Wani kwararre a fannin lafiya da ke aiki da asibitin koyarwa na Aminu Kano ya ce bisa kididdigar baya-bayan nan sama da mutane miliyan 11 ne ke dauke da ciwon suga a Najeriya, wasu da dama kuma ba a gano su ba.

 

 

 

Farfesa Zuba Ilyasu, ya bayyana hakan ne a lokacin da yake gabatar da jawabi a taron shekara-shekara na kungiyar likitocin endocrinologists of Nigeria (ACEN) karo na 14, wanda ya gudana a Tahir Guest Palace Kano.

 

 

 

Farfesa Ilyasu ya yi nuni da cewar akwai bukatar wayar da kan jama’a game da salon rayuwa da ake bukatar a yi amfani da su wajen magance matsalar ciwon suga da kuma kiba.

 

 

Shugaban taron, Emeritus Farfesa Musa Borodo, ya yi tir da tsadar hanyoyin samar da kiwon lafiya a kasar nan, inda ya jaddada bukatar da ake da shi na samar da dabarun rage radadin cututtuka kamar kiba da ciwon suga.

 

 

 

Borodo ya lura cewa taron zai gyara hanyoyin da za a fadakar da jama’a kan salon rayuwa da kuma rigakafin cututtuka.

 

 

Shugaban ACEN, Dr. Williams Balogun, ya bayyana bukatar gwamnati da masu ruwa da tsaki su kara saka hannun jari wajen magance matsalolin cututtuka masu yaduwa.

 

 

Ya kuma jaddada kudirin kungiyar na samar da dabarun magance matsalar ciwon suga da kiba.

 

 

 

“Wannan taron zai bayyana ra’ayoyi da bincike iri-iri da nufin tabbatar da cewa an magance wadannan illoli na ciwon suga da kiba sosai.” –

 

Da yake jawabi a lokacin taron Gwamna Abba Kabir wanda kwamishinan lafiya Dr Abubakar Labaran Yusuf ya wakilta ya ce taron ya zo kan lokaci.

 

Ya ce gwamnatin jihar Kano ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen hada kai da kungiyoyin likitoci kamar ACEN da nufin hada kai don magance ciwon suga da kiba kasancewar su cututuka masu kalubale.

 

Abba Kabir Yusuf ya yi kira ga mahalarta taron da su fitar da kudurori da za su magance yawaitar cutar siga da kiba.

 

Taron na da nufin bayyana ra’ayoyi daban-daban da binciken bincike don magance barazanar ciwon sukari da kuma kiba.

 

 

Taron ya ja hankalin mahalarta daga dukkan sassan tarayyar.

 

 

ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Taro

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Jigawa Ta Amince da Sama da Naira Biliyan 2.6 Domin Aikin Hajjin 2026

Daga Usman Muhammad Zaria 

Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da naira biliyan 2.6 domin gudanar da ayyukan Hajjin shekarar 2026.

Kwamishinan Yada Labarai, Matasa, Wasanni da Al’adu na jihar, Alhaji Sagir Musa Ahmed ne ya bayyana hakan jim kadan bayan kammala taron Majalisar Zartarwa ta Jiha da aka gudanar a gidan gwamnati da ke Dutse, babban birnin jihar.

A cewarsa, majalisar ta amince da kashe sama da naira biliyan 2 da miliyan 651 domin ayyukan Hajjin 2026, biyo bayan gabatar da bukatar da Sakataren Gwamnatin Jihar (SSG) ya yi.

Alhaji Sagir Musa Ahmed ya ce za a yi amfani da kudaden ne a bangarorin sufuri da jijigilaAlhazai, jin dadinsu, ayyukan lafiya da kuma shirye-shiryen gudanarwa.

Sauran bangarorin sun hada da duk wasu muhimman abubuwa da za su tabbatar da ingantaccen tsari da nasarar aikin Hajji ga Alhazan jihar Jigawa.

Kwamishinan ya kara da cewa, majalisar ta kuma amince da kashe sama da Naira Biliyan 1 da Miliyan 300 domin tallafin karatu (bursary) ga dalibai 19,716 da aka tantance kwanan nan.

Ya bayyana cewa daga cikin adadin, akwai dalibai maza 12,638,  da mata 7,088 da ke karatu a manyan makarantu 77.

Ya ce wannan tallafi zai taimaka wajen bunkasa harkar ilimi, rage nauyin kudi a kan iyaye da iyalai, tare da karfafa gwiwar dalibai su yi fice a karatunsu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince da Sama da Naira Biliyan 2.6 Domin Aikin Hajjin 2026
  • Shuwagabannin Kasashen Iran Da Iraqi Sun Tattauna A Wajen Taron Zaman Lafiya A Kasar Turkmanistan
  • Pezeshkian: Duniya Tana Bukatar Amintaccen Madogara, Zaman Lafiya Da Kuma Hadin Kai
  • Kamfanonin Sin Sun Kera Tare Da Sayar Da Motoci Sama Da Miliyan 31 Tsakanin Janairu Zuwa Nuwamban Bana
  • Shugabannin Sin Sun Yi Taron Koli Na Tattauna Aikin Raya Tattalin Arziki Don Tsara Abubuwan Da Za A Aiwatar A 2026
  • EFCC ta tsare tsohon ministan ƙwadago, Chris Ngige
  • Borkina Faso Ta Saki Sojojin Sama Na Najeriya 11 Da ta Kama Bayan Jirginsu Yayi Saukar Gaggawa.
  • Najeriya da Saudiyya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar samar da tsaro
  • Rikicin Iyakar Thailand da Cambodia Ya Tilasta wa Dubban Mutane Barin Muhallansu
  • Iran Tana Daukar Bakwancin Taron BRICS Na Binciken Kimiya Da Kuma Ci Gaban Ilmi