Hadin Kai Ne Kadai Zai Kai Masana’antar Kannywood Tudun Mun Tsira -Ado Ahmed Gidan Dabino
Published: 9th, March 2025 GMT
Hakan ya sa yanzu ba kasafai masu shirya fina finan Hausa ke mayar da adadin abinda su ka kashe wajen shirya fim ba, don kuwa ba kowane yake da yawan mabiyan da za su kalli abinda ya dora a YouTube ba da har zai samu wani abin kirki, hakazalika gidajen Talabijin da ke saye ba wani kudin azo a gani suka bayarwa ba, yanzu idan fim dinka bai kai matsayin shiga tashar NETFLID ta kasar Amurka ba, ba lallai ne ya kai inda kake bukata ba inji shi.
Ya ci gaba da cewa hakan yasa nike bayar da shawara wajen ganin mun fadada tunaninmu wajen zakulo wasu sabbin hanyoyi da zamu dinga fitar da fina finanmu zuwa inda ya kamata domin samun kudaden shiga kamar sauran abokan sana’armu da ke Kudancin Nijeriya, inda zaka ji sun samu miliyoyin kudade ta hanyar fina finansu.
Sannan kuma akwai bukatar hadin kai a tsakaninmu ta yadda zamu kasance tsintsiya madaurinki daya, misali idan mutum daya zai iya zuba jarin miliyan 10 ya shirya fim din da ba zai iya zuwa koina ba, kamata ya yi ace mutane da yawa sun hadu sun zuba jari mai yawa wajen shirya fim din da zai iya tasiri a idon Duniya kuma su samu manyan kudaden da za su cire kudin da su ka zuba su kuma samu kudaden da za su shirya wani fim din a gaba.
Daga karshe Ado Ahmed Gidan Dabino ya bukaci jaruman fim, wadanda su ka samu wani mukami na jagoranci a masana’antar ko kuma a cikin gwamnatin jiha ko ta tarayya, da su dinga kwatanta adalci bakin gwargwado kuma su dinga tunawa da abokan sana’arsu wadanda ba su samu irin wannan damar ba yayin gudanar da mulki.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Kannywood
এছাড়াও পড়ুন:
Matawalle Ya Ba Magoya Bayan APC Na Zamfara Naira Miliyan 500
Ministan kasa a ma’aitar tsaro, Mohammed Bello Matawalle, ya ba magoya bayan jam’iyyar (APC) a jihar Zamfara gudumuwar kudi naira miliyan 500 domin a taimaka musu wajen gudanar da azumin watan Ramadan cikin sauki.
Mai ba da shawara na musamman kan harkokin siyasa Mattawalle, Alhaji Ibrahim Danmalikin Gidan Goga ne ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Gusau.
A cewar Gidan-Goga, Ministan ya zabi bayar da kudi ne maimakon kayan abinci, saboda tuni wasu ‘yan siyasa a jihar suka raba wa magoya bayansu hatsi.
Ya kuma jaddada cewa tallafin kudi zai baiwa magoya bayan jam’iyyar APC damar siyan wasu muhimman abubuwan da ake bukata a cikin watan Ramadan.
“A wannan karon, maimakon ba wa jama’a hatsi iri-iri, Ministan ya yanke shawarar bayar da tsabar kudi saboda wasu ‘yan siyasa sun riga sun raba kayan abinci,” ya bayyana.
Ya ci gaba da cewa, tsohon Gwamna Sanata Abdul Aziz Yari ya bayar da gudummawar tireloli na hatsi iri-iri 496, wanda hakan ya sa Ministan ya kara wannan kokari da tallafin kudi.
Gidan-Goga ya bayyana cewa, mutane 200 daga kowace karamar hukuma 14 da ke Zamfara sun karbi ₦100,000 kowanne, wanda ya kai miliyan 280.
“Masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC 24 daga kananan hukumomi biyar na shiyyar Sanatan Zamfara ta Yamma sun karbi ₦250,000 kowanne, wanda ya kai miliyan 30.”
“Masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC 90 daga kananan hukumomin jihar Zamfara ta tsakiya da kuma ta Zamfara ta Arewa sun karbi ₦250,000 kowanne, wanda ya kai miliyan 22.5.”
Sauran nau’ikan wadanda suka ci gajiyar kuma sun sami kudade a matsayin wani bangare na kunshin jin dadin Ramadan na Minista.
Gidan-Goga ya tabbatar da cewa sama da kashi 80 cikin 100 na wadanda aka yi niyya sun karbi kudadensu.
Ya lura cewa wadanda suka amfana daga Bakura, Gummi, Kaura-Namoda, Maradun, Shinkafi, da Talata-Mafara duk sun tattara kudadensu.
Sai dai kawo yanzu mutum 100 da suka ci gajiyar tallafin daga kananan hukumomin Tsafe, Zurmi, Bungudu, Bukkuyum, da Anka ne kowannensu ya karbi nashi kason, yayin da sauran wadanda suka ci gajiyar shirin za a biya su nan gaba kadan.
Ya kara da cewa har yanzu wadanda suka ci gajiyar tallafin daga karamar hukumar Birnin Magaji ba su samu kudadensu ba sakamakon tsaikon da aka samu wajen gabatar da jerin sunayen wadanda suka karba.
AMINU DALHATU