Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-11-02@19:37:52 GMT

Fafaroma Francis ya Rasu

Published: 21st, April 2025 GMT

Fafaroma Francis ya Rasu

Fadar Vatican ta sanar da mutuwar shugaban majami’ar katolika na duniya, Fafaroma Francis yana da shekaru 88 a duniya.

A shekarar 2023 ne cocin ya zaɓi Fafaroman, wanda asalin sunansa shi ne Cardinal Jorge Mario Bergoglio a matsayin wanda zai jagorance ta, bayan saukar Fafaroma Benedict XVI daga kan muƙamin.

Da safiyar Litinin ne ɗaya daga cikin jagororin cocin ya sanar cikin jimami game da rasuwar ta Fafaroma Fraincis, inda ya ce: “Ya ku ƴan’uwana, cikin alhini, ina sanar da ku game da rasuwar Babanmu a addini, Francis.

Da misalin ƙarfe 7:35 na wannan safiya (Agogon Vatican), Bishop ɗin Roma, Francis ya koma ga mahalicci. Ya sadaukar da rayuwarsa baki ɗaya wajen bauta wa ubangiji da kuma coci.”

“Ya koya mana bin littafi mai tsarki sau da ƙafa, da karsashi da kuma soyayya a fadin duniya, musamman ga wadanda ke cikin talauci da kuma wadanda aka tauye.”

“Cikin godiya mai tarin yawa kan matsayinsa na manzo daga Yesu, mun miƙa ruhin Fafaroma Francis gare ka, kasancewarka mai matuƙar rahama maras iyaka.”

Marigayi Fafaroma Francis ya yi ƙoƙarin kawo sauye-sauye masu dama ga mabiya ɗariƙar katolika, amma ya fi samun goyon baya daga masu ra’ayin mazan jiya.

Shi ne Fafaroma na farko daga nahiyar Amurka, kuma na farko daga ɓarin duniya na kudu.

Ba a taɓa samun wani fafaroma daga wata nahiya ba bayan Turai, tun bayan mutuwar Fafaroma Gregory III wanda aka haifa a Syria a shekarar 741.

Magabacinsa, Fafaroma Benedict XVI shi ne fafaroma na farko da ya yi ritaya daga kan muƙamin don ƙashin kansa a tsawon shekaru 600.

BBC/Hausa

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Fafaroma Rasuwa Fafaroma Francis

এছাড়াও পড়ুন:

An Bude Sabon Babin Huldar Sin Da Koriya Ta Kudu

 

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya November 1, 2025 Daga Birnin Sin An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya November 1, 2025 Daga Birnin Sin Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar November 1, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba
  • Wadi Al-Salam: Maƙabartar Musulmai Mafi Girma A Duniya
  • An Bude Sabon Babin Huldar Sin Da Koriya Ta Kudu
  • Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya
  • An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya
  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
  • M D Duniya Tayi Gargadi Game Da Gwajin Nukiliya Da Amurka Ta Sanar Za ta yi
  • An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m
  • Madagascar Ta Sanar da Kafa Sabuwar Gwamnati Tare da Manyan ‘Yan Adawa
  • Juventus ta ɗauki tsohon kociyan Italiya, Luciano Spalleti