Manyan Matakai Biyar Da Manoma Da Masu Zuba Hannun Jari A Fannin Aikin Noma Ya Kamata Su Yi La’akari Da Su Kamar Yadda kwararrun Suka Bayar Da Shawara:

1- Irin Kwakwar Manja Na Malesiya

Bukatar da ake da ita ta Irin Kwakwar Manjan Nijeriya a duk shekara, ya kai na tan miliyan 3, inda kuma wanda ake samarwa a cikin kasar, ya ragu da tan miliyan 1.

4.

Kazalika, a gonar da ake noman Kwakwar Manja, za a iya samar da tan 12.5 a kowace hekta daya a duk shekara. Misali, a 2023 a heckta 20 a cikin shekara daya, an girbe Kwakwar da ta kai kimanin tan 250, inda akalla aka samu ribar kimanin Naira 150,000 na kowanne tan daya, wanda kuma ke nuna karin samun kudin shigar da ya kai Naira miliyan 37.5.

Hakan ya kuma kara nuna yadda aka kara bunkasa samun kudin shiga a shekarar da kimanin Naira miliyan 26.25.

2- Gonar  Noman Filanten:

Nijeriya ce kan gaba a duniya wajen noman Filanten, duba da cewa; a duk shekara ana noma amfanin da ya kai kimanin tan miliyan 2.8 zuwa tan miliyan 3.1.

Idan kana da Naira miliyan 5, za ka iya mallakar hekta ta noman Filanten, amma ya danganta da inda gonar taka take.

Haka zalika, bisa bai wa gonar kulawar da ta kamata, a tushe daya na Filanten a shekara, za a iya samar kimanin rassa 10,000.

Sannan, duk Nono daya na Filanten, ana sayar da shi daga Naira 2,000 zuwa Naira 4,000, inda a shekara daya, za a iya tara sama da Naira miliyan 40, wato tun daga wata 18 da aka shuka Irin nata.

Kulawar da ake ba shi a shekara bayan an shuka Irinsa, har zuwa girmansa da fara nunarsa, an kiyasata ana kashe sama da Naira miliyan 2, inda manoman za su iya samun ribar sama da miliyan 18 ko fiye da haka a shekara daya.

3- Gonar  Noman Dabino:

Nijeriya ce kan a gaba a Afirka wajen noman Dabino, duba da cewa; an kiyasta cewa, a shekara daya ana noma sama da tan 250,000.

Sai dai, abin takaici a 2024, Nijeriya ta shigo da Dabino daga ketare da ya kai na dala miliyan 17.8, inda kasar kuma ta fitar da Dabinon na kimanin dala miliyan 2,070 kacal.

Amfanin da ake yi da shi a duniya a shekara daya, ya kai akalla na tan miliyan 8.5, inda a gabas ta tsakiya da Afirka ta tsakiya, suka kasance kan gaba wajen nomansa da kuma rabar da shi.

Dabino na kaiwa tsawon shekara biyar kafin ya fara yin ‘ya’ya.

4- Irin Kwaka Na Malesiya:

A cewar wasu bayanai da Hukumar Kula da Samar da Abinci da Aikin Gona ta Duniya (FAO) ta fitar, ta dora Nijeriya kan mataki na 18 wajen noman Kwaka a duniya, duba da cewa; kasar na noma Kwakawar da ta kai kimanin tan 225,526 2021.

Wanda ya zuba hannun jari a fannin, zai  iya samun ribar sama da Naira miliyan 36 daga hekta goma da aka noma. Samar da heckta 10 a gonar noman Kwaka, zai kasance daidai da zuba hannun jari na kimanin Naira 26,550,000.

Idan har aka shuka ta, a kowace bishiya daya a shekara za ta iya samar da ‘ya’ya 100 , inda za su kai yawan ‘ya’ya 70 da za a girbe a shekara guda.

Kowane Nono daya na Kwakawar, za a iya sayar da shi kan Naira 900, wanda kuma za a iya samar da kudin shiga kimanin Naira  63,000,000 a shekara daya.

Kazalika, bayan ware kudin aikin da manomi ya kashe, zai kuma iya samun ribar da ta kai ta Naira 36,450,000 a shekara daya.

