Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Alhassan (a) 112
Published: 21st, April 2025 GMT
Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na kissoshin rayuwa shiri wanda yake kawo maku kissiso da suka zo cikin alkur’ani mai girma ko kuma cikin wasu littafan wadanda suka hada da littafin dastane rastan, ko kum littafin mathnawi na maulana Jalaluddeen rumi.
///… Masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata, a kuma cikin sirar Imam Al-hassan limami na biyu daga cikin limamai masu tsarki daga iyalan gidan manzon All..(s), kuma da na farko ga Fatimah diyar manzon All..(s), sannan jikansa na farko.
A cikin shirimmu da ya gabata mun kawo maku yadda Abuzar a Alghifari babban sahabin manzon All..(s) wanda ya kasance daga cikin mutane na farko da suka musulunta a Makka, sannan ya kuma garinsu giffar yana kiran mutane zuwa ga addinin musulunci har zuwa lokacinda manzon All..(s) yayi hijira, zuwa Madina sai shi ma yayi hijira. Banda haka, manzon All..(s) ya yabeshi a cikin hadisai da dama saboda tsoron All..ta zuhudu da kuma sanin addini.
Amma a lokacinda Uthman bin Affan ya zama khalifa ya kuma dora danginsa Banu Umayya a kan al-ummar musulmi suna azabtar da shi suna kuma kwasar kudaden jama’a suna kashewa kansu, ya fuskanci matsaloli da sahabban manzon All..(s) da dama daga ciki har da Abuzar Alghiffari, wanda ya ci gaba da sukar khalifa da kuma danginsa, har sai da ya kore shi daga madina zuwa Sham da farko, sannan ya sake dawo da shi Madina a cikin mummunan hali, amma Abuzar bai dandara ba, ya ci gaba da sukansu har sai da wata rana, Khalifa yayi tambaya a kan al-amuran addini sai wani bayahude wanda bai dade da musulunct ba, ya bada amsa kuma ba dai dai ba, sai Abuzar ya tashi a kasansa, sai Khalifa kuma ya tashi a kan Abuzar yana masa tsawa, daga karshe ya sake korarsa daga Madina karo na biyu, amma a wannan karon ya kore shi zuwa wani daji inda babu mutane, kuma yace zai zauna a wurin har sai ya mutunu.
Munji yadda ya umurci Marwan dan hakam, ya bashi guzuri ya koma can inda ba zai ga wani ba, kuma ba wanda zai ganshi. Sai Marwan ya ajiye shi a wani wuri kafin ya kammala hada masa guzuri, sannan khalifa ya fadawa Marwan ya fitar da shi cikin kaskanci daga Madina sannan kada ya bar wani ya yi magana da shi ko y ace za iyi bankwana da shi.
Sai mutanen madina da dama, a lokacinda suka ji abinda ya faru da Abuzar sun sabawa Khalifa Uthman sun zo suna bankwana da Abuzar suna kuma Magana da shi suna bashi hakuri, suna masa naisiha kan ya yi hakari da abinda ya sameshi.
Daga cikin wadanda suka sabawa Khalifan Uthman, akwai Amirul Muminina Aliyu dan Abu talib (a). Ya fito tare da yayansa Alhassan da Alhussan (a) da Akilu dan Abitalib, da Abdullahi dan Jaafar, sun nufi Abuzar a inda suka ajiye shi.
A lokacinda Marwan dan ya ga haka, sai ya yi yaje wajen Imam Hassan (a) yana cewa: Ya kai Alhassan baka san cewa khalifa yah ana a yi Magana da wannan mutum ba? Idan baka sani ba to ka sani!.
Sai Imam Ali (a) ya shi da dokinsa ya kuma bugi kunnen dokinsa da bulala da ke hannunsa, ya na cewa: Kauce ! All..ya kaudakai zuwa wuta, sai Marwan ya ji tsoro, sannan ya yi sauri ya je ya fadawa Uthman abinda ya faru.
Sai Imam Ali (a) ya sauka ya zo kusa da Abuzar ya kuma ya masa bankwana, ya kuma yi masa Jababi wanda ya zabe masa salwa, (tsuntsun da All..ya saukarwa banu Isra’ila a lokacinda suke dimwa a yankin Sina). Kalmomi wadanda suka kasance hakan a tsawon zamansa a Rabazah.
Ya na cewa:
Ya Abazar lalle kai ka yi fushi don All.., ka yi kaunar samun lada daga wanda kayi fushi dauminsa, Lalle mutanen nan sun ji tsoranka, saboda duniyarsu, kai kuma ka ji tsoronsu saboda addininka, ka barsu da abinda suka ji tsoronka sabo da shi, ka gudu da abinda ka ji tsoronsu saboda shi, ai su suka fi bukatar abinda ka hanasu, sannan ka wadatu daga abinda suka hanaka, da sannu zaka sani waye mai riba a gobe kiyama. Kuma wanda yafi yawan hasada.
