Har ila yau, kwamishinan ma’aikatar Dr. Ali Haruna Abubakar Makoda ya bukaci iyaye da daliban makarantun da su tabbatar sun koma makaranta a ranar da aka ware.

 

Ya yi gargadin cewa, za a dau matakin ladabtarwa a kan Daliban da suka gaza bin doka.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku.

Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Zamfara ta amince da naɗin sabon Sarkin Katsinan Gusau

Gwamnan Zamfara, Dauda Lawal ya amince da naɗin Alhaji Abdulkadir Ibrahim Bello a matsayin sabon Sarkin Katsinan Gusau.

Sakataren Gwamnatin Zamfara, Malam Abubakar Mohammad Nakwada ne ya bayyana haka a wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Suleman Ahmad Tudu ya fitar a Talatar nan.

Ambaliya ta yi ajalin mutum 30 a China ’Yan bindiga sun kashe mutum 5 a sabon hari a Alkaleri

Sanarwar ta ce an yi amfani da dokoki da tanade-tanaden doka ne wajen amincewa da naɗin wanda masu zaɓen sarkin masarautar suka zaɓa.

Gwamna Lawal ya taya sabon sarkin murna, sannan ya yi kira gare shi da ya yi koyi da magabatansa, musamman ganin shi tsatson Malam Sambo Ɗan Ashafa ne.

Ya kuma yi kira ga sabon sarki ya dage wajen kira da samun haɗin kai da ci gaban masarautar Gusau da jihar, da ma ƙasar baki ɗaya.

Alhaji Abdulkadir zai ɗare karagar ne a matsayin Sarki na 16 na masarautar, inda zai maye gurbin mahaifinsa, Marigayi Mai martaba Dr. Ibrahim Bello, wanda ya rasu a ranar 25 ga watan Yulin 2025.

Sabon sarkin ne babban ɗan marigayin, kuma kafin naɗa shi sarki, shi ne Bunun Gusau.

Ana iya tuna cewa, a Juma’ar makon jiya ce aka samu rahoton rasuwar Sarkin Katsinan Gusau, Dokta Ibrahim Bello yana da shekara 71 da haihuwa.

Sarkin ya rasu ne a daren Juma’a 24 ga watan Yulin 2025 bayan doguwar jinya a wani asibiti da ke Abuja, babban birnin Nijeriya.

Sanarwar da gwamnatin Zamfarar ta fitar ta ce: “Rasuwar mai martaba babban rashi ne ga Jihar Zamfara da ma daukacin Arewacin Nijeriya.”

Gwamna Dauda Lawal ne ya jagoranci jana’izar sarkin a Babban Masallacin Juma’a na Kanwuri da ke birnin Gusau.

A watan Maris na 2015 aka naɗa marigayi Dokta Ibrahim Bello a matsayin sarkin Gusau na 15, inda ya maye gurbin ɗan’uwansa Alhaji Muhammad Kabiru Danbaba bayan rasuwarsa.

Marigayin ya bar mata da ’ya’ya sama da 20.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwar Sin Da Amurka
  • Gwamnatin Kano Ta Kammala Gyaran Makarantu Sama Da 1,200 A Kananan Hukumomi 44
  • Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu
  • Gwamnatin Zamfara ta amince da naɗin sabon Sarkin Katsinan Gusau
  •  Kasar Holland Ta Hana MInistocin HKI Biyu Shiga Cikin Kasarta
  • Gwamnonin Nijeriya Sun Yi Ta’aziyyar Waɗanda Suka Rasu A Ambaliyar Ruwa A Adamawa
  • Gwamnan Zamfara Ya Naɗa Abdulkadir Ibrahim A Matsayin Sabon Sarkin Katsinan Gusau Na 16
  • EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Akwa Ibom