayun 2025 An samu tsohon shugaban hukumar tsaron Faransa da zamba

“Wannan tallafi yana da muhimmanci domin zai taimaka wa mata su kula da kansu da iyalansu ba tare da jira komai daga mazajensu ba.

“Wannan kuma wani yunƙuri ne na taimakon jama’a kamar yadda maigidana, Hon. Ali Isa JC, ke yi a kodayaushe,” in ji ta.

Ta bayyana cewa mijinta ya tallafa wa mutum sama da 2,000 da kayan abinci da na noman rani don rage yunwa a cikin al’umma.

Haka kuma, ta taɓa koyawa wasu mata sana’ar yin takalma, wanda har takalmansu ke zuwa ƙasashen waje saboda ingancinsu.

Hajiya Sa’adatu ta ja hankalin matan da suka amfana da injinan da ka da su sayar da su, sai dai su yi amfani da su don amfanin kansu da iyalansu.

“Idan kuka yi amfani da wannan tallafi yadda ya kamata, zai zamo muku wata babbar hanya ta samun riba kamar yadda waɗanda suka koyi sana’ar takalma suka samu nasara,” inji ta.

Sannan ta yi kira ga masu hali da su taimaka wa jama’a, ba sai ‘yan siyasa kaɗai ba, domin hakan zai rage zaman banza da talauci a cikin al’umma.

Wasu daga cikin matan da suka amfana sun jinjina mata, inda suka ce ta zama abin koyi a cikin mata.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗan Majalisa Injinan Markaɗe Matar Ali JC Rage Talauci

এছাড়াও পড়ুন:

Mahajjata 2,235 Ne Suka Yi Rijistar Aikin Hajjin 2026 A Sokoto

A cewar Musa, shirye-shiryen sun hada da jigilar kayayyakin tafiya, masaukai da kammala yarjejeniyar ciyarwa da hukumomin da suka dace a Kasar ta Saudiyya.

 

A cewarsa, adadin mahajjatan da suka yi rajistar ya hada har da jami’an gwamnati.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai ‘Yan Siyasa Ne Ke Zagon Ƙasa Ga Ci Gaban Nijeriya — Sarki Sanusi II December 11, 2025 Labarai Kotu Ta Yanke Wa Wani Mutum Hukuncin Kisa Bisa Garkuwa Da Kashe Mai Gidansa A Kano December 11, 2025 Manyan Labarai Katsina Ta Amince Da Bayar Da Alawus Na Naira 30,000 Duk Wata Ga Malaman Karkara December 11, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan sanda sun ba da tabbacin isasshen tsaro a zaɓen ƙananan hukumomin Borno
  • Yadda za ku cike neman aikin jami’an lafiya a Hajjin 2026 da NAHCON
  • Yadda za ku nemi aikin jami’an lafiya a Hajjin 2026 da NAHCON
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince da Sama da Naira Biliyan 2.6 Domin Aikin Hajjin 2026
  • Iyaye Sun Yi Fitowar Farin Dango Don Yi Wa “Yayansu Allurar Rigakafi a Sule-Tankarkar
  • 2027: Jam’iyyar NNPP ta rantsar da sabbin shugabanni a Gombe
  • Yadda APC Da ADC Ke Amfana Da Rikicin Jam’iyyar PDP
  • Mahajjata 2,235 Ne Suka Yi Rijistar Aikin Hajjin 2026 A Sokoto
  • Ma’aikatar Mata da Walwalar Jama’a ta Jihar Jigawa ta Kare Kasafin Kudinta a Gaban Majalisa
  • Shugaban Kasar Iran Yace Mata Su ne Ginshin Gina Makomakar Kowacce Kasa