Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-05-01@02:47:17 GMT

NEMA Ta Bada Tallafi Ga Wadanda Gobara Ta Shafa A Kauran Namoda

Published: 10th, February 2025 GMT

NEMA Ta Bada Tallafi Ga Wadanda Gobara Ta Shafa A Kauran Namoda

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa NEMA ta gabatar da kayan agaji ga gwamnatin jihar Zamfara domin tallafawa wadanda gobara ta shafa a wata makarantar Islamiyya da ke Kaura Namoda.

 

A lokacin da take mika  kayayyakin, Darakta Janar na Hukumar Hajia Zubaida Umar, ta ce matakin ya nuna damuwar gwamnatin tarayya kan halin da wadanda abin ya shafa ke ciki.

Babbar Daraktar wanda shugaban NEMA shiyar Sokoto, Aliyu Shehu Kafindangi ya wakilta, ya ce tallafin ya hada da kayan abinci kamar buhunan shinkafa, da masara, da man girki, da kayayyakin amfani  gida.

A baya dai Hajiya Zubaida Umar ta ziyarci wadanda lamarin ya rutsa da su wadanda har yanzu suke ci gaba da karbar magani a asibitin mata da yara na Khadijah da ke Kaura Namoda.

A asibitin, wakilin na shugabar ta NEMA, ya kuma gabatar da kayayyakin jinya ga hukumar lafiya matakin farko domin ci gaba da kula da wadanda abin ya shafa.

Ya kuma jagoranci tawagar masu ruwa da tsaki da suka hada da wakilan hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Zamfara ZEMA, da  ma’aikatar jin kai ta jihar Zamfara, da kuma karamar hukumar Kaura Namoda zuwa wurin da lamarin ya faru domin jajanta wa makarantar.

Wadanda suka karbi kayayyakin da hukumar ta NEMA ta bayar, a madadin gwamnatin jihar sun hada da babban sakatariyar hukumar ta ZEMA, wadda Daraktan Yaki da iftila’i, Hassan Usman Dauran, da wakilta, da Sarkin Kaura-namoda, Alhaji Sanusi Muhammad Asha da kuma kwamishinan ma’aikatar jin kai ta jihar Zamfara, wanda babban sakataren ma’aikatar  Mohammed Bashir Maradun ya wakilta.

Haka kuma tawagar ta kai ziyarar ban girma ga Sarkin Kaura-namoda, Alhaji Sanusi Muhammad Asha a fadarsa.

Tun da farko, Sarkin Kauran Namoda, Alhaji Sanusi Asha, ya yi alkawarin sanya ido kan rabon kayan abincin ga wadanda abin ya shafa da kwamitin bayar da agajin gaggawa da gwamnatocin jihohi da kananan hukumomi suka kafa.

Hakazalika, ZEMA da ma’aikatar jin kai ta jihar, sun yabawa hukumar NEMA bisa wannan karimcin.

Daga Aminu Dalhatu

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kauran Namoda jihar Zamfara Kaura Namoda

এছাড়াও পড়ুন:

Sama Da Masu Sayayya Daga Ketare 220,000 Ne Suka Halarci Bikin Baje Kolin Canton Karo Na 137

 

Bikin baje kolin na wannan karo da ake gudanarwa a birnin Guangzhou dake kudancin kasar Sin daga ranar 15 ga watan Afrilu zuwa ranar 5 ga watan Mayu, an shirya shi ne cikin matakai uku. Matakin farko ya mayar da hankali ne kan masana’antu masu ci gaba, na biyu a kan ingantattun kayayyakin gida, na uku kuma a kan kayayyakin dake sa kaimi ga inganta rayuwa. (Mohammed Yahaya)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe Falasdinawa kusan 30 a wani sabon kisan kiyashin Isra’ila a Gaza
  • NEMA Ta Karɓi ‘Yan Nijeriya 203 Da Suka Maƙale A Libya
  •  Bom Da Ya Tashi A Arewa Maso Gabashin Najeriya Ya Kashe Mutane 6
  •  Falasdinawa 40 Sun Yi Shahada A Cikin Sa’oi 24 A Gaza
  • Gwamna Namadi Ya Nada Aisha Mujaddadi Sabuwar Shugabar Hukumar InvestJigawa
  • Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok
  • Shugaban Kungiyar Hizbullah Ya Abbaci Abubuwa 3 Wadanda Yakamata Kasar Ta Maida Hankali A Kansu
  • Hajjin 2025: An Fara Yi Wa Maniyyata Allurar Rigakafi A Jigawa
  • Sama Da Masu Sayayya Daga Ketare 220,000 Ne Suka Halarci Bikin Baje Kolin Canton Karo Na 137
  • Jagora Ya Bada Umurnin A Gudanar Bincike Mai Zurfi A Fashewar Tashar Jiragen Ruwa Na Shaheed Rajae