Netanyahu zai gurfana a kotu kan cin hanci
Published: 10th, February 2025 GMT
Fira Ministan Isra’ila, Banjamin Netanyahu, zai gurfana a kotu kan zargin aikata zamaba da karbar cin hanci da rashawa.
Za a gurfanar da Mista Netanyahu ne daomin ya amsa tambayoyi a shari’ar da aka jima ana zargin sa da aikata manyan laifuka uku na cin hanci da cin amana.
Masu gabatar da kara na zargin sa da aikata laifukan da suka hada da karbar cin hanci da zamba da kuma cin amana.
A kan haka yake fuskantar zargin bayar da cin hanci da kuma cin amanar dukiyar al’umma da aka ba shi.
Ana kuma zargin shi da matarsa da karbar toshiyar baki ta Dalar Amurka 21,000 daga wani furodusa a masana’anatar fina-finan Amurka ta Hollywood, dan kasar Isra’ila mai suna Arnon Milchan, da wani attajirin kasar Australiya, James Packer.
Yana kuma fuskantar zargin kulla yarjejeniyar da mamallakin kamfanin jaridar Yedioh Ahronoth, Arnon Mozes, domin tallata shi, inda shi kuma zai yi dokar da za ta hana bunkasar wata jarida da ke gogayya da Yedioh Ahronoth.
A kan wannan kuma ana zargin Netanyahu da laifin zamba da kuma cin amana.
Tun shekarar 2020 Netanyahu yake fuskantar wadannan zarge-zarge, amma ya musanta aikata ba daidai ba.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Syria: Adadin Wadanda Aka Kashe A Rikicin Bangaranci Sun Kai 70
Ma’aikatar harkokin wajen kasar Syria ta nuna kin amincewarta da tsoma bakin kasashen waje a rikicin da kasar take fuskanta.
Sanarwar ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Syria ta kuma ce; gwamnatin kasar za ta kare dukkanin ‘yan kasar.
Kasar Syria tana fuskantar fada a tsakanin ‘yan Duruz da kuma sojojin gwamnatin kasar a yankin Sahanaya da Ashrafiyyah a yankin Suwaida.
Ya zuwa yanzu dai adadin wadanda su ka rasa rayukansu sun kai 70.