An kama matashi kan zargin kashe matar ɗan uwansa mai juna biyu
Published: 24th, August 2025 GMT
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kwara, ta kama wani matashi mai shekara 29, Sylvester Enemo, bisa zargin kashe matar ɗan uwansa, Misis Esther Enemo, wacce ke ɗauke da juna biyu a Ilorin.
An samu gawar Esther mai shekara 39 a yankin Temidire Zone 4, a bayan gidanta cikin daji, an yayyanka jikinta.
An haramta bukukuwan aure a Taraba NDLEA ta kama matashi da wiwi ta miliyan 10 a KanoAn gano wasu sassan jikinta a cikin wani buhu da aka jefar a ƙarƙashin gada, sai dai har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto ba a ga kanta ba.
Shaidu sun ce an ga Sylvester da safiyar ranar Alhamis ya fita daga gidan da leda baƙa kuma da jini a jikinta.
Maƙwabta, sun ce marigayiya tana gida ita kaɗai a daren kafin a kashe ta, kuma an ga lokacin da ta yi cefane kafin ta koma gida, lamarin da ya nuna kamar tana jiran wani.
Kisan ya tayar da hankalin al’umma, inda ake zargin yana da alaƙa da tsafi.
Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, SP Adetoun Ejire-Adeyemi, ta tabbatar da faruwar lamarin, inda ta ce jami’an CID sun kama wanda ake zargi bayan samun rahoton faruwar lamarin.
Ta kuma bayyana cewa Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar, Ojo Adekimi, ya bayar da umarnin gudanar da bincike tare da tabbatar da adalci.
An kai gawar marigayiyar ɗakin ajiye gawa na Asibitin Koyarwa na Jami’ar Ilorin (UITH), kafin kammala bincike.
Rundunar ta kuma yi kira ga jama’a da su kwantar da hankali tare da guje wa yaɗa jita-jita da ka iya tayar da fitina a jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Ɗan Uwa Kwara zargi
এছাড়াও পড়ুন:
An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
Antoni Janar na Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke birnin Yamai a Nijar, ya bayyana cewa an kama tsohon Ministan Harkokin Waje, Ibrahim Yacoubou, bisa zargin hannunsa a cikin wata aika-aika ta kisan kai domin yin tsafi.
A cewar Maazou Oumarou, lamarin ya samo asali ne daga wani binciken ’yan sanda da aka fara gudanarwa tun a ranar 29 ga Yuli, 2025.
KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan NejaYa bayyana cewa, an soma gudanar da binciken ne dangane da yunƙurin kisa a wani yanki da ke wajen birnin Yamai, lamarin da ya kai ga cafke ababen zargin a garin Dosso.
Wani mutum mai suna Mahamadou Noura ne ya bayyana cewa shi ne ya yi yunƙurin kisan, tare da wasu kashe-kashe guda shida da ya aiwatar a baya, bisa umarnin wasu mutane, ciki har da tsohon ministan Ibrahim Yacoubou.
Mutumin ya shaida wa mahukunta cewa ya aikata hakan ne domin yin tsafi da gawarwakin, a madadin wasu mutane da suka haɗa da: Issa Ali Maiga da Ismael Morou Karama da Elhadji Bilya da kuma Issa Seybou Hama.
TRT ya ruwaito cewa tuni dai an cafke duk ababen zargin, yayin da Kotun Ɗaukaka Ƙarar ta umurci ’yan sanda da su ci gaba da bincike tare da ɗaukar ƙarin matakan da za su tabbatar da gaskiya.
Sanarwar ta ce: “Manufar wannan mataki na shari’a ita ce a tattara cikakken rahoto da ke ƙunshe da dukkan abubuwan da suka faru, sannan a miƙa shi ga ɓangaren gurfanarwa.”
Mai shigar da ƙara a ɓangaren gwamnati ya ce, la’akari da girman wannan lamari, wajibi ne a gudanar da bincike cikin gaggawa.
Haka kuma ya buƙaci al’umma da su mutunta ’yancin kotu tare da bayar da cikakken goyon baya domin fayyace gaskiya.
Ana iya tuna cewa, Ibrahim Yacoubou na daga cikin manyan jami’an da aka kama bayan juyin mulkin Nijar na ranar 26 ga Yuli, 2023, sai dai daga bisani an ba shi beli na wucin gadi a cikin watannin baya.