Gwamnatin Kano Ta Amince Juma’a 28 Ga Fabrairu A Matsayin Ranar Hutun Zangon Karatu Na Biyu
Published: 25th, February 2025 GMT
Har ila yau, kwamishinan ma’aikatar Dr. Ali Haruna Abubakar Makoda ya bukaci iyaye da daliban makarantun da su tabbatar sun koma makaranta a ranar da aka ware.
Ya yi gargadin cewa, za a dau matakin ladabtarwa a kan Daliban da suka gaza bin doka.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku.
এছাড়াও পড়ুন:
An samu gobara a wasu matatun mai guda biyu na Iran bayan harin da Isra’ila ta kai
Wasu Hare-haren da gwamnatin Isra’ila ta kai ya haddasa gobara a wasu matatun mai a lardin Bushehr da ke kudancin kasar Iran.
Gobarar ta tashi ne a wurin a ranar Asabar bayan da wasu kananan jiragen yakin Isra’ila guda biyu suka kai hare-hare a kan kayayyakin sarrafa iskar gas da ke yankin kudancin Pars.
Hare-haren sun yi haddassa fashe fashe a matatar iskar gas ta Fajr-e Jam, daya daga cikin mafi girma a Iran, da kuma wata karamar matatar mai a mataki na 14 na tashar iskar gas ta Kudu Pars.
Har yanzu ba a fitar da kiyasin barnar a hukumance ba.
Bayan gobarar, ma’aikatar mai ta Iran ta fitar da wata sanarwa inda ta tabbatar da harin.
Sanarwar ta ce, nan da nan aka kaddamar da aikin shawo kan gobarar da dakile ta.”
Matatar man ta Pars ta kudu ita ce tashar iskar gas mafi girma a duniya, wacce ke kan iyakar teku tsakanin Iran da Qatar.
Ta kunshi sama da kashi 70% na bukatun iskar gas na Iran.