Da ace sammai da kassai sun fada a kan a kan bawa, sannan ya ji tsoron All…da lalle sai All..ya yi masa mafita daga garesu! Lalle kada wani abu ya shagaltaka sai gaskiya. Kuma kada kayi kewan bata, da ka karbi duniyarsu da sai sun so ka, da kayi aron wani abu daga cikinta da sun amintar da kai. (khuduba 129 cikin Nahjul Balagha).
Tare da wadannan kalmomi masu muhimmanci Imam Ali(a), ya dauki iyakance matsayin Abuzar da halin da ya fada ciki, da kuma abinda ya sa sarakunan Banu umayya suka ki shi. Yau tashi a kansu ne don ya tsira da addininsa, su kuma sun tashi a kansa ne don suna jin zai bata masu duniyarsu. Don tashi a kansu ne don ya farkar da mutane hatsarin wadannan shuwagabannin ga akidun musulunci musamman kan abinda zai zo nan gaba.
Daga nan sai Imam Alhassan (a) ya yi sauri yak ama hannun Abuzar ya yi musafaha da shi, ya kuma yi masa bankwana, ya kuma yi masa Magana wadanda zasu kwantar da hankalinsa. Yana cewa:
Ya ammina ! Ba don yakamata ga wanda akewa bankwana ya yi shiru, sannan wanda yake bankwana ya juya ya dawo ba, da zance yayi kadan, ko da kuwa bakinciki mai tsawo ne. Wadanan mutane, sun dora maka, abinda muke gani, ka yi bankwana da duniya tare da tunanin rabuwa da ita watarana, Ka kuma manta da tsananin da ya tsananta a cikinta da fatan abinda ke bayanta., ka yi hakuri har sai ka hadu da annabinka (s) ya na mai yarda da kai.
Don haka Imam Hassan (a) ya yi masa wasiyya da hakuri kan abinda ya sameshi har zuwa haduwarsa da ubangiji, da kuma manzon All..(a).
Sai Abuzar alghiffari yad aga kansa ya kalli iyalan gidan manzon All..(s) yana mai matukar bakin cika da rabuwa da su, sannan ya bude bakinsa yana cewa:
All,,yayi maku rahama , ya ku iyalan gidan rahama, kuna tunatar da ni manzon All..(s) a duk lokacinda na kalleku, bani da wani masu zama a Madina wadanda ne shaukinsu banda ku. Lalle na yi nauyi ga Uthman a Hijazi kamar yadda na yi nauyi da Mu’awiya a Sham, banda haka Uthman ya ki in kasance tare da dan’uwansa da kuma dan yar uwansa, a birane guda biyu (kufa da Basra) don kada in bata masu al-amarinsu a cikin mutanen wadan nan birane.
Don haka ne suka koreni zuwa wurinda bani da mataimaki, da kuma mai kare ni sai All… Na rantse da All..bana bukatar wanda zai kasance tare da ni sai All.., sannan bana jin kewar wani abu matukar ina tare da All….).
Daga nan sai aka kori Abuzar daga madinan manzon All..(s), aka nisantar da shi daga iyalan gidan manzon All…, aka nisantar da Abuzar daga Madina duk tare da cewa manzon All..(s) ya fadi matsayinsa a cikin sahabbansa, daga cikin yace wanda yake son ganin annabi Isa a cikin zuhudunsa da Rashin yawan maganarsa da kuma shiriyasa. Manzon All..(s) ya yabe shi da fadin gaskiyarsa.
Uthman ya koreshi daga madina manzon All….(s) don yaje ya mutu a can, shi kadai. Shi kuma shi kuma da danginsa su ci gaba da cin duniyar al-umma. Suna yin abinda suka ga dama.
Imam Aliyu (a) da yayansa suna komawa gida sai ga wata Jama’a tazo daga wajen Khalifa sun fada masa cewa, khalifa Uthman yayi fushi da shi, kuma yana kiransa kan ya sabawa umurninsa na hana mutane yin bankwana da Abuzar Alghiffari makiyinsa.
Sai Imam(a) yace masu : Fushin dawaki ga linzami kenan. Yana nufin don dawaki na fushi da lanzami sai a bar Sanya masu linzami ne?
Sai Imam (a) ya je wajen Khalifa ya shiga wajensa., sai Khalifa yayi sauri ya fara fada masa, kan cewa: Me yasa ka maida dan aike na?
Sai Imam Yace: Amma Marwan ya zo mani yana son ya maidani sai na maida shi daga hanani zuwa wajen Abuzar, amma umurninka bai saba masa ba.
Sai Uthman ya ce: Shin umurnina bai kai gareka ba, kan cewa na hana mutane su yi bankwana da Abuzar ba?
Sai Imam (a) yace: shin duk wani umurnin da ka bayar, sannan ana ganin sabon All..a ciki, a yi biyya ga umurninka?
Sai Uthman yace: Ka daki Marwan, sai Imam Yace: Ban dake shi ba, sai dai na daki kunnen abin hawansa ne, sannan ga abin hawa na, idan ya na son ya rama kamar yadda na daki tasa ya yi hakan. Amma dangane da ni, na rantse da All.. idan ka zageni, sai na zageka da zagi irinsa. Ba zan yi kariya cikinsa ba kuma ba zan fada bas ai gaskiya.
Sai Uthman yace: Me yasa Marwan ba zai zageka bai dan ka zage shi? Kuma na rantse da All.. a wajene ba abinda ka fishi da shi.
Sai Imam (a) yayi Fushi, da uthman saboda ya daidai da Marwan, (alhali ya sani) manzon All..(s) ya fada dangane da shi, :Matsayinka da ni kamar matsayin Haruna da Musa ne, a yayinda yake fada dangane da Marwan Hakam: Tsaka dan tsaka, kuma wanda manzon All..(s) ya la’aneshi tun yana cikin tsotson mahaifinsa; Sai Imam (a) yace: Ni kake fadawa wannan zancen? Kana daidaita ne da Marwan? Na rantse da All..ya fika, kuma babana ya fika, babanka, kuma mahaifiyata ta fi mahaifiyarka, kuma ga wannan kori ne ya zare su.
Sau Uthman yayi shiri, sanna Imam (a) ya juya ya tafi ya na fushi da Uthman, saboda dai-datashi da Marwan Dan hakam, bai bashi matsayin da All..da manzonsa (s) suka bashi ba. Bai bashi hatta matsayin da sahabanna manzon All..(s) suke bashi ba. Kuma idan ba don Aliyu (a) baya khainci ba, da yah ana Uthman zama Khalifa a lokacinda Abdurraman dan Auf ya bijiro basa Khalifanci tare da shardanta masa da bin Abubakar da Umar. Amma yaki amincewa, a sannan ne ya bijirowa Uthman ya yarda da dukkan sharuddan da suke cikinta, ya kuma saba masu gaba daya. Bai bi littafin All..ba bai bi sunnan manzon All..ba, bai kuma bi hatta sunnar Abubakar da Umar ba.
Masu sauraro a nan zamu dasa aya sai kuma wata fitowa idan All..ya kaimu wassalamu alaikum wa rahamatullahi wa barakatuhu.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: na rantse da All masu sauraro iyalan gidan bankwana da
এছাড়াও পড়ুন:
2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
An ture Mataimakin Gwamna Gefe, Tsarin karba-karba Na Goyon Bayan Kwara ta Arewa.
Gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazak, zai kammala wa’adinsa na biyu a shekarar 2027, amma babu wata alamar cewa mataimakinsa, Mista Kayode Alabi, zai gaje shi.
Yanayin siyasa a jihar na nuna cewa yankin Sanatocin Kwara Arewa ne ake sa ran zai samar da gwamna na gaba; Alabi yana daga Kwara Kudu.
Kwara ta Arewa ba ta samar da gwamna da tun daga 1999, yayin da Kwara Kudu ta rike kujerar siyasa ta farko a jihar na tsawon shekaru takwas, kuma zuwa 2027 Kwara Tsakiya za ta kasance ta rike kujerar na shekaru 20.
Masu nazarin siyasa guda biyu, Comrade Abdul-Rahoof Bello-Labelabe da Comrade AbdulLateef Ishowo, sun bayar da dalilan da suka sa mataimaka ke samun wahalar gadon shugabanninsu.
Kwamared Abdul-Rahoof Bello-Labelabe ya ce, “Mataimakan gwamnoni ana kallonsu ne a matsayin wasu mutane da ke shiga zabe a kan tikitin jam’iyya daya tare da gwamnonin da suke aiki tare.
Amma a mafi yawan lokuta, ba su ne zabin gwamnonin ba, sai jam’iyya ta tilasta wa gwamnonin domin cika sharudan zabe.”
“Tun da kundin tsarin mulki bai bai wa mataimaka wasu ayyuka na musamman ba, galibi gwamnonin suna kallon su a matsayin safaya taya kawai.
