Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Zamfara Ta Tabbatar Da Harin ‘Yan Bindiga A Banga
Published: 9th, April 2025 GMT
Rundunar ‘yan sandan Jihar Zamfara ta tabbatar da wani mummunan hari da ‘yan bindiga suka kai a garin Banga, da ke cikin karamar hukumar Kauran Namoda, inda aka kashe mutane biyu tare da sace wasu da dama.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sanda ta jihar, DSP Yazid Abubakar, ne ya bayyana hakan cikin wata tattaunawa ta wayar tarho da wakilinmu da ke Gusau, babban birnin jihar.
DSP Abubakar ya ce bincike na ci gaba da gudana domin gano adadin mutanen da aka sace a harin.
Ya tabbatar da cewa ana kokari don ganin an ceto mutanen da aka sace cikin koshin lafiya.
Yazid ya kara da cewa an kara kaimi wajen daukar matakan tsaro domin hana faruwar irin wannan lamari a nan gaba.
Shaidu sun shaida wa Rediyon Najeriya cewa maharan sun farmaki garin ne da misalin tsakar dare a ranar Laraba, inda suka buda wuta daga wurare da dama, lamarin da ya haifar da firgici ga mazauna garin.
Wani mazaunin garin da ya nemi a sakaya sunansa ya bayyana cewa ‘yan bindigar sun yi ta barna na tsawon sa’o’i, inda suka kashe wani dattijo da wata yarinya ‘yar shekara 18 mai suna Amina.
Ya ce da farko maharan sun sace kimanin mutane 26, amma ba su samu nasarar guduwa da su baki daya ba, sakamakon hanzarin da jami’an tsaro da ‘yan sa-kai suka yi.
Wakilinmu ya samu rahoton cewa hadin gwiwar jami’an tsaro da ‘yan sa-kai ya kai ga kashe wasu daga cikin ‘yan bindigar, yayin da wasu suka tsere da raunukan harbin bindiga. An kuma tabbatar da cewa maharan sun kasa guduwa da shanun da suka sace.
A cewar shaidu, jami’an tsaro da taimakon jiragen saman rundunar sojin saman Najeriya sun toshe hanyar da maharan ke kokarin tserewa ta kusa da kauyen Yamutsawa.
Daga Aminu Dalhatu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
‘Yan Sandan Nasarawa Sun Kama Mutum Shida Da Laifin Fashi Da Makami Da Garkuwa Da Mutane
Rundunar ‘yan sandan jihar Nasarawa ta cafke wasu mutane shida da ake zargin ‘yan fashi da makami da masu garkuwa da mutane ne a karamar hukumar Doma da ke jihar.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar SP Ramhan Nansel ya bayyana haka a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a lafiya, ya ce jami’an sun kuma kama wani makiyayi dauke da makamai a karamar hukumar Keana ta jihar.
Sanarwar ta ce, jami’an sashin Doma da ke aiki da sahihan bayanan sirri daga wani dan kasa mai kishin kasa, karkashin jagorancin jami’in ‘yan sandan shiyya, sun kai samame a wata maboyar ‘yan ta’adda da ke Yelwa Ediya inda aka kama wadanda ake zargin.
Ya ce a yayin da ake yi musu tambayoyi, wadanda ake zargin sun amsa laifin yin garkuwa da wani kansila mai ci inda suka sace wayoyin hannunsa guda biyu.
Sun kuma amince da cewa sun tare hanyar Doma zuwa Yelwa ne inda suka kai hari kan wani Ibrahim Haruna Yelwa Ediya tare da kwace babur dinsa kirar Bajaj wanda kudinsa ya kai ₦970,000 yayin da ake sayar da babur din da suka sace.
SP Ramhan Nansel ya bayyana cewa, a yayin aikin jami’an sun kwato kudi ₦100,000 – kudaden da aka siyar da babur din da aka binne a daji, tare da babur Bajaj daya.
A wani labarin makamancin haka, jami’an sashin Keana sun amsa kiran da suka yi na cewa makiyayan da ke kiwo a filayen gonaki a Gidan Zaki Hassan da ke karamar hukumar Kuduku a karamar hukumar Keana, yayin da makiyayan suka yi ta harbe-harbe kafin su gudu.
‘Yan sandan da ke aiki da jama’ar gari sun kama wani makiyayi mai shekaru 20, sannan sun kwato bindiga samfurin AK-47 guda daya dauke da harsashi guda shida.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Shattima Jauro Mohammed, ya bayar da umarnin mika duk wadanda ake tuhuma zuwa sashin binciken manyan laifuka na jihar domin gudanar da bincike mai zurfi tare da gurfanar da su gaban kuliya.
CP Mohammed ya jaddada kudirin rundunar na tabbatar da zaman lafiya ga kowa da kowa, yana mai gargadin cewa ba za a samu mafaka ga masu aikata laifuka ba.
Ya bukaci mazauna yankin da su kasance masu bin doka da oda kuma su ci gaba da bayar da bayanai masu inganci a kan lokaci don taimakawa ayyukan ‘yan sanda.
Rel/Aliyu Muraki/Lafia.