Fafaroma Francis ya Rasu
Published: 21st, April 2025 GMT
Fadar Vatican ta sanar da mutuwar shugaban majami’ar katolika na duniya, Fafaroma Francis yana da shekaru 88 a duniya.
A shekarar 2023 ne cocin ya zaɓi Fafaroman, wanda asalin sunansa shi ne Cardinal Jorge Mario Bergoglio a matsayin wanda zai jagorance ta, bayan saukar Fafaroma Benedict XVI daga kan muƙamin.
Da safiyar Litinin ne ɗaya daga cikin jagororin cocin ya sanar cikin jimami game da rasuwar ta Fafaroma Fraincis, inda ya ce: “Ya ku ƴan’uwana, cikin alhini, ina sanar da ku game da rasuwar Babanmu a addini, Francis.
Da misalin ƙarfe 7:35 na wannan safiya (Agogon Vatican), Bishop ɗin Roma, Francis ya koma ga mahalicci. Ya sadaukar da rayuwarsa baki ɗaya wajen bauta wa ubangiji da kuma coci.”
“Ya koya mana bin littafi mai tsarki sau da ƙafa, da karsashi da kuma soyayya a fadin duniya, musamman ga wadanda ke cikin talauci da kuma wadanda aka tauye.”
“Cikin godiya mai tarin yawa kan matsayinsa na manzo daga Yesu, mun miƙa ruhin Fafaroma Francis gare ka, kasancewarka mai matuƙar rahama maras iyaka.”
Marigayi Fafaroma Francis ya yi ƙoƙarin kawo sauye-sauye masu dama ga mabiya ɗariƙar katolika, amma ya fi samun goyon baya daga masu ra’ayin mazan jiya.
Shi ne Fafaroma na farko daga nahiyar Amurka, kuma na farko daga ɓarin duniya na kudu.
Ba a taɓa samun wani fafaroma daga wata nahiya ba bayan Turai, tun bayan mutuwar Fafaroma Gregory III wanda aka haifa a Syria a shekarar 741.
Magabacinsa, Fafaroma Benedict XVI shi ne fafaroma na farko da ya yi ritaya daga kan muƙamin don ƙashin kansa a tsawon shekaru 600.
BBC/Hausa
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Fafaroma Rasuwa Fafaroma Francis
এছাড়াও পড়ুন:
An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin
Hukumar jin daɗin jama’a ta Jihar Kwara tare da haɗin gwiwar Hukumar Gyaran Hali ta Najeriya sun kama wasu mabarata a titunan Ilorin, ciki har da wasu da aka samu da kuɗaɗen ƙasashen waje.
Daga cikin waɗanda aka kama akwai wani mabaraci mai suna Musa Mahmud daga Jihar Kano, wanda aka samu da takardar daloli.
Musa Mahmud ya shaida wa manema labarai cewa wani ne ya ba shi takardar Dala a Abuja.
Jami’ai sun bayyana damuwa kan yadda masu bara ke riƙe da kuɗaɗen da ba su dace da yanayin rayuwarsu ba.
Mutuwar majinyata: Asibitin Aminu Kano na roƙon KEDCO ya dawo da wutar lantarki Cire tallafin man fetur shi ne abin da ya dace —Sarki Sanusi II“Za mu bincika asalin waɗannan kuɗaɗen da kuma dalilin da ya sa suke da su,” in ji Adebayo Okunola, shugaban cibiyar gyaran hali a Jihar Kwara.
Jami’an gwamnati sun kwashe kusan mutane 40 daga wuraren da suka haɗa da Tipper Garage, Offa Garage, Tank da Geri Alimi Roundabout.
Jami’an sun ce bakwai daga cikin waɗanda aka kama an taɓa kama su a baya, amma sun koma tituna bayan an sako su.
Kwamishinar jin daɗin jama’a ta jihar, Dakta Mariam Imam, ta ce adadin masu bara da aka kama ya ragu sosai idan aka kwatanta da na baya, inda ta ce suna sauya dabaru don su guje wa kama.
Ta roƙi jama’a da su daina ba wa masu bara kuɗi kai tsaye, su maida gudummawarsu ta hanyar wuraren ibada da gidajen marayu.
Jami’an gyaran hali sun ce za a tilasta wa waɗanda aka kama su yi aikin tsaftace tituna a matsayin horo da kuma darasi.
Wasu daga cikin masu barar sun roƙi gwamnati da ta tausaya musu, ba su da wata hanyar rayuwa sai bara.