Aminiya:
2025-04-30@23:05:59 GMT

Makahon da ke sana’ar POS

Published: 9th, March 2025 GMT

Isyaku Mahmud, makaho ne dan shekara 28 da ke sana’ar sayar da data a yankin Kudancin Kaduna.

Ya shaida wa Aminiya cewa har sana’ar hada-hadar kudi ta POS yana yi a baya, amma yanzu ba shi da jari.

Ta’addancin yankin Sahel ya ninka na sauran sassan duniya — Rahoto Yadda masana’antun Arewa suka koma kufai

Aminiya ta ga yadda makahon yake sarrafa manhajojin WhatsApp is Fesbuk kuma yake sayar da data kai tsaye daga wayarsa ta hanyar amfani da tsarin Smart Cash tare da tura kudi da wayar tasa, kamar yadda ya gwadawa wakilinmu.

Dan asalin garin Yalwa da ke Karamar Hukumar Tudun Wada (Dan Kadai) da ke Jihar Kano ne, ya kwashe shekaru kusan biyar yana zuwa yawon bara a garin Kafanchan da ke Jihar Kaduna.

Aminiya ta samu zantawa da shi, inda ya gwada duk abubuwan da yake yi da wayarsa ciki, har da lalubo wakar da ya yi ya kuma tura cikin wani zaure na mawaƙa ba tare da wani ya nuna masa ko ya taimaka ba.

Yana iya kuma tattaunawa da kowa ta hanyar sauti a manhajar WhatsApp tunda bai iya rubutu ba.

Amma da kansa yake budewa ya lalubo wanda yake son tura wa da sako kuma ya tura masa.

“Ka san ina yin wakokin yabon Manzon Allah. Idan na samu ƙarin baitin sai na ɗauko wayata na rera tunda ba zan iya rubutawa ba.

“Idan na gama hada adadin baitukan da nake so akwai dalibai ’yan Islamiyya, sai na ba su muje inda ake buga wakoki a studiyo, sai su hau su rera.

“Ba ni nake rerawa ba, amma duka wakokina ne. A can garinmu nake wannan kuma a yanzu haka ina da kasidu da aka buga sun haura guda 20.

“An haife ni ne a shekarar 1997, an shaida min cewa an haife ni da idanu na garai, amma bayan an yaye ni, a shekarar sai mahaifiyata ta rasu kuma tun daga nan sai na daina gani, wato na makance, shine har zuwa yau kuma,” in ji shi.

Ya ce ya yi karatun tsangaya kafin daga baya aka matsa masa cewa sai ya fita yawon bara.

“Saboda haka ba a son raina nake bara ba, amma a lokacin babu wani abu da zan iya yi. Wannan ya faru ne a shekarar 2012 tun lokacin nake bara.”

Ya ce da zai samu wani tallafi na jari, a shirye yake ya yi wasu sana’o’i ko buɗe shagon harkar POS ko wani abu da zai iya dogaro da shi musamman yanzu da yake da yara ƙananan guda biyu da yake son su samu kulawa ta musamman tare da yin karatu mai zurfi.

“Ina da mata daya da ƙananan yara guda biyu kuma gaskiya ina son su yi karatu duka na addini da na boko.”

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Za a rataye wani soja saboda laifin kashe budurwarsa

Wata koutun soja ta yanke wa wani jami’inta hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan samun sa da laifn kashe buduwarsa.

Kotun da ta zauna a Hedikwatar Runduna ta 82 da ke Enugu, ta yanke wa Private Adamu Mohammed hukuncin kisa kan laifin budurwar taas mai suna Hauwa Ali.

Da yake sanar da hukuncin, Shugaban kotun, Birgediya Sadisu Buhari, ya ce, “Kotun Soja ta Kasa ta yanke hukuncin cewa sojan da ake tuhuma, mai lamba 21NA/80/6365 Private Adamu Mohammed, an yanke masa hukuncin kisa ta hanyar rataya bisa tuhumar kisan kai.”

Mukaddashin kakakin Rundunar, Jonah Unuakhalu, ya ce kwamitin kotun  ya cimma matsaya ɗaya bayan nazari mai zurfi na shaidu, tarihin aikin wanda ake tuhuma, da kuma roƙon sassauci daga lauyansa.

Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok Kano: Galadima biyu a masarauta ɗaya Bom ɗin Boko Haram ya kashe mutane 26 a Borno

Ya shaida wa manema labarai a Abuja cewa kotun sojan, ta kuma yanke wa wani Soja mai suna Private Abubakar Yusuf hukuncin ɗaurin shekaru 10 a kurkuku saboda samun sa da laifin fashi da makami a wani shahararren kantin sayayya a Enugu.

Ya kara da cewa an yanke wa waɗannan mutane biyu hukuncin ne bayan kammala shari’o’insu kan laifukan kisan kai da fashi da makami.

Babban Kwamandan Runduna ta 82, Manjo-Janar Oluyemi Olatoye, ne ya kaddamar da kotun sojin a ranar 18 ga Fabrairu, 2025, domin yanke hukunci kan shari’o’in da suka shafi ma’aikatan da suka yi kuskure a cikin Rundunar.

A cewarsa, waɗannan hukunce-hukuncen sai sun samu tabbatarwa daga hukumomin soji da suka dace, wanda ya nuna ƙarshen shari’o’in sojojin.

Ya sake jaddada ƙudurin Sojojin Najeriya na tabbatar da ɗa’a da kuma kiyaye mafi girman ƙa’idoji na ɗabi’u da ƙwarewa.

“Kuskuren ayyukan wasu kaɗan ba su nuna ƙimar ƙungiyar ba. A koyaushe ana ɗaukar matakai masu sauri da kuma ƙarfi don tabbatar da riƙon amana da adalci,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran ta sha alwashin ci gaba da aiwatar da manufofinta na raya dangantakarta da Nijar
  • Rawar da Arewa za ta taka a Zaɓen 2027
  • Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
  • Ta yi wa saurayinta ƙaryar shekarunta 27 maimakon 47
  • An dawo da wutar lantarki a Sifaniya da Portugal
  • Za a rataye wani soja saboda laifin kashe budurwarsa
  • Makiyayi Ya Kashe Abokai 2 A Nasarawa Kan Rikicin Kiwo
  • Makafi 37 Sun Zana Jarabawar JAMB A Bauchi
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jadadda Cewa: Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kan Iran Zai Fuskanci Mayar Da Martani
  • Yadda matar gwamna ta sa mata gasar haihuwar ’yan uku