Hakan ya sa yanzu ba kasafai masu shirya fina finan Hausa ke mayar da adadin abinda su ka kashe wajen shirya fim ba, don kuwa ba kowane yake da yawan mabiyan da za su kalli abinda ya dora a YouTube ba da har zai samu wani abin kirki, hakazalika gidajen Talabijin da ke saye ba wani kudin azo a gani suka bayarwa ba, yanzu idan fim dinka bai kai matsayin shiga tashar NETFLID ta kasar Amurka ba, ba lallai ne ya kai inda kake bukata ba inji shi.

Ya ci gaba da cewa hakan yasa nike bayar da shawara wajen ganin mun fadada tunaninmu wajen zakulo wasu sabbin hanyoyi da zamu dinga fitar da fina finanmu zuwa inda ya kamata domin samun kudaden shiga kamar sauran abokan sana’armu da ke Kudancin Nijeriya, inda zaka ji sun samu miliyoyin kudade ta hanyar fina finansu.

Sannan kuma akwai bukatar hadin kai a tsakaninmu ta yadda zamu kasance tsintsiya madaurinki daya, misali idan mutum daya zai iya zuba jarin miliyan 10 ya shirya fim din da ba zai iya zuwa koina ba, kamata ya yi ace mutane da yawa sun hadu sun zuba jari mai yawa wajen shirya fim din da zai iya tasiri a idon Duniya kuma su samu manyan kudaden da za su cire kudin da su ka zuba su kuma samu kudaden da za su shirya wani fim din a gaba.

Daga karshe Ado Ahmed Gidan Dabino ya bukaci jaruman fim, wadanda su ka samu wani mukami na jagoranci a masana’antar ko kuma a cikin gwamnatin jiha ko ta tarayya, da su dinga kwatanta adalci bakin gwargwado kuma su dinga tunawa da abokan sana’arsu wadanda ba su samu irin wannan damar ba yayin gudanar da mulki.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Kannywood

এছাড়াও পড়ুন:

Ƙasashe 12 da suka samu tikitin Kofin Nahiyyar Afrika na mata

A ci gaba da wasannin neman shiga gasar cin kofin Nahiyyar Afirka na 2026 da ƙasar Morocco zata karɓi baƙunci, yanzu haka ƙasashe 6 sun samu nasarar shiga gasar.

Ƙasashen da suka samu tikitin sun haɗa da mai masaukin baƙi: Morocco  da Najeriya da Zambia da Tanzania da Malawi da Algeria da Ghana da Senegal da Kenya da Burkina Faso da Cape Verde da Afrika ta Kudu.

Gwamnan Bauchi na neman ƙirƙirar sabbin ƙananan hukumomi 29 ACF ta mara wa gwamnatin Tinubu baya

Wannan dai ita ce gasa karo na 14 da za a buga a tarihi daga ranar 17 ga watan Maris zuwa 3 ga watan Afrilu na 2026.

Ƙasashen da suka kai wasan kusa da na ƙarshe a Kofin Nahiyyar Afirkan za su wakilci nahiyar a Kofin duniya na mata da za a buga a ƙasar Brazil a 2027.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya
  • Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar
  • Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
  • ‘An Kashe Masu Zanga-zanga Akalla 500 a Tanzania’
  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • Shugaban Lebanon Ya Umarci Sojoji Da Su Fuskanci Duk Wani Kutse Na Isra’ila A Kudancin Kasar
  • Borno ta fara fitar da kayan robobi zuwa ƙasashen waje – Zulum
  • Gobara ta tashi a babban kanti a Abuja
  • Ƙasashe 12 da suka samu tikitin Kofin Nahiyyar Afrika na mata