HausaTv:
2025-11-02@06:25:19 GMT

Sharki: Takaitaccen Rayuwar Sayyid Shahid Hassan Nasarallah (r)

Published: 23rd, February 2025 GMT

Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka, sharhin bayan labarammu zai yi magana dangane da ‘Sayyid Haassan Nasarallah’ shahidin Al-umma’ wanda aka yi jana’izar sa a ranar lahadin da ta gabata. Wanda ni tahir amin zan karanta.

A ranar lahadi 23  ga watan Fabrayrun shekara ta 2025 ne aka gudanar da Jana’izar babbsan sakataren kungiyar Hibullah, sayyid Hassan nasaralla, da kuma magajinsa na tsawon kwanaki 6 Sayyid Hashim safiyyuda deen, kafin haka shi ne shugaban majalisar zartarwa na kungiyar Hizbullah.

 

An haifi sayyid Hassan nasaralla (r ) a ranar 31 ga watan Augustan shekara ta 1960  a wani kauye a kudancin kasar Lebanon, Sayyid ya tashi a cikin gida mai saukin rayuwa, ya fara karatu kamar yadda ko wani yaro yake tashi a gidajensu a kudancinsu a kudancin kasar Lebanon.  Sannan ya fara karatu addinin a gida, daga bayana ya je birnin Najaf na kasar Iraqi inda yayi karatun a gaban malaminsa nafarko Sayyid Shahid Abbas Al-musawi, amma a gwamnatin Iraki a lokacin wacce ta shiga yaki da kasar Iran ta  kori malaman addina da dama daga kasar ta Iraki daga ciki har da shi Shaida Nasarallah da kuma malaminsa Sayyida Abbas Almusawi.

Bayan sun dawo gida Lebalon Sayyid Hassan Nasarallah ya koma birnin Qom na kasar Iran inda ya ci gaba da karatunsa na addinin. Amma a gwagwarmayan da kungiyar Hizbullah ta kasar Lebanon ta fara da sojojin HKI wadanda a shekara ta 1982 suka mamaye kasar Lebanon daga ciki har da birnin Beirut na kasar, gwagwarmayan ta gaiga sojojin HKI sun kashe malaminsa kuma shugaban kungiyar wato Abbas Almusawi a shekara ta 1992.

Shahasar Sayyida Abbas Almusawi ya sa kungiyar ta ga cewa ba wanda ya dace da shugabancin kungiyar ta kuma ci gaba da shugabancin sayyid Abbas Musawi sais hi sayyid Hassan nasaralla. Sayyida Hassan Nasarallah ya karbi wannan matsayin a ranar 16, ga watan Fabarairu shekara 1992, kuma tun lokacin ne yake jagorantar wannan kungiyar daga nasara zuwa nasarori.

Da farko kungiyar ta sami nasarar korar sojojin HKI daga kasar Lebanon a shekara ta 2000. Wannan nasarar ta fitar da kungiyar a fili a kasar Lebanon da kuma yankin. Da kuma duniya gaba daya.

Don haka Amurka tare da HKI sun yi shirin shafe kungiyar daga doron kasa, wanda ya kai ga yakin da ake kira “yakin kwanaki 33′ a shekara ta 2006 dakarun Hizbullah karkashin  sayyid Hassan Nasarallah, suka basu mamaki, a yakin, inda ta halaka sojojin HKI da dama, suka lalata tankunan yakin ‘samfurin Mirkava’ kirar kasar Amurka. Don haka a aka tsagaita wuta da HKI, ba tare da sojojin HKI sun shiga kasar Lebanon ba, ballanta na su shafe kungiyar hizbulla daga doron kasa. A dole HKI ta amince da kudurin kwamitin tsaro na MDD mai lamba 1701.

Sannan Sayyid Hassan Nasarallah, ya sami nasar musayar fursinoni na HKI, inda yahudawan suka mika fursinonin 5 masu rai wadanda take tsare da su, daya daga cikinsu Samir Qantar yayi shekaru 30 a cikin gidan yari na HKI, da kuma daruruwan gawakin larabawa musamman Falasdinawa da take rike da su. Sanan kungiyar ta mikawa yahudawan gawakin yahudawa biyu da suke tsare da su.

Wannan ma ya kara fitarb da kungiyar ga duniya gaba daya da kuma gano irin kwakwalwan da shugaban wannan kungiyar yake da shi.

Sannan yakin da kungiyar ta shiga don tallafawa Falasdinawa a Gaza, a ranar 8 ga watan Octoban shekara ta 2023, ya kara fitar da irin karfin da kuma ci gaban da kungiyar Ta tayi, inda a cikin watanni kusan 12 na farkon na yakin ta sami nasara korar yahudawa daga arewacin kasar Falasdinu da aka mamaye, ta lalata na’urorin leken asiri HKI da dama a yankin, sannan ta sami nasar amfani da jiragen yakin leken asirinta mai suna Hud-hud wajen saukar hotunan wurare masu muhimmanci a cikin HKI. Da kuma daga karshe bayan da jiragen yahudan suka sauke ton 85 na makaman a kan gine gine guda 6 wadanda suka tabbatar yana cikinsu, sun kashe Sayyid Hassan nasaralla a ranar 27-ga watan Satumba -2024.

Amma kungiyar ta nuna karfta na makamai masu linzami da kuma makamai wasu wargaza tankunan yaki na mirkava, da kuma halaka sojojin HKI, na tsawon kwanaki 60. Wanda ya tilastawa HKI bukatar a tsagaita wuta., amma ba’a sami damar ya masa da kuma Sayyid shafiyyud deen jana’iza ba sai ranar Lahadi 23-02-2025.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Sayyid Hassan nasaralla sayyid Hassan nasaralla Hassan Nasarallah a kasar Lebanon a shekara ta kungiyar ta da kungiyar

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini

Shugaban kasar Nigeria Bola Ahmad Tinubu ya fada wa Shugaban Amurka Donald Trump cewa; a Nigeria ba a lamunta da duk wani rikicin addini.

Shugaban na kasar Najeriya ta mayar wa da Tinubu martani ne saboda yadda ya bayyana Najeriya a matsayin kasa mai