“Wannan rashin aikin hukuma ko warewa da ake yi wa mataimaka na haifar da rashin jin dadi, hassada da rashin amana, sannan kuma yana haifar da fushi da dangantaka mara kyau da shugabansu.
“Saboda haka, gwamnonin na tafiyar da mulkinsu ne, suna barin mataimakansu a duhu. Don haka, a karshen wa’adin gwamnonin, tsoron ramuwar gayya ko adalci mai daukar fansa zai fara yawo a zukatansu, kuma za su nemi wani mutum mafi aminci domin ya gaje su, domin samun kwanciyar hankali da zaman lafiya bayan sauka daga mulki.”
A nasa bangaren, Kwamared AbdulLateef Ishowo ya ce, “Abin ya danganta da irin rawar da ake takawa. Yayin da wasu mataimaka ke da matsananciyar halayya kuma suna da buri fiye da kima, wasu shugabanni kuma suna da mulkin kai ba tare da bukata ba.
“Dauki tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar da tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo, misali; yayin da na karshe ya bar fagen siyasa ga na farko cikin kyautatawa, Atiku ya yi amfani da damar wajen kokarin kwace matsayi daga shugabansa. Wannan dai yanayi ne na musayar bangarori biyu.”
BORNO: Karfin Iko Ya Hana Kadafur Cimma Burinsa
Kididdigar siyasa da ta kasance al’ada a siyasar Jihar Borno tun fara dimokuradiyya a 1999 za ta zama babban cikas ga mataimakin gwamna na yanzu, Alhaji Usman Kadafur, wajen gaje Gwamna Babagana Umara Zulum a karshen wa’adinsa a zaben shekara mai zuwa.
Yayin da yake magana da wakilinmu a Maiduguri, wani masani kan siyasa kuma dan asalin Kudu Borno, Adamu Ali, ya ce abu ne mai wuya Kadafur ya gaji Zulum, inda ya lura cewa a farko, Kadafur ba shi ne mafi karbuwa ba ko ma a Karamar Hukumarsa ta Biu a Kudu Borno.
Ali, wanda ya bayyana cewa Kadafur bai yi tasiri ga mutanen yankinsa ba, ya kara da cewa babu wata yarjejeniya ta hukuma da ke nuna cewa iko ya kamata a mika wa Borno ta Kudu, yankin da mataimakin gwamnan ya fito.
Ya ce, a gaskiya, lokaci guda tilo da aka sami dan fatan mika iko zuwa Borno ta Kudu shi ne a lokacin mulkin tsohon Gwamna Ali Modu Sheriff. A yankin Uba na Borno Kudu, Sheriff ya yi wata sanarwa cewa, bayan shi, iko ya kamata ya koma Borno ta Kudu saboda abokinsa, marigayi Zubairu Maina. Sai dai, da zarar Zubairu Maina ya rasu, duk wannan tsari ya tsaya cak.
Masanin siyasar ya ce, “Idan ka duba tsarin, kafin wani ya fito a matsayin gwamna, akwai wani tsari, kuma wannan tsari yawanci yana tafiya ne ta hanyar zaben farko. Ana gudanar da zaben farko ne ta hannun wakilai, kuma mafi yawan wakilan sun fito ne daga kabilar Kanuri wadda ke sarrafa Arewa da Borno ta Tsakiya.”
“Yankin Borno ta Kudu na da kananan hukumomi tara kawai, kuma duk da irin kokarin da suka yi, ko da dukkan kananan hukumomin sun hadu, za su samar ne da kashi daya cikin uku na wakilai ne kawai. Saboda haka, saboda wannan dalili, zai yi wuya ga mataimakin gwamna na yanzu, Kadafur, ya gaji ubangidansa, Gwamna Zulum, balle a ce iko ya koma Borno ta Kudu sai dai idan wani abu mai ban mamaki ya faru.”
LEADERSHIP Weekend ta ruwaito cewa tun fara dimokuradiyya, kabilar Kanuri a Arewa da Borno ta Tsakiya ce ke samar da gwamna, yayin da mukamin mataimakin gwamna ake bai wa mutanen Borno ta Kudu.
Bisa dalilin da ya sa mataimakan gwamna ba sa yawan gaje gwamnoninsu, wani babban dan siyasa a Borno, Alhaji Ahmed Ashemi, ya ce gwamnonin ba sa son mutanen da suka yi aiki tare da su su hau mukamin gwamna su kuma zama masu karfi kamar yadda suka kasance lokacin da suka zama gwamna.
Ashemi ya ce, “Bayan shekaru takwas ko hudu, gwamnonin ba sa son mataimakansu su zama gwamnonin kuma su zama masu mulki a birnin.”
“Ta yaya wanda nake ba wa umarni kuma yake bin bayana zai zama gwamna kwatsam? Daga baya kuma na koma gefe na zama dan kallo.”
“A wasu wurare, saboda wata kabila ce ke rike da kujerar gwamna tsawon lokaci, masu rike da iko ba za su so a mika kujerar zuwa wata karamar kabila ta hannun mataimakin gwamna ba — sai dai idan wani lamari kamar mutuwa ya sauya tsarin.”
GOMBE: Siyasar Addini Ta Hana Mataimaki Cimma Burinsa
Yayin da Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya na Jihar Gombe ke shirin fita daga ofis a 2027, yanayin siyasar jihar ya fara dumi. Tambayar da ke mamaye al’amuran siyasa ita ce: “Wa zai fito a matsayin gwamna na gaba?”
Mataimakin Gwamna, Dr Manassah Daniel Jatau, dan kirista daga Kudu na Karamar Hukumar Balanga, zai iya kasancewa cikin wannan tattaunawa da damar gaje shugabansa, amma tun dawowar dimokuradiyya a 1999, siyasar Gombe tana bin wani tsarin da ake iya hasashe wanda aka tsara ne bisa la’akari da yankuna da addini.
Dukkan gwamnonin da aka zaba tun daga Abubakar Habu Hashidu zuwa Danjuma Goje, Ibrahim Hassan Dankwambo, har zuwa Inuwa Yahaya na yanzu duk sun fito ne daga arewacin jihar da Musulmi suka fi rinjaye, yayin da mataimakansu suke fitowa daga kudu inda Kiristoci suka fi yawa.
Ga masana kamar Dr Musa Tukur, malamin kimiyyar siyasa a Jami’ar Gombe, wannan tsarin hada yankuna biyu ya taimaka wajen inganta hadin kai, amma kuma ya haifar da katangar gado. Babu wani mataimakin gwamna a tarihin dimokuradiyyar Gombe da ya taba gadon shugabansa.
Wannan yana nuna cewa yawancin masu zabe a yankunan da Musulmi suka fi rinjaye suna yawan zabar ‘yan takarar Musulmi, yayin da yankunan Kiristoci ke fifita Kiristoci. Wannan ne dalilin da ya sa tun daga 1999, kujerar gwamna ta kasance a hannun bangaren arewa mai rinjayen Musulmi.
Saboda haka, masu lura da al’amura na ganin cewa takarar shekara ta 2027 ba za ta karya wannan tsari ba, wanda hakan ke nuna cewa hanyar Jatau zuwa mulki za ta kasance mai wahala. A cewar mai sharhi kan harkokin siyasa, Ibrahim Alkali, “Gombe ba ta kai matsayin da za ta ba da dama ga dan kudu Kirista ya zama gwamna ba, musamman duba da yanayin cikin gida na jam’iyyar APC.”
Yayin da wasu maganganu a kafafen sada zumunta ke nuna cewa ana hasashen wanda Gwamna Yahaya zai fi so ya gaje shi, da sunaye kamar Injiniya Aliyu Muhammad Kombat da Arc. Yakubu Yunusa na kamfanin Lubell Nig Ltd., mai sharhi Abdulrahman Musa ya bayyana cewa salon Yahaya ya yi kama da na shugabannin da ke kallon batun gadon mulki a matsayin hanyar kare gadonsu, ba wai neman zama uba a siyasa ba.
Duk da cewa Jatau mataimaki ne mai biyayya kuma gogaggen ma’aikaci a fanninsa, wasu daga cikinsu na ganin ba ya cikin manyan ‘yan takarar da ake tattaunawa a kansu don su gaji kujerar mulki. Sai dai wasu na ganin cewa tsayawar Jatau takara na iya zama gwaji ga matakin wayewar siyasar jihar.
Jihar Imo: Mataimakin Gwamana Bai Da Kahon Karon Yin Takara
Yanayin siyasa a Jihar Imo bai nuna cewa mataimakiyar gwamna, Hajiya Chinyere Ekomaru, za a ba ta dama ta gaji gwamnatin Gwamna Hope Uzodimma ba.
Dalilin hakan ba ya da nisa, domin mataimakiyar gwamnan tana kama da sabuwa a harkar siyasa, tana da karancin kwarewa, tsarin siyasa da kwarewar da ake bukata don tafiyar da jihar mai rikitarwa kamar Imo.
Wannan kuma yana da alaka da asalin aikinta, kasancewarta ma’aikaciyar gwamnati mafi yawan lokacinta, ba tare da samun gogewar siyasa sosai ba.
