Sama Da Mutane Miliyan 11 Ne Ke Fama Da Ciwon Suga A Najeriya – Farfesa Zubairu Ilyasu
Published: 25th, April 2025 GMT
Wani kwararre a fannin lafiya da ke aiki da asibitin koyarwa na Aminu Kano ya ce bisa kididdigar baya-bayan nan sama da mutane miliyan 11 ne ke dauke da ciwon suga a Najeriya, wasu da dama kuma ba a gano su ba.
Farfesa Zuba Ilyasu, ya bayyana hakan ne a lokacin da yake gabatar da jawabi a taron shekara-shekara na kungiyar likitocin endocrinologists of Nigeria (ACEN) karo na 14, wanda ya gudana a Tahir Guest Palace Kano.
Farfesa Ilyasu ya yi nuni da cewar akwai bukatar wayar da kan jama’a game da salon rayuwa da ake bukatar a yi amfani da su wajen magance matsalar ciwon suga da kuma kiba.
Shugaban taron, Emeritus Farfesa Musa Borodo, ya yi tir da tsadar hanyoyin samar da kiwon lafiya a kasar nan, inda ya jaddada bukatar da ake da shi na samar da dabarun rage radadin cututtuka kamar kiba da ciwon suga.
Borodo ya lura cewa taron zai gyara hanyoyin da za a fadakar da jama’a kan salon rayuwa da kuma rigakafin cututtuka.
Shugaban ACEN, Dr. Williams Balogun, ya bayyana bukatar gwamnati da masu ruwa da tsaki su kara saka hannun jari wajen magance matsalolin cututtuka masu yaduwa.
Ya kuma jaddada kudirin kungiyar na samar da dabarun magance matsalar ciwon suga da kiba.
“Wannan taron zai bayyana ra’ayoyi da bincike iri-iri da nufin tabbatar da cewa an magance wadannan illoli na ciwon suga da kiba sosai.” –
Da yake jawabi a lokacin taron Gwamna Abba Kabir wanda kwamishinan lafiya Dr Abubakar Labaran Yusuf ya wakilta ya ce taron ya zo kan lokaci.
Ya ce gwamnatin jihar Kano ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen hada kai da kungiyoyin likitoci kamar ACEN da nufin hada kai don magance ciwon suga da kiba kasancewar su cututuka masu kalubale.
Abba Kabir Yusuf ya yi kira ga mahalarta taron da su fitar da kudurori da za su magance yawaitar cutar siga da kiba.
Taron na da nufin bayyana ra’ayoyi daban-daban da binciken bincike don magance barazanar ciwon sukari da kuma kiba.
Taron ya ja hankalin mahalarta daga dukkan sassan tarayyar.
ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Taro
এছাড়াও পড়ুন:
Taron Abuja kan Tattaunawakan Tattalin Arziki Kasa- “Akwai yiyuwar tattalin arzikin kasa zai murmure a shekarar 2026”
Taron Abuja kan Tattaunawakan Tattalin Arziki Kasa- “Akwai yiyuwar tattalin arzikin kasa zai murmure a shekarar 2026”
Masana a Taron Abuja na Tattaunawa kan Tattalin Arziki Kasa da ake wa lakabi da Abuja Economic Dialogue 2025 da Kamfanin Ignite Capital ke shiryawa duk shekara da haxin gwiwar Kamfanin Innovision Global Consulting sun yi hasashen cewa, za a samu saukar kayan masarufi da Karuwar samar da ayyukan yi a faxin kasa a shekara mai zuwa ta 2026.
Masana tattalin arzikin da suka yi fashin baki kan yadda tattalin arzikin Nijeriya ke tafiya a cikin watanni tara da suka gabata, a taro sun haxa da Dakta Paul Arinze, Shugaban Kamfanin Bincike da Nazari kan harkokin tattalin arziki mai suna Pedestal Africa da Dakta Umar Kwairanga Kwararre kan harkokin tattalin arziki da ayyukan banki da Dakta Sara Alade tsohuwar Mataimakiyar Gwamnan Babban Banki na Kasa kuma Kwararriya a fagen tattalin arziki da kuma Dakta Nuruddeen Zauru wani masanin tattalin arziki.
A cikin sakonsa na fatan alheri tsohon Mataimaki Shugaban Kasa kuma Sardaunan Zazzau, Alhaji Namadi Sambo ya yi tsokaci kan bukatar cewa, lokaci ya yi da gwamnati za ta xauke cigaban da take ikirarin samu a fannin tattalin arziki daga alkalumma a takarda zuwa aiwatarwa a aikace. Ta yadda talakawa za su ga sauKin da ci gaban da aka samu kasa ba labari ba.
Da yake tofa albarkacin bakinsa a taron tsohon Shugaban Majalisar Dattawa ta Qasa, Alhaji Abubakar Bukola Saraki, ya bayyana cewa, ya zuwa yanzu ya dace shugabanni a Nijeriya su san cewa, ba tare da samar da cikakken tsaro da dauwamammiyar wutar lantarki ba tattalin arzikin Nigeriya zai ci gaba da yin kwan gaba-kwan baya.
Saraki ya kuma yi kira da gwamnati da rinka karfafa gwiwar kamfanonin cikin kasa ta hanyar sayen kayayyakin da suke samarwa.
Mai masaukin baki kuma Shugaban Kamfani Ignite Capital, Bukar Abba Kyari ya yaba wa gwamnatin Shugaba Tinubu, kan irin matakan da yake xauka don inganta tattalin arzikin kasa tare da tallafa wa matasa kan harkokin da suka shafi kasuwancin zamani na yanar gizo.