Sama Da Mutane Miliyan 11 Ne Ke Fama Da Ciwon Suga A Najeriya – Farfesa Zubairu Ilyasu
Published: 25th, April 2025 GMT
Wani kwararre a fannin lafiya da ke aiki da asibitin koyarwa na Aminu Kano ya ce bisa kididdigar baya-bayan nan sama da mutane miliyan 11 ne ke dauke da ciwon suga a Najeriya, wasu da dama kuma ba a gano su ba.
Farfesa Zuba Ilyasu, ya bayyana hakan ne a lokacin da yake gabatar da jawabi a taron shekara-shekara na kungiyar likitocin endocrinologists of Nigeria (ACEN) karo na 14, wanda ya gudana a Tahir Guest Palace Kano.
Farfesa Ilyasu ya yi nuni da cewar akwai bukatar wayar da kan jama’a game da salon rayuwa da ake bukatar a yi amfani da su wajen magance matsalar ciwon suga da kuma kiba.
Shugaban taron, Emeritus Farfesa Musa Borodo, ya yi tir da tsadar hanyoyin samar da kiwon lafiya a kasar nan, inda ya jaddada bukatar da ake da shi na samar da dabarun rage radadin cututtuka kamar kiba da ciwon suga.
Borodo ya lura cewa taron zai gyara hanyoyin da za a fadakar da jama’a kan salon rayuwa da kuma rigakafin cututtuka.
Shugaban ACEN, Dr. Williams Balogun, ya bayyana bukatar gwamnati da masu ruwa da tsaki su kara saka hannun jari wajen magance matsalolin cututtuka masu yaduwa.
Ya kuma jaddada kudirin kungiyar na samar da dabarun magance matsalar ciwon suga da kiba.
“Wannan taron zai bayyana ra’ayoyi da bincike iri-iri da nufin tabbatar da cewa an magance wadannan illoli na ciwon suga da kiba sosai.” –
Da yake jawabi a lokacin taron Gwamna Abba Kabir wanda kwamishinan lafiya Dr Abubakar Labaran Yusuf ya wakilta ya ce taron ya zo kan lokaci.
Ya ce gwamnatin jihar Kano ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen hada kai da kungiyoyin likitoci kamar ACEN da nufin hada kai don magance ciwon suga da kiba kasancewar su cututuka masu kalubale.
Abba Kabir Yusuf ya yi kira ga mahalarta taron da su fitar da kudurori da za su magance yawaitar cutar siga da kiba.
Taron na da nufin bayyana ra’ayoyi daban-daban da binciken bincike don magance barazanar ciwon sukari da kuma kiba.
Taron ya ja hankalin mahalarta daga dukkan sassan tarayyar.
ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Taro
এছাড়াও পড়ুন:
NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Matakin hana malaman da ba su da rajista hawa mumbari a Neja yana ci gaba da yamutsa hazo a ciki da wajen jihar.
Yayin da wasu suke ganin wannan mataki bai dace ba, wasu kuwa gani suke faduwa ta zo daidai da zama, wato matakin ya zo a daidai lokacin da ake bukata.
NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa DAGA LARABA: Dalilan Da Suka Sa Nayi Yunkurin Kashe Kaina Har Sau UkuShirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kan tanadin Dokar Kasa game da wannan batu.
Domin sauke shirin, latsa nan