Budurwa ta gantsara wa saurayinta cizo a mazakuta a Ribas
Published: 17th, May 2025 GMT
Wata mata da age zargin ta cije mazakutar saurayinta ta shiga hannun ’yan sanda.
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Ribas ta kama matar mai shekara 43 ne bayan ta yi wa masoyin nata wannan aika-aika ne a lokacin da suke rikici a cikin gida a unguwar Mile 3 da ke yankin Diobu a garin Fatakwal babban birnin jihar.
Lamarin wanda ya afku a ranar Alhamis, ya girgiza mazauna titin Bishop Okoye mai yawan jama’a lokacin da aka samu labarin lamarin.
A cewar majiyoyi, rikicin ya fara ne lokacin da masoyin matar ya nemi kwanciya da ita.
An bayar da rahoton cewa matar ta ƙi amincewa da buƙatar saurayin nata, inda ta zarge shi da yin amfani da ƙwayoyin masu ƙara kuzarin tsawaita saduwa.
Wani mazaunin garin da ya zanta da wakilin PUNCH da ya nemi a sakaya sunansa ya ce, “Saurayin matar ya fusata ne, saboda masoyiyar tasa ta ƙi amincewa da buƙatarsa.
“Ana cikin haka, ta yi nasarar kama mazaƙutarsa da bakinta kuma ta gantsara masa cizo.”
Rahotanni sun ce kururuwar mutumin ta ja hankalin maƙwabta, inda wasu suka yi yunƙurin riƙe matar kafin ’yan sanda su shiga tsakani.
Majiyar ta ƙara da cewa, “Matar ta cije kan mazaƙutar mutumin gaba ɗaya.”
Jami’an rundunar ’yan sanda reshen Nkpolu ƙarƙashin jagorancin jami’in ’yan sanda na yankin ne suka ceto ta, inda aka tsare su.
An garzaya da wanda aka ciza zuwa wani asibiti da ba a bayyana ba a cikin birnin domin kula da lafiyarsa cikin gaggawa.
Da aka tuntuɓi kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Ribas, Sufeto Grace Iringe-Koko, ta tabbatar da faruwar lamarin a ranar Juma’a.
“Eh, zan iya tabbatar da lamarin, an kama matar (wanda ake zargi) mai shekaru 43, kuma ana ci gaba da bincike,” in ji Iringe-Koko.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Saurayi
এছাড়াও পড়ুন:
Yajin Aikin ASUU: Ba za mu biya duk wanda bai yi aiki ba — Gwamnatin Tarayya
Gwamnatin Tarayya, ta gargaɗi Ƙungiyar Malaman Kami’o’i ta Ƙasa (ASUU), cewa za ta aiwatar da dokar “babu aiki, babu albashi” idan malaman suka ci gaba da yajin aikin da ka iya zai kawo cikas ga harkokin karatu.
A wata sanarwa da ma’aikatar ilimi ta fitar da yammacin ranar Lahadi, Ministan Ilimi, Maruf Tunji Alausa, da Ƙaramar Ministan Ilimi, Suwaiba Sa’id Ahmed, sun ce gwamnati tana da niyyar magance ƙorafe-ƙorafen ASUU ta hanyar tattaunawa cikin lumana.
Mutumin da ya sayar da ɗansa kan N1.5m ya shiga hannu a Ebonyi Egbetokun ya sauke kwamishinan ’yan sandan Abuja“Gwamnati ta nuna gaskiya, haƙuri da kyakkyawar niyya a tattaunawarta da ƙungiyar,” in ji sanarwar.
Ministocin sun bayyana cewa yawancin buƙatun ASUU, kamar ƙarin kuɗin koyarwa da inganta yanayin aiki an riga an biya musu.
Sauran matsalolin kuma suna ƙarƙashin kulawar kwamitocin gudanarwar jami’o’i, waɗanda gwamnati ta sake kafawa don su kula da batutuwan da suka rage.
Sai dai duk da waɗannan matakan, ASUU ta zaɓi shiga yajin aiki.
Ministocin sun ce wannan mataki bai nuna haɗin kai ko adalci ga ɗalibai da jama’a ba.
Sun ƙara da cewa: “Gwamnati ta yi tsayin daka wajen tabbatar da zaman lafiya da daidaita karatu a jami’o’i.
“Amma sun yi gargaɗi cewa, dokar “babu aiki, babu albashi” tana nan daram a tsarin dokokin ƙwadago na Najeriya, kuma gwamnati za ta yi amfani da ita idan aka katse harkokin karatu.
Gwamnati ta roƙi ASUU da ta sake tunani tare da dawowa teburin sulhu, inda ta ce ƙofarta a buɗe ta ke don tattaunawa da yin sulhu.