Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka, sharhin bayan labarammu na yau za yi magana dangane da “Rage kisasfin kudan ma’aikatar harkokin wajen Amurla da kimani kasha 50% da kuma tasirinsa ga matsayin Amurka a duniya da kuma cikin gida. Wanda ni tahir amin zan karanta.

A makon da ya gabata ne shugaban kasar Amurka Donal Trump ya bada sanarwan, rahe kasafin kudi na ma’aikatar harkokin wajen kasar da kasha 50%, saboda haka kuma ya rufe wasu daga cikin ofisoshin jakadancin kasar da kananan ofisoshin jakadancin kasar fiye da 30 a yankuna daban daban a duniya amma mafi yawansu a nahiyar Afirka.

Dangane da wannan matakin da gwamnatin kasar Amurka masana daga ciki ga wajen kasar ta Amurka masu yawa sun nuna damuwarsu da kuma rashin amincewarsu da hakan.

A majalisar dokokin kasar, wakilai daga jam’iyyu biyu masu mulkin Amurka wato Republican da kuma Democrat sun nuna rashin amincewarsu da matakan da shugaba Trump ya dauka, suna kuma ganin hakan wata alama ce jada bayan Amurka daga harkokin kasashen duniya, kuma da haka tauraron kasar zata dushe a duniya. Sannan akwai has ashen cewa kasar China zata maye gurbin Amurka a cikin al-amura da dama, musamman a kasashen da Amurka ta janye.

Kafin haka dai shugaban kasar Amurka ya janye kasar Amurka daga manya-manayn kungiyoyin bada agaji a duniya, wadanda suka hada da hukumar lafiya ta duniya WHO, hukumar abinci ta duniya.

Banda haka Amurka ta janye tallafin da take bawa kungiyar tsaro ta NATO wanda yake taimakawa abokan kasar na turai kan abubuwan da suka shafi tsaro, da kuma wasu al-amur da dama.

Masu sukan shugaban daga cikin har da sanatoci da tsoffin janar-janar na sojojin Amurla wadanda suka yi ritaya kimani 120 suke ganin, shugaban trump ya mikawa kasashen China da rasha dukkan wuraren da ya janye tallafi, ko kuma ya rufe ofishin jakadancin Amurka a duniya.

Wadannan masana dai suna ganin, ragewa ma’aikatar harkokin wajen kasar kudede masu yawa wanda ya kai dalar biliyon kimani 25, ya nuna cewa gwamnatin Amurka bata da wakilai a wasu wurare masu mihimmanci da dama a duniya, don haka ba zata sami labarin abinda yake faruwa a cikinsu ba. Kuma mai yuwa samun wadannan labarai suna da muhimmanci.

Wasu masu sukan suna ganin a halin da ake ciki mafi yawan kawayen Amurka, musamman kasashen turai sun tashi daga abokan aiki zuwa ga makiya ga gwamnatin Amurka. Sannan a kasashen masu tasowa, wadanda suke neman tallafi da taimako, Amurka ta bawa kasar China da Rasha dama ta su amfana da wadannan kasashe, ko basu bada kyauta ba, amma suna iya zuba jari a cikin kasashen inda bangarorin biyu zasu amfana.

A wani bangare kuma shugaban yana da shirin rage kudaden da ake kashewa ayyukan gwamnati a cikin gida, inda hakan ya kai ga rufe kafafen yada labarai da daman a gwamnatin Amurka. Hakan ya sa mutane da dama sun rasa ayyukansu a cikin kasar. Sannan daga kasashen waje ba, dubban ma’aikata sun rasa ayyukan daga kungiyoyin bada agaji ko kiwon lafiya ko tallafawa yara karkashin MDD wadanda gwamnatin Trump ta janye tallafin da suke bayarwa.

Daga karshe masana suna ganin, idan wannan halin ya ci gaba da alamun shugaba Donal Trump kama hanyar rusa kasar Amurka daga ciki da kuma wajen kasar a cikin shekaru 4 da zai yi a matsayin shugaban kasa. Mai yuwa gwamnatin da zata zo bayan tasa ta gaggauta gyaran wasu daga cikin abubuwan da ya bata. Amma wasu barnan da yayi ba zasu sake gyaruwa ba.

Don haka daga karshen dai Amurka ta kama hanyar wargajewa, idan ba an yi wani abu da gaggawa ba.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: harkokin wajen kasar Amurka wajen kasar a gwamnatin

এছাড়াও পড়ুন:

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

Babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na Sin CMG, ya gabatar da labarin ganawar da aka yi jiya Alhamis tsakanin shugabannin Sin da Amurka a Busan na Korea ta Kudu, cikin harsuna 85. Kuma zuwa yau Juma’a, mutanen da suka karanta rahotanni masu alaka da ganawar ta hanyoyin watsa labarai na dandalin CMG sun kai miliyan 712. Haka kuma, kafafen watsa labarai na kasa da kasa 1678, sun wallafa tare da tura rahotanni da bidiyon labaran CMG na harsuna daban daban game da ganawar, har sau 4431.

 

Har ila yau a wannan rana, an gudanar taron tattaunawa na kasa da kasa kan bude kofa da kirkire kirkire da ci gaba na bai daya a kasar Uruguay, wanda CMG da hadin gwiwar ofishin jakadancin Sin dake kasar suka shirya a Montevideo babban birnin Uruguay. (Mai fassara: FMM)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa October 31, 2025 Daga Birnin Sin Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace October 31, 2025 Daga Birnin Sin Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Araqchi: Da Hadin Bakin Amurka, Gwamnatin Isra’ila ta kaddamar Da Hari Kan Kasar Iran
  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  • Kasar Qatar Ta Ba Da Tallafin Gaggawa Ga Al’ummar Sudan Bayan Gumurzun El-Fasher
  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini
  • Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
  • CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka
  • Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai