HausaTv:
2025-07-31@16:33:25 GMT

Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Fara Janyewa Daga Yankin Netzarim Da Ke Zirin Gaza

Published: 9th, February 2025 GMT

Sojojin mamayar Isra’ila sun fara janyewa daga yankin Netzarim da ke tsakiyar Zirin Gaza

Kafofin yada labaran haramtacciyar kasar Isra’ila sun tabbatar da cewa: Sojojin mamayar Isra’ila za su fara ficewa daga yankin Netzarim da ke tsakiyar Zirin Gaza a daren jiya.

Jaridar Yedioth Ahronoth ta haramtacciyar kasar Isra’ila ta watsa rahoton cewa: Rundunar sojin mamayar Isra’ila ta ba da umarnin ficewa daga yankin Netzarim da ke tsakiyar Gaza a wani bangare na aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin kungiyar Hamas da gwamnatin mamayar Isra’ila a yankin.

Jaridar ta bayyana cewa: Runduna ta 162 ta sojojin mamayar ta sake matsawa zuwa kusa da kan iyaka da kuma janyewa daga yankin Netzarim na nufin cewa, babu sojojin mamayar Isra’ila a arewacin Zirin Gaza.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: daga yankin Netzarim da mamayar Isra ila

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Namadi Ya Biya Sama Da Naira Biliyan Daya Ga Tsofaffin Ma’aikata

Hukumar Tsarin Fansho na Hadin Gwiwa tsakanin Jiha da Kananan Hukumomi a Jihar Jigawa ta bayyana cewa ta raba sama da Naira Biliyan 1 da dubu 500 ga tsofaffin ma’aikata 569.

Yayin da yake jawabi ga wadanda suka ci gajiyar shirin a gaban Gidan Fansho kafin fara rabon kudin, Shugaban Ma’aikatan Gwamnatin Jihar, Alhaji Muhammad K. Dagaceri, ya bayyana tsarin fansho na jihar a matsayin daya daga cikin mafi nagarta a kasar nan.

A cewarsa, fiye da jihohi ashirin sun kai ziyara jihar Jigawa domin koyon yadda take tafiyar da shirin fansho.

Ya jinjina wa Gwamna Umar Namadi saboda dagewarsa da kuma jajircewarsa wajen dorewa da inganta tsarin fansho a jihar.

Alhaji Dagaceri ya yabawa Gwamna Namadi kan goyon bayansa da matakan da ya dauka tun bayan hawansa mulki domin inganta tsarin, yana mai jaddada irin tasirin alherin da shirin ke yi ga tsofaffin ma’aikata da daukacin ma’aikatan gwamnati.

Ya bukaci tsofaffin ma’aikata da wadanda ke aiki yanzu da su ci gaba da yi wa gwamnati addu’a, tare da nuna godiya ga Gwamna Namadi bisa irin ayyukan alherinsa.

A nasa jawabin, Shugaban hukumar ta Fansho, Dr. Binyaminu Shitu Aminu, ya bayyana cewa fiye da naira biliyan 1 da rabi ne za a raba tsakanin tsofaffin ma’aikata 569.

“Wannan adadi ya kunshi nau’o’in biyan kudi daban-daban, ciki har da hakkokin ritaya, hakkokin mutuwa da sauran ragowar hakkokin fansho na mamatan ma’aikata,” In ji Dr. Aminu.

Dr. Aminu ya kara da cewa, cikin wadanda za su amfana, 287 sun fito ne daga ma’aikatan jiha, 158 daga kananan hukumomi, yayin da 124 suka fito daga Hukumar Ilimin Kananan Hukumomi (LEA).

Ya kara da cewa, za a biya sama da Naira Miliyan 875 ga ma’aikatan da suka yi aiki a karkashin gwamnatin jiha, sannan sama da Naira Miliyan 355 kuma ga wadanda suka fito daga kananan hukumomi, da kuma sama da naira miliyan 274 ga wadanda suka fito daga LEA.

Shugaban hukumar ya tabbatar da cewa hukumar za ta ci gaba da biyan hakkokin fansho a kan kari, ciki har da biyan fansho na wata wata a cikin mako na farko na kowane wata.

 

Ya jaddada kudurin gwamnatin jihar na inganta walwalar ma’aikata, domin samun rayuwa mai kyau da kwanciyar hankali bayan kammala aikin.

Usman Muhammad Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza
  • Sojojin Yemen Sun Kai Zafafan Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila Guda Uku  
  • Adadin Falasdinawan da Isra’ila take kashewa a Gaza yanzu ya haura 60,000
  • Kasashen Yankin Caribbean Suna Son Bunkasa Alakarsu Ta Kasuwanci Da Nahiyar Afirka
  • Amincewa Da Kasar Falasɗinu: Birtaniya Ta Gindaya Wa Isra’ila Sharuɗɗa
  • DAGA LARABA: Dalilan al’ummomi na rungumar gwaji kafin aure
  • Sojojin HKI Sun Ci Gaba Da Kashe Kawunansu
  • Wani mutum ya mutu yayin raba faɗar ma’aurata 
  • An fara shigar da kayan agaji a Gaza
  • Gwamna Namadi Ya Biya Sama Da Naira Biliyan Daya Ga Tsofaffin Ma’aikata