Hadin Kai Ne Kadai Zai Kai Masana’antar Kannywood Tudun Mun Tsira -Ado Ahmed Gidan Dabino
Published: 9th, March 2025 GMT
Hakan ya sa yanzu ba kasafai masu shirya fina finan Hausa ke mayar da adadin abinda su ka kashe wajen shirya fim ba, don kuwa ba kowane yake da yawan mabiyan da za su kalli abinda ya dora a YouTube ba da har zai samu wani abin kirki, hakazalika gidajen Talabijin da ke saye ba wani kudin azo a gani suka bayarwa ba, yanzu idan fim dinka bai kai matsayin shiga tashar NETFLID ta kasar Amurka ba, ba lallai ne ya kai inda kake bukata ba inji shi.
Ya ci gaba da cewa hakan yasa nike bayar da shawara wajen ganin mun fadada tunaninmu wajen zakulo wasu sabbin hanyoyi da zamu dinga fitar da fina finanmu zuwa inda ya kamata domin samun kudaden shiga kamar sauran abokan sana’armu da ke Kudancin Nijeriya, inda zaka ji sun samu miliyoyin kudade ta hanyar fina finansu.
Sannan kuma akwai bukatar hadin kai a tsakaninmu ta yadda zamu kasance tsintsiya madaurinki daya, misali idan mutum daya zai iya zuba jarin miliyan 10 ya shirya fim din da ba zai iya zuwa koina ba, kamata ya yi ace mutane da yawa sun hadu sun zuba jari mai yawa wajen shirya fim din da zai iya tasiri a idon Duniya kuma su samu manyan kudaden da za su cire kudin da su ka zuba su kuma samu kudaden da za su shirya wani fim din a gaba.
Daga karshe Ado Ahmed Gidan Dabino ya bukaci jaruman fim, wadanda su ka samu wani mukami na jagoranci a masana’antar ko kuma a cikin gwamnatin jiha ko ta tarayya, da su dinga kwatanta adalci bakin gwargwado kuma su dinga tunawa da abokan sana’arsu wadanda ba su samu irin wannan damar ba yayin gudanar da mulki.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Kannywood
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Najeriya Ta Yi Allawadai Da Harin Da “Isra’ila” Ta Kawo Wa Iran
A wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen Najeriya ta fitar, ta yi tir da harin na Isra’ila akan Iran tare da bayyana cewa, ya haifar da rikici a tsakanin bangarorin biyu da kuma musayar harba makamai masu linzami.
Gwamnatin ta Najeriya ta nuna bakin cikinta akan abinda ya faru, tare da kuma da yin kiran a tsagaita wutar yaki da gaggawa, da kai zuciya nesa.
Har ila yau, sanarwar ma’aikatar harkokin wajen ta Nigeria wacce kakakinta Kimiebi Imomotimi Ebienfa ya rattabawa hannu a yau Asabar,14 ga watan Yuni 2025, ta jaddada cewa; yaki ba zai maye gurbin tattaunawa ba, kuma hanyar diplomasiyya ce za ta kai ga samar da zaman lafiya mai dorewa, girmama juna da aiki da dokokin kasa da kasa.,