Leadership News Hausa:
2025-07-31@22:25:52 GMT

Matar Gwamnan Kebbi Ta Rarba Tallafin Kayan Noma Ga Mata Manoma 100 

Published: 25th, February 2025 GMT

Matar Gwamnan Kebbi Ta Rarba Tallafin Kayan Noma Ga Mata Manoma 100 

nkin.

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An Horas Da Mata 600 Kan Abincin Yara Mai Gina Jiki A Jigawa

A wani yunkuri na yaki da rashin abinci mai gina jiki da kuma karfafa tattalin arzikin mata a jihar Jigawa, Gwamna Umar Namadi ya jagoranci bikin yaye mata 600 da suka samu horo kan yadda ake sarrafa abincin yara mai gina jiki daga kayayyakin da ake samarwa a gida, wanda aka fi sani da “Tom Brown”.

Malam Umar Namadi ya bayyana wannan shiri a matsayin wata dabara ta cikin gida da aka kirkira domin shawo kan matsalolin rashin abinci mai gina jiki a tsakanin yara, da kuma karfafa tattalin arzikin mata.

“Muna matukar godewa Allah da ya ba mu hikima da basira don kirkirar wannan tsari wanda zai taimaka mana mu cimma manufofi da dama a lokaci guda.” In ji shi.

“Bayan bai wa wadanda aka horar damar samun ingantacciyar hanyar dogaro da kai, wannan kuma wata babbar dabara ce wajen yaki da rashin abinci mai gina jiki a cikin yara. Hakan kuma zai taimaka wajen hana matsalolin nakasa a kwakwalwa, domin kare damar girman yaron yadda ya dace.”

Gwamnan ya jaddada cewa Tom Brown, wanda wasu ke kira da Kwashpap, an tabbatar da ingancinsa wajen magance matsalar rashin matsakaicin abinci mai gina jiki (Moderate Acute Malnutrition – MAM) ta hanyar hadin kayan gida kamar gero, gyada da wake.

Ya kara da cewa wannan shiri na da cikakken daidaito da manufofin gwamnatin jihar na bunkasa abinci mai gina jiki, wanda ya fara haifar da sakamako mai kyau.

A cewarsa, kowace daga cikin matan 600 da suka amfana da shirin ta samu kayan fara sana’a da suka hada da injin rufe roba da kayan masarufi domin farawa da sarrafa Tom Brown a matakin gida.

Namadi ya bayyana cewa kananan hukumomi da cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko a fadin jihar za su hada gwiwa domin tabbatar da amfani da kuma shigar da wadannan kayayyaki cikin shirye-shiryen inganta abincin yara.

Ya ce, horar da wadannan mata 600 wani bangare ne na kokarin gwamnati wajen hanzarta samun ci gaba a fannin kula da rayuwar al’ummar,  da ingantacciyar lafiyar yara.

Gwamna Namadi ya kuma sake jaddada kudirin gwamnatinsa na rage dogaro da kayan abinci masu tsada da ake shigowa da su daga kasashen waje, ta hanyar bunkasa hanyoyin cikin gida masu saukin samu da kuma arha.

Ya sanar da cewa jihar Jigawa na cikin jerin jihohin da ke amfana da shirin ANRiN na Bankin Duniya, wanda ke mayar da hankali kan kara samun damar kula da lafiyayyen abinci ga mata da yara ‘yan kasa da shekaru biyar.

“Babban burin wannan shiri shi ne kara yawan amfani da ingantattun hanyoyin kula da abinci ga mata masu juna biyu da masu shayarwa da kuma yara ‘yan kasa da shekaru biyar. Wannan yana da nasaba da hangenmu cewa shirin ANRiN zai taka rawar gani wajen hanzarta ci gabanmu ta bangaren samar da abinci mai gina jiki ga yara.”

 

Usman Muhammad Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Horas Da Mata 600 Kan Abincin Yara Mai Gina Jiki A Jigawa
  • Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza
  • Tallafin matar Tinubu na N1bn ga ’yan gudun hijirar Binuwai ya bar baya da kura
  • Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega
  • Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma
  • Gwamnan Kaduna Ya Sauke Kwamishinan Yaɗa Labarai, Ya Maye Gurbinsa Da Maiyaki
  • An Kaddamar da Makon MNCH na 2025, Ya Rarraba Fakitin Bayarwa 6,000, Kayan C/S 500
  • Jami’ar Jihar Gombe za ta fara sabbin darussa 6 a fannin noma
  • Gwamnan Zamfara Ya Naɗa Abdulkadir Ibrahim A Matsayin Sabon Sarkin Katsinan Gusau Na 16
  • Tsohon Ɗan Takarar Mataimakin Gwamnan Kaduna Na PDP Ya Koma ADC