Isyaku Mahmud, makaho ne dan shekara 28 da ke sana’ar sayar da data a yankin Kudancin Kaduna.
Ya shaida wa Aminiya cewa har sana’ar hada-hadar kudi ta POS yana yi a baya, amma yanzu ba shi da jari.
Ta’addancin yankin Sahel ya ninka na sauran sassan duniya — Rahoto Yadda masana’antun Arewa suka koma kufaiAminiya ta ga yadda makahon yake sarrafa manhajojin WhatsApp is Fesbuk kuma yake sayar da data kai tsaye daga wayarsa ta hanyar amfani da tsarin Smart Cash tare da tura kudi da wayar tasa, kamar yadda ya gwadawa wakilinmu.
Dan asalin garin Yalwa da ke Karamar Hukumar Tudun Wada (Dan Kadai) da ke Jihar Kano ne, ya kwashe shekaru kusan biyar yana zuwa yawon bara a garin Kafanchan da ke Jihar Kaduna.
Aminiya ta samu zantawa da shi, inda ya gwada duk abubuwan da yake yi da wayarsa ciki, har da lalubo wakar da ya yi ya kuma tura cikin wani zaure na mawaƙa ba tare da wani ya nuna masa ko ya taimaka ba.
Yana iya kuma tattaunawa da kowa ta hanyar sauti a manhajar WhatsApp tunda bai iya rubutu ba.
Amma da kansa yake budewa ya lalubo wanda yake son tura wa da sako kuma ya tura masa.
“Ka san ina yin wakokin yabon Manzon Allah. Idan na samu ƙarin baitin sai na ɗauko wayata na rera tunda ba zan iya rubutawa ba.
“Idan na gama hada adadin baitukan da nake so akwai dalibai ’yan Islamiyya, sai na ba su muje inda ake buga wakoki a studiyo, sai su hau su rera.
“Ba ni nake rerawa ba, amma duka wakokina ne. A can garinmu nake wannan kuma a yanzu haka ina da kasidu da aka buga sun haura guda 20.
“An haife ni ne a shekarar 1997, an shaida min cewa an haife ni da idanu na garai, amma bayan an yaye ni, a shekarar sai mahaifiyata ta rasu kuma tun daga nan sai na daina gani, wato na makance, shine har zuwa yau kuma,” in ji shi.
Ya ce ya yi karatun tsangaya kafin daga baya aka matsa masa cewa sai ya fita yawon bara.
“Saboda haka ba a son raina nake bara ba, amma a lokacin babu wani abu da zan iya yi. Wannan ya faru ne a shekarar 2012 tun lokacin nake bara.”
Ya ce da zai samu wani tallafi na jari, a shirye yake ya yi wasu sana’o’i ko buɗe shagon harkar POS ko wani abu da zai iya dogaro da shi musamman yanzu da yake da yara ƙananan guda biyu da yake son su samu kulawa ta musamman tare da yin karatu mai zurfi.
“Ina da mata daya da ƙananan yara guda biyu kuma gaskiya ina son su yi karatu duka na addini da na boko.”
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
A wani bidiyo daban da PUNCH Metro ta gani a Facebook, wanda Mc Pee ya wallafa, wani mutum da ake zargin dalibi ne na jami’ar ya bayyana abin da ya faru.
A cewarsa, marigayin ya roki a bar shi ya rayu kafin daga bisani wanda ake zargin ya kashe shi.
Ya ce: “Nanpon ya riga ya yanke Peter a kumatunsa yayin da yake rokon a bar shi. Lokacin da muka shiga tsakani muka ce ya daina, sai ya yi barazanar yanka duk wanda ya kusanto shi.
“Da Peter ya ga ba ya sauraron rokonsa, sai ya rungume shi yana rokonsa da kuka.
“Mun fita neman taimako amma babu wanda ya amsa mana. Da Peter ya yi kokarin tserewa sai ya fadi, Nanpon ya kamo shi ya ci gaba da saransa da adda.”
Wani kwararren masanin tsaro da yaki da ta’addanci ya wallafa a dandalin D a ranar Lahadi cewa jami’an rundunar ‘yan sandan Jihar Filato sun kama wanda ake zargin.
Ya kuma ambaci majiyoyi da suka tabbatar da faruwar lamarin ta hanyar rahoton da aka samu daga Babban Jami’in Tsaro na jami’ar.
Ya rubuta cewa, “Rundunar ‘Yansanda ta Filato ta kama wani dalibi mai shekaru 23 na Jami’ar Jos bisa zargin kashe abokinsa sannan ya binne shi a rami mara zurfi a cikin dakinsa da ke kauyen Rusau a Karamar Hukumar Jos ta Arewa.
“Majiyoyi sun tabbatar da faruwar lamarin a ranar Lahadi a Jos, inda suka danganta da rahoton da aka samu daga Babban Jami’in Tsaron jami’ar.
“A cewar majiyoyin, wanda ake zargin mai suna Dabid Nanpon Timmap, dalibi a matakin shekara ta uku a jami’ar, ya kai wa Peter Mata Mafurai, mai shekaru 22, hari da adda, ya kashe shi a gidansa.”
Zagazola ya kara da cewa, bayan samun kiran gaggawa da misalin karfe 9:30 na safiya, DPO na sashin Laranto ya jagoranci tawagar ‘yansanda zuwa wurin, inda aka kama wanda ake zargin.
“Majiyoyin sun ce bincike ya nuna cewa wanda ake zargin ya binne mamacin a cikin rami mara zurfi da ya haka a cikin dakinsa. An tono gawar kuma an kai ta dakin ajiye gawarwaki na Asibitin koyarwa na Jami’ar Bingham domin yin binciken gawar (autopsy),” in ji shi.
Ya kara da cewa, an tsare wanda ake zargin yayin da ake ci gaba da bincike domin gano hakikanin dalilin kashe abokin nasa.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA