HausaTv:
2025-07-31@16:48:25 GMT

An Fara Tattaunawa Tsakanin Isra’ila Da Hamas Kan Mataki Na Gaba Na Tsagaita Wuta

Published: 28th, February 2025 GMT

Kasar Masar ta ce an fara tattaunawa tsakanin Isra’ila da Hamas kan mataki na gaba na tsagaita wuta a Gaza.

Ma’aikatar yada labaran kasar Masar ta fada a jiya Alhamis cewa, tawagogin Isra’ila, Qatar da Amurka na birnin Alkahira domin tattaunawa mai zurfi kan yarjejeniyar tsagaita bude wuta a Gaza.

“Bangarorin da abin ya shafa sun fara tattaunawa mai zurfi don tattaunawa kan matakai na gaba na yarjejeniyar tsagaita wuta, a ci gaba da kokarin tabbatar da aiwatar da fahimtar juna da aka amince da su a baya,” in ji sanarwar.

Ta kara da cewa, masu shiga tsakani suna tattaunawa kan hanyoyin da za a iya “inganta isar da kayayyakin jin kai” zuwa yankin Falasdinu da yaki ya daidaita.

A ranar Alhamis, ministan harkokin wajen Isra’ila Gideon Saar ya ce wata tawaga za ta je Masar domin ganin ko akwai halin tattaunawa kan tsawaita wa’adin zangon farko na tsagaita bude wuta da zai kare nan da kwanaki biyu.

Jami’an gwamnatin sun ce suna neman tsawaita matakin farko, inda Hamas za ta sakin ‘yan Isra’ila guda uku a kowane mako domin musayar Falasdinawa da Isra’ila ke rike da su.

Majalisar ministocin Isra’ila na fuskantar matsin lamba daga jama’a na su tsaya kan tsagaita bude wuta don ‘yantar da sauran fursunonin.

Matakin na farko na tsagaita wutar dai zai kare ne a ranar Asabar.

Kimanin mutane 58 ne Hamas ke tsare da su har yanzu a Gaza, ciki har da 34 da sojojin Isra’ila suka ce sun mutu.

Kungiyar ta Hamas dai ta ce a shirye take ta sako dukkan sauran mutanen da ta ke garkuwa da su gabadaya idan har aka cimma yarjejeniyar a matakin na biyu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza

Ministan ya kuma ce ƙasarsa na shirin sanya hannu a wata takarda don neman goyon bayan sauran ƙasashe wajen ganin an kafa ƙasar Falasɗinu da Isra’ila.

A taron Majalisar Ɗinkin Duniya da aka gudanar na kwana biyu, ƙasashe 125 sun amince cewa hanyar warware rikicin Gaza ita ce kafa ƙasashe biyu, wato Falasɗinu da Isra’ila.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Man Utd Na Tattaunawa Da Golan PSG, Chelsea Ta Nace Wa Garnacho
  • Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza
  • Amincewa Da Kasar Falasɗinu: Birtaniya Ta Gindaya Wa Isra’ila Sharuɗɗa
  •  Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai
  • Kasar Iran Ta Musanta Yin Katsalandan A Tattaunawar Neman Tsagaita Bude Wuta A Gaza
  • Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa
  • An fara shigar da kayan agaji a Gaza
  • An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden
  • Hamas: HKI Da Amurka Sun Janye Daga Tattaunawa Ne Don Sake Damarar Yaki
  • Shugaban Kasar Masar Ya Roki Trump Ya Kawo Karshen Yaki A Gaza