Gwamna Uba Sani ya amince da sabon tsarin biyan  diyya ta hanyar amfani da fasahar zamani  ga Hukumar Kula da Bayanan Filaye ta Kaduna (KADGIS), da nufin dakile almundahana a harkokin biyan diyya na filaye a fadin jihar.

Daraktan Hukumar KADGIS Dr. Bashir Garba Ibrahim, ne ya bayyana hakan yayin da ya karbi bakuncin mambobin Kungiyar ‘Yan Jarida ta kasa (NUJ), rashen Rediyon Najeriya Kaduna, a ofishinsa da ke Kaduna.

Dr. Bashir Garba Ibrahim ya bayyana cewa wannan sabuwar manhaja za ta rika adana bayanan masu asalin filayen da za a biya diyya, da suka hada da daukar hoton ‘yan yatsun da lambar katinsu na dan kasa NIN, domin hana masu zamba karbar diyya akan filayen da ba nasu ba ne.

Haka zalika, Daraktan ya yi bayanin sauye-sauye da aka aiwatar a karkashin jagorancinsa tun bayan hawansa kan mukami.

Ya ce cikin shekaru biyu da suka gabata, KADGIS ta warware sama da kararrakin rikicin fili 700, tare da kaddamar da tsarin rangwamen kashi 20 bisa 100 ga wadanda suka biya dukkan bashin da ke kansu gaba daya, wanda hakan ya inganta samun kudaden shiga da inganta ayyuka matuka.

Dr. Bashir Garba ya tabbatar da cewa yanzu takardar mallakar fili (Certificate of Occupancy – C of O) tana cikin tsarin gaggawa, inda ake iya fitar da ita cikin sa’o’i 24 muddin dukkan sharudda sun cika, inda ake iya bayar da takardun shaidar mallakar sama da 200 a kowane mako.

A nasa jawabin, Shugaban NUJ reshen Rediyon Najeriya Kaduna, Umar Adamu S. Fada, ya yaba wa Daraktan da dukkan ma’aikatan hukumar bisa wadannan sauye-sauye, musamman na sabuwar manhajar  biyan diyya, da kuma hanzarta fitar da takardun shaidar mallaka.

Ya nuna farin ciki da damar hadin gwiwa a tsakanin bangarorin biyu, tare da bayyana shirin kungiyar na yin aiki tare da sashen hulda da jama’a na hukumar domin inganta samar da bayanai.

Kungiyar ta kuma yi tayin tallafawa hukumar, ta hanyar amfani da shirye-shiryen tasharsu don kara kusantar da jama’a ga ayyukan hukumar, da kara fadakar da su kan harkokin filaye a fadin jihar.

 

Umar S. Fada 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An tattauna yadda za a inganta walwalar malamai a Gombe

Ƙungiyar Malaman Makarantu ta Najeriya (NUT) reshen Jihar Gombe, ta ziyarci shugaban ƙungiyar shugabannin ƙananan hukumomi na jihar, Barista Sani Ahmad Haruna, a ofishinsa da ke Gombe.

Shugaban ƙungiyar, wanda shi ne shugaban Ƙaramar Hukumar Gombe, ya bayyana cewa gwamnati da shugabannin ƙananan hukumomi za su ci gaba da yin duk mai yiwuwa wajen inganta walwalar malamai.

Tinubu ya janye dokar ta-ɓaci da ya sanya a Ribas Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi

Ya ce: “Ba za mu taɓa barin malamai su shiga cikin matsanancin hali ba. Za mu duba matsalolinsu domin tabbatar da walwalarsu da ci gaban ilimi a jihar.”

Sani, ya kuma yaba da yadda NUT ke tattaunawa cikin lumana da kawo shawarwari maimakon ɗaukar matakan da za su iya kawo tsaiko ga harkar ilimi.

A nasa jawabin, shugaban NUT na jihar ya ce sun kai ziyarar ne domin tattauna matsalolin da malamai ke fuskanta, musamman na makarantun firamare da ƙananun sakandare da ke ƙarƙashin kulawar ƙananan hukumomi.

Ya ƙara da cewa manufar NUT ita ce samar da fahimtar juna da haɗin kai tsakaninsu da shugabannin ƙananan hukumomi domin gano hanyoyin magance matsaloli cikin lumana.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 
  • Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka
  • An tattauna yadda za a inganta walwalar malamai a Gombe
  • NECO ta saki sakamakon jarabawar 2025
  • Gwamnatin Kano Ta Inganta Cibiyoyin Horas Da Sana’o’i Domin Dakile Aikata Laifuka Tsakanin Matasa
  • DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya
  • Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok
  • Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara