Aminiya:
2025-08-01@05:05:34 GMT

Abba ya naɗa sabon Sakataren Gwamnatin Kano

Published: 9th, February 2025 GMT

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya naɗa Umar Farouk Ibrahim a matsayin sabon Sakataren Gwamnatin Kano.

Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwar da Kakakin Gwamnatin Kano, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a yammacin ranar Asabar.

Shigo da hatsi daga ƙetare ya karya farashinsa a Neja Ya yi wa kansa keji don daina shan sigari

Sanarwar ta ce naɗin sabon Sakataren Gwamnatin zai fara aiki ne a hukumance daga ranar Litinin mai zuwa 10, ga Fabarairun 2025.

Sanarwar ta ce an naɗa sabon Sakataren Gwamnatin wanda ya shafe sama da shekaru talatin yana aikin gwamnati la’akari da ƙwarewar aiki da yake da ita a hukumomi da ma’aikatu daban-daban na wajen ganin an cimma muradin gwamnati mai ci na ciyar da Jihar Kano gaba.

Naɗin na Umar Farouk Ibrahim na zuwa ne watanni biyu bayan sauke tsohon Sakataren Gwamnatin Kano, Dokta Baffa Abdullahi Bichi daga muƙamin a sakamakon dalilan rashin lafiya, kamar yadda sanarwar sauke shi ta bayyana haka a baya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Sakataren Gwamnatin Kano Umar Farouq Ibrahim sabon Sakataren Gwamnatin Gwamnatin Kano

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya naɗa sabon shugaban hukumar kashe gobara ta ƙasa

Shugaba Bola Tinubu ya amince da naɗin Olumode Samuel Adeyemi a matsayin sabon Shugaban Hukumar Kashe Gobara ta Ƙasa.

Sabon shugaban hukumar zai fara aiki a hukumance daga ranar 14 ga watan Agusta, 2025.

Mamakon ruwan sama ya haddasa ambaliya a Maiduguri  Sojoji sun daƙile hari, sun kashe mayaƙan Boko Haram 9 a Borno

An sanar da wannan naɗin ne a ranar Laraba cikin wata sanarwa da Hukumar CDCFIB, ta fitar, wacce sakatarenta, Abdulmalik Jibrin, ya rattaba wa hannu.

Wannan naɗin na zuwa ne bayan da shugaban hukumar na yanzu, Injiniya Abdulganiyu Jaji Olola, ke shirin ritaya a ranar 13 ga watan Agusta, 2025, bayan cika shekaru 60 a duniya.

Olumode Samuel Adeyemi yana da ƙwarewa da gogewa a aikin kashe gobara.

Ya fara aikinsa a Hukumar Kashe Gobara ta Abuja, kafin daga bisani ya koma Hukumar Kashe Gobara ta Ƙasa, inda ya bi matakai har ya kai matsayin Mataimakin Shugaban Hukumar a sashen kula da ma’aikata.

A tsawon lokacin da ya shafe yana aiki, ya samu horo da ƙwarewar da ake buƙata a cikin gida da kuma waje.

Haka kuma ya riƙe muƙamai daban-daban a hukumar, kuma memba ne a ƙungiyoyi irin su ANAN, Cibiyar Gudanar da Harkokin Kamfanoni ta Ƙasa, Cibiyar Gudanar da Harkokin Jama’a ta Ƙasa, da kuma Cibiyar Kula da Kuɗaɗe ta Ƙasa.

Hukumar ta yaba wa shugaban da zai ritaya, bisa gudunmawar da ya bayar da kuma irin shirye-shiryen da ya jagoranta a lokacin da yake shugabancin hukumar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu ya karɓi baƙuncin Abdulmumin Jibrin Kofa
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • Tinubu ya naɗa sabon shugaban hukumar kashe gobara ta ƙasa
  • Shugabannin Arewa Sun Tattauna Sabon Hanyar Ci Gaba – Minista Uba Maigari Ya Yaba
  • Gwamnatin Kano Ta Kammala Gyaran Makarantu Sama Da 1,200 A Kananan Hukumomi 44
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Na Da Kwamitoci 30 Da Ke Sa Ido Kan Ma’aikatun Gwamnati
  • Gwamna Lawal Ya Naɗa Sabon Sarkin Gusau
  • ‘Yan Sanda A Kano Sun Kama Kasurgumin Dan Fashin Nan Barga Da Wasu Mutum 14
  • Gwamnan Zamfara Ya Naɗa Abdulkadir Ibrahim A Matsayin Sabon Sarkin Katsinan Gusau Na 16
  • ’Yan sa-kai aƙalla 100 da jami’an tsaro 30 sun mutu a bakin aiki a Katsina —Gwamnati