Aminiya:
2025-05-01@09:35:57 GMT

Netanyahu zai gurfana a kotu kan cin hanci

Published: 10th, February 2025 GMT

Fira Ministan Isra’ila, Banjamin Netanyahu, zai gurfana a kotu kan zargin aikata zamaba da karbar cin hanci da rashawa.

Za a gurfanar da Mista Netanyahu ne daomin ya amsa tambayoyi a shari’ar da aka jima ana zargin sa da aikata manyan laifuka uku na cin hanci da cin amana.

Masu gabatar da kara na zargin sa da aikata laifukan da suka hada da karbar cin hanci da zamba da kuma cin amana.

Laifukan sun hada da sa da daga kafar harajin Dala miliyan 500 ga kamfanin sadarwa na Bezeq Telecom domin kamfanin ya tallata shi da matarsa Sara a wani shafin yada labarai. Ɗan fashi ya yi wa ɗaliban jami’a uku fyaɗe ’Yan sanda na neman ’yan bola-jari ruwa a jallo a Abuja

A kan haka yake fuskantar zargin bayar da cin hanci da kuma cin amanar dukiyar al’umma da aka ba shi.

Ana kuma zargin shi da matarsa da karbar toshiyar baki ta Dalar Amurka 21,000 daga wani furodusa a masana’anatar fina-finan Amurka ta Hollywood, dan kasar Isra’ila mai suna Arnon Milchan, da wani attajirin kasar Australiya, James Packer.

Yana kuma fuskantar zargin kulla yarjejeniyar da mamallakin kamfanin jaridar Yedioh Ahronoth, Arnon Mozes, domin tallata shi, inda shi kuma zai yi dokar da za ta hana bunkasar wata jarida da ke gogayya da Yedioh Ahronoth.

A kan wannan kuma ana zargin Netanyahu da laifin zamba da kuma cin amana.

Tun shekarar 2020 Netanyahu yake fuskantar wadannan zarge-zarge, amma ya musanta aikata ba daidai ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Isra ila Netanyahu

এছাড়াও পড়ুন:

Syria: Adadin Wadanda Aka Kashe A Rikicin Bangaranci Sun Kai 70

Ma’aikatar harkokin wajen kasar Syria ta nuna kin amincewarta da tsoma bakin kasashen waje a rikicin da kasar take fuskanta.

Sanarwar ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Syria ta kuma ce; gwamnatin kasar za ta kare dukkanin ‘yan kasar.

Kasar Syria tana fuskantar fada a tsakanin ‘yan Duruz da kuma sojojin gwamnatin kasar a yankin Sahanaya da Ashrafiyyah a yankin Suwaida.

Ya zuwa yanzu dai adadin wadanda su ka rasa rayukansu sun kai 70.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Syria: Adadin Wadanda Aka Kashe A Rikicin Bangaranci Sun Kai 70
  • Gwamnatin Tarayya ta ayyana hutu gobe Alhamis
  • Munafunci Dodo Ya Kan Ci Mai Shi
  • Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
  • Kano: Galadima biyu a masarauta ɗaya
  • Kotu Ta Kori Ƙarar Neman Diyyar N1bn A Kan Buhari Da Emefiele Kan Sauya Fasalin Naira
  • Shugaban Majalisar Ƙoli ta Shari’ar Musulunci a Najeriya ya rasu
  • Yadda matar gwamna ta sa mata gasar haihuwar ’yan uku
  • Shekara 10 ina sayar da sassan jikin ɗan Adam — Wanda ake zargi
  • Falasdinu: Mahmud Abbas Ya Nada Magaji Da Kuma Mataimakasa