5- Gonar Noman Kashu:

A cewar wani rahoto da jaridar ‘The Nation’ ta wallafa, sama da hecta 600,000 aka ware domin nomansa, wanda zai iya samar da kimanin tan 220,000 a shekara. Farashin Kashu, ya kai daga tan Naira miliyan daya zuwa Naira miliyan 1.5.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: da Naira miliyan a shekara daya kimanin Naira iya samar da a iya samar tan miliyan wajen noman a a shekara

এছাড়াও পড়ুন:

Mun yi asarar shanu 340 a hannun ɓarayi a Yuli — Miyetti Allah

Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya reshen Jihar Benuwe, a ranar Alhamis, ta bayyana cewa aƙalla shanu 340 na mambobinta ne aka sace a cikin watan Yuli na 2025.

Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da sakataren ƙungiyar na jiha, Ibrahim Galma ya fitar kuma aka rabawa manema labarai a Makurdi.

Tinubu ya tsawaita wa’adin aikin shugaban hukumar Kwastam Mutum 9 sun rasu a hatsarin kwale-kwale a Jigawa

A cewar sanarwar, lamarin ya faru ne a garin Agatu da wasu sassan Ƙaramar hukumar Guma da ke Jihar Benuwe.

Galma ya kuma yi zargin cewa, ɓarayin shanu da ke afkawa jama’a a Ƙaramar hukumar Agatu sun faɗaɗa hare-harensu zuwa sassan Jihar Kogi.

“A ranar 19 ga Yuli, 2025 wasu da ake zargin ’yan ƙabilar unguwar Eguma ne a ƙaramar hukumar Agatu sun sace shanu 73 na wani Sale Abubakar (makiyayi Fulani), kuma har ya zuwa yanzu ba a ƙwato shanun ba.

“A ranar 21/7/2025 wani gungun masu aikata laifuka daga unguwar Agatu sun yi awon gaba da shanu 80 na Ardo Sarkin Fulanin Bagana, an yi awon gaba da shanun ne a Jihar Kogi, kusa da kan iyaka da ƙaramar hukumar Agatu ta Jihar Benuwe.

Ɓarayin sun kwashe shanun zuwa ƙauyukan Agatu. Daga baya kuma, an ƙwato shanu 30 daga cikin 80 a Agatu, inda ba a iya gano 50 ba.

“A ranar 24 ga Yuli, 2025 wasu miyagu matasa ‘yan garin Agatu sun yi awon gaba da wasu shanu 213 na Garah Mobaba, hakan kuma ya faru ne a kan iyaka tsakanin Jihar Kogi da Ƙaramar hukumar Agatu ta Jihar Benuwe, haka kuma lamarin na faruwa a wasu sassan Ƙaramar hukumar Guma ta Jihar Benuwe, inda aka samu rahotannin sace-sacen shanu da kuma kashe-kashen makiyaya.”

Shanun mallakin Sale Abubakar (makiyayin Fulani), kuma har ya zuwa yanzu, ba a ƙwato shanun da aka sace ba.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kananan Yan Wasan Dabben Gargajiya Na Iran Sun Zama Zakara A Gasar Wannan Shekara
  • Mun yi asarar shanu 340 a hannun ɓarayi a Yuli — Miyetti Allah
  • Man Utd Na Tattaunawa Da Golan PSG, Chelsea Ta Nace Wa Garnacho
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Tallafin Miliyoyin Naira Ga Ƴan NURTW da Mahauta a Jigawa
  • Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana
  • An shawarci Manoman Kwara Da Su Yi Taka-Tsan-Tsan Saboda Hasashen Ruwa Da Tsawa A Jihar
  • Faransa Ta Bayyana Wuce Gona Da Irin ‘Yan Sahayoniyya Kan Falasdinawa Da Ayyukan Ta’addanci
  • Gwamnatin Sakkwato Ta Sayo Manyan Tan-tan 250 Na Sama Da Naira Biliyan 22
  • Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana
  • Mutum daya Yayi Shahada 4 Sun Ji Rauna Sanadiyar Hare-Haren HKI A Lebanon