Idan aka kalli halayyarta da kyau, ana iya fahimtar cewa watakila kawai an jawo ta cikin siyasa ne don cike gurbi, ba tare da niyyar ta gaji shugabanta ba.
Wani mai sharhi kan siyasa, Dr Harold Onumo, ya shaida wa LEADERSHIP Weekend cewa yawancin gwamnonin ba sa son barin mataimakansu su gaje su saboda son kai, tsoron abin da ba a sani ba, da kuma karancin kwarin gwiwa.
Ya bayyana cewa wasu gwamnonin na jin tsoron cewa idan suka ba da dama irin wannan, mataimakansu za su iya zama masu kudi da tasiri fiye da su.
A cewarsa, gwamnonin yawanci suna son su ci gaba da zama masu sarrafa al’amura, kuma su kasance ana kallonsu a matsayin “uba” a siyasa.
“Suna son su ci gaba da zama shugabanni kuma su rike tsarin siyasa gaba daya. Sun fi son yanayi inda su kadai suke da iko a fagen siyasa,” in ji shi.
Ga Dr Chinyere Ekomaru, mataimakiyar gwamnan Jihar Imo ta yanzu, batun gadon mulki na iya zama babban kalubale, musamman ganin yadda manyan ‘yan siyasa ke kara neman kujerar Douglas House.
Tun bayan dawowar dimokuradiyya a 1999, babu wani gwamna a Jihar Imo da ya taba nasarar saka mataimakinsa ya gaje shi a kujerar mulki.
Yayin da Cif Achike Udenwa ya fi son Cif Iyke Ibeh, manyan ‘yan siyasa sun hadu ne suna goyon bayan Dr Ikedi Ohakim.
Lokacin da Ohakim ya nemi wa’adi na biyu, tsohon Shugaban Kasa Goodluck Jonathan ya ba da goyon baya ga Owelle Rochas Okorocha maimakon sa.
A lokacin da Okorocha ya yi kokarin saka wanda yake so surukinsa, Cif Uche Nwosu manyan kungiyoyin siyasa suka ki, lamarin da ya haifar da fitowar Emeka Ihedioha, wanda daga baya aka maye gurbinsa da Uzodimma.
A halin yanzu, rikici na tasowa tsakanin yankin majalisar dattawan Owerri da Okigwe kan wanda ya kamata ya gaji Uzodimma.
Yankin Owerri na jaddada cewa tun daga 1999 sun rike kujerar gwamna na kusan watanni takwas ne kawai a karkashin Cif Emeka Ihedioha.
A gefe guda kuma, yankin Okigwe na cewa dole ne a kammala wa’adinsu da aka katse lokacin mulkin Dr Ikedi Ohakim kafin yankin Owerri ya sake samun damar rike kujerar.
Masana harkokin siyasa na jaddada cewa Dr Chinyere Ekomaru, a matsayinta na mace, ba ta da karfin siyasa ko tasiri da zai ba ta damar ta gaji Uzodimma, domin har yanzu ba ta taka muhimmiyar rawa a kowace babbar matsalar siyasa a cikin jihar ba.
Sir Sunny Ndukwu, wani jigo a jam’iyyar PDP daga Ngor Okpala, ya ce babu wata dama da Ekomaru za ta samu.
A cewarsa, burin yankin Owerri a yanzu shi ne kujerar gwamna gaba daya, ba na mataimaki ba kamar a da.
Ya bayyana cewa, da marigayi Cif Emmanuel Iwuanyanwu, tsohon Shugaban Ohanaeze Ndigbo na Duniya, yana raye, da Ekomaru na iya samun dama. Amma da rasuwarsa, damar siyasarta ta ragu kwarai.
“A da, tsawon shekaru fiye da ashirin, ana tattauna makomar siyasar yankin Owerri a fadar marigayi Cif Emmanuel Iwuanyanwu. Mataimakiyar gwamnan Jihar Imo a yanzu, samfur ce daga gidan siyasar Iwuanyanwu.
“Zan iya fada maka, da yana raye, da Ekomaru tana cikin manyan ‘yan takarar kujerar gwamna. Amma yanzu Iwuanyanwu ya rasu, kuma wannan damar siyasa da take da ita a baya ta shude, sai dai in da gaske tana da niyyar tsayawa takarar 2027.”
Ya kara da cewa: “Magana ta gaskiya, bana tunanin Gwamna Uzodimma zai zabi Ekomaru a matsayin wacce zai goyi baya don ta gaje shi. Zaben gwamnan Imo zai kasance mai zafi sosai, kuma ba na tunanin gwamnan zai zabi wanda ba shi da ingantaccen tsari na siyasa a ko’ina cikin jihar.
“Kodayake Uzodimma gwamna ne mai ci, duk wanda zai zaba a matsayin magajinsa dole ne ya kasance mutum mai karfi a siyasa, domin sakamakon zaben gwamna na 2023 na iya bambanta kwarai da abin da za mu gani a 2027,” in ji Ndukwu.
Ko da yake Uzodimma bai bayyana wanda yake so ya gaje shi ba tukuna, masu lura da harkokin siyasa na ganin cewa hakan zai kasance aiki mai wahala, amma zai iya yiwuwa idan aka yi la’akari da dangantakarsa mai karfi a jam’iyyar APC.
Bauchi: Ministoci da Magoya baya na Neman Gaje Bala Mohammed
Takarar neman zama gwamnan Bauchi a shekarar 2027 ta fara a hankali tun kafin fitowar tallace-tallace da gangamin siyasa. A bayan fage, ana kafa kungiyoyi, ana gudanar da tarurruka a Abuja da Bauchi, kuma ana tsaurara niyyar takara.
Gwamna Bala Mohammed na jam’iyyar PDP yana wa’adinsa na karshe, kuma fafutukar neman wanda zai gaje shi tana jan hankalin fitattun manyan ’yan siyasa a tarihin jihar.
Abin da ya bambanta wannan takara shi ne irin mutanen da ke son tsayawa: ministocin tarayya, sanata, kwamishinoni, kwararru, da manyan masu tsara dabarun siyasa duk suna hangen zama gwamna.
Wannan ba zabe kadai ba ne, har ma rikici ne na tasiri, gadon mulki, da kuma tasirin kungiyoyin siyasa na yankuna daban-daban.
Ko da yake jam’iyyar ADC karamar jam’iyya ce, tana da fitattun ‘yan takara biyu: tsohon Shugaban Hafsan Sojojin Sama kuma dan takarar APC a zaben 2023, Ambasada Sadikue Abubakar, wanda ya dawo takara da kwarewar soja, gogewar diflomasiyya, da kuma gagarumin goyon baya.
Baya ga shi, akwai Sanata Halliru Dauda Jika, dan siyasa mai karfi a kasa wanda ke da zurfin tasiri a siyasar Bauchi. Sai dai kalubalen su shi ne yadda za su iya farfado da karfin jam’iyyarsu wacce ba ta da tsari mai karfi kamar manyan jam’iyyu.
Jam’iyyar All Progressibes Congress (APC) ita ce ake ganin tana da jerin fitattun ‘yan takara mafi karfi.
Sanata Shehu Buba Umar na zuwa da kwarewar majalisa, goyon bayan talakawa, da kuma tsari mai karfi.
Bala Wunti kuwa, shahararre ne a fannin man fetur da iskar gas. Ko da yake wannan shi ne karo na farko da zai shiga siyasa kai tsaye, Wunti yana samun karbuwa sosai a Bauchi.
Ministoci biyu da ke kan mulki sun kara zafafa takarar sosai: Ministan Lafiya da Walwalar Jama’a, Farfesa Muhammad Ali Pate, kwararren masani ne da duniya ke girmamawa, yayin da takwaransa na Harkokin Waje, Jakada Yusuf Tuggar, ke da karfafan dangantaka a duniya.
A bangaren APC, tambayar ba wai wanene yake son tikitin takara ba bace, har ma wa jam’iyyar za ta iya haduwa a bayansa.?
Jam’iyya mai mulki, PDP, kuwa tana fuskantar rikicin tsarin wanda zai gaje ta.
Dr Yakubu Adamu, Kwamishinan Kudi kuma daya daga cikin amintattun abokan Gwamna, sabon shigowa ne daga fannin banki amma baya da zurfin tushe a siyasa.
Farouk Mustapha, Kwamishinan Harkokin Musamman da Cigaban Karkara, yana zuwa da kuzarin talakawa da karbuwa daga bangarori daban-daban na siyasa.
Ya taba yin takarar gwamna a karkashin jam’iyyar APC kafin ya koma PDP a gabanin zaben 2023, kuma ya kasance Darakta Janar na yakin neman zaben Gwamna Bala Mohammed.
Usman Adamu Shi Ma Dan Takara Ne Mai Biyayya Ga Gwamnati
Duk da haka, yiwuwar shigar Sanata Abdul Ningi, babban dan siyasa mai karfin tasiri a fadin jihar na iya canza daidaiton siyasa da kuma kalubalantar ikon gwamna.
Tare da ministoci, kwamishinoni, kwararru, gogaggun ‘yan siyasa da kuma rikicin biyayya ga jam’iyya da burin kashin kai, zaben 2027 na neman zama mafi rikitarwa a tarihin siyasar Bauchi cikin shekaru da dama.
Lissafin ya riga ya fara a hankali, cikin dabara, kuma cikin tsanani.
Nasarawa: Gwamna na juyawa, mataimakin gwamna na neman kujerar majalisar dattawa
A Jihar Nasarawa, mataimakin gwamna mai ci, Dakta Emmanuel Akabe, an ruwaito cewa yana neman kujerar majalisar dattawa ta yankin kudu, alamar cewa tsarin juyawar mulki da ake bi a jihar bai dace da yankinsa ba.
Wakilinmu ya ruwaito cewa tsarin da aka kafa tun daga 1999 yana bai wa yankuna damar karbar mulki ta juyawa bayan kammala wa’adin shekaru biyu daga wani yanki.
Ana sa ran cewa a 2027, mulki zai koma Nasarawa ta Yamma (yankin Keffi).
An riga an fara ganin manyan tallolin siyasa (billboards) da ke dauke da sakonnin burin Dakta Akabe na neman kujerar majalisar dattawa a Lafia, babban birnin jihar, da sauran sassan yankin mazabar Nasarawa ta Kudu.
Wanda ke rike da kujerar a halin yanzu, Sanata Mohammed Onawo, ana hasashen yana da wasu manyan burin siyasa.
Mataimakin Gwamna Akabe, kamar yadda LEADERSHIP Weekend ta gano, yana da kyakkyawar alaka da babban ubangidansa, Gwamna Abdullahi Sule, kuma har yanzu an ba shi cikakken ‘yanci wajen gudanar da aikinsa.
Oyo: Mataimakin gwamnan ya kame bakinsa a yayin da tsarin rabon mulki ke haifar da matsin lamba daga waje
A Jihar Oyo, mataimakin gwamna, Barista Bayo Lawal, bai nuna wata sha’awa ta tsayawa takarar gwamna a 2027 ba.
Haka kuma babu wata matsala da aka sani tsakaninsa da gwamnan jihar, Seyi Makinde.
Ko da yake akwai kiraye-kirayen da ke neman a bai wa yankin Oke-Ogun inda mataimakin gwamna ya fito damar zama gwamna na gaba, Lawal bai bayyana wani niyyar tsayawa takara ba a fili.
Sai dai wasu ‘yan takara daga jam’iyyun siyasa daban-daban sun fara nuna sha’awar shiga gasar zaben gwamna.
Legas: Masu Tasiri A Siyasa Na Hangen Wasu Ba Mataimakin Gwamna Ba
A Jihar Legas, ana ganin cewa Gwamna Babajide Sanwo-Olu ba shi da karfi sosai wajen yin tasiri a zaben wanda zai gaje shi.
Mataimakinsa, Dr Obafemi Hamzat, a cewar rahotanni, ba ya cikin jerin mutanen da ake kallon su a matsayin masu yuwuwar zama magadansa a shekarar 2027, lokacin da su biyun za su kammala wa’adin su na biyu tare.
A baya, Hamzat ya taba zama Kwamishinan Kimiyya da Fasaha a lokacin da Shugaba Bola Tinubu yake gwamna na Jihar Legas. Ya ci gaba da rike wannan mukamin a karkashin Gwamna Babatunde Fashola da ya hau karagar mulki a shekarar 2007.
Majiyoyi daga cikin manyan masu tasiri a siyasar Legas sun nuna cewa zai yi wuya a ba Hamzat mulki saboda gogewarsa da ‘yancin kansa. Wata daga cikin majiyoyin ta ce, “Zai yi wahala a sarrafa mutum mai irin wannan kwarewa da gogewa.”
Tun bayan saukarsa daga mulki a shekarar 2007, Shugaba Tinubu ne ya kasance ginshikin da ke yanke shawara kan wanda zai zama gwamna a Legas.
Ogun: Mataimakin Gwamna Ba Ya Cikin ‘Yan Takara, Manayn ‘Yan Siyasa Sun Fara Gangami
Haka nan a Jihar Ogun, Gwamna Dapo Abiodun na iya kin amincewa da fitowar mataimakiyarsa, Noimot Salako-Oyedele, a matsayin wacce za ta gaje shi.
Ana samun rahotannin cewa Sanata Solomon Adeola, shugaban kwamitin Majalisar Dattawa kan Kasafin Kudi, da tsohon Jakadan Nijeriya a Birtaniya, sun fara nuna sha’awar takarar kujerar gwamna domin gadar Abiodun.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA