HausaTv:
2025-06-15@21:47:07 GMT

An Fara Tattaunawa Tsakanin Isra’ila Da Hamas Kan Mataki Na Gaba Na Tsagaita Wuta

Published: 28th, February 2025 GMT

Kasar Masar ta ce an fara tattaunawa tsakanin Isra’ila da Hamas kan mataki na gaba na tsagaita wuta a Gaza.

Ma’aikatar yada labaran kasar Masar ta fada a jiya Alhamis cewa, tawagogin Isra’ila, Qatar da Amurka na birnin Alkahira domin tattaunawa mai zurfi kan yarjejeniyar tsagaita bude wuta a Gaza.

“Bangarorin da abin ya shafa sun fara tattaunawa mai zurfi don tattaunawa kan matakai na gaba na yarjejeniyar tsagaita wuta, a ci gaba da kokarin tabbatar da aiwatar da fahimtar juna da aka amince da su a baya,” in ji sanarwar.

Ta kara da cewa, masu shiga tsakani suna tattaunawa kan hanyoyin da za a iya “inganta isar da kayayyakin jin kai” zuwa yankin Falasdinu da yaki ya daidaita.

A ranar Alhamis, ministan harkokin wajen Isra’ila Gideon Saar ya ce wata tawaga za ta je Masar domin ganin ko akwai halin tattaunawa kan tsawaita wa’adin zangon farko na tsagaita bude wuta da zai kare nan da kwanaki biyu.

Jami’an gwamnatin sun ce suna neman tsawaita matakin farko, inda Hamas za ta sakin ‘yan Isra’ila guda uku a kowane mako domin musayar Falasdinawa da Isra’ila ke rike da su.

Majalisar ministocin Isra’ila na fuskantar matsin lamba daga jama’a na su tsaya kan tsagaita bude wuta don ‘yantar da sauran fursunonin.

Matakin na farko na tsagaita wutar dai zai kare ne a ranar Asabar.

Kimanin mutane 58 ne Hamas ke tsare da su har yanzu a Gaza, ciki har da 34 da sojojin Isra’ila suka ce sun mutu.

Kungiyar ta Hamas dai ta ce a shirye take ta sako dukkan sauran mutanen da ta ke garkuwa da su gabadaya idan har aka cimma yarjejeniyar a matakin na biyu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi

Bayan hakan, Pogba ya kunce kwantiraginsa da Juventus a watan Nuwamban 2024, kuma tun watan Maris da ya gabata ya samu damar komawa fili domin shirya dawowarsa.

Yanzu haka yana ci gaba da atisaye tare da fatan ƙulla sabuwar yarjejeniya da Monaco domin ci gaba da taka leda a ƙasarsa ta haihuwa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ƴansanda Sun Fara Tsananta Ɗaukar Mataki Kan Ƴan Daba A Kano
  • Iran Ta Cilla Makamai Kan HKI Da Rana A Karon Farko A Yau Lahadi
  • Iran Ta Sanar Da Dakatar Da Tattaunawa Da Amurka A Wannan Lokaci Da Take Fuskantar Yaki Daga Isra’ila
  • Oman ta tabbatar da soke tattaunawar Iran da Amurka zagaye na shida
  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi
  • An Samu Babban Canji Kan Tsarin Ciniki A Tsakanin Sin Da Afirka
  • Jami’in Hamas Ya Jinjinawa Iran Kan Kakkausan Martanin Da Ta Mayar Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Iran : Halin da ake ciki ba zai iya bada damar tattaunawa da Amurka ba
  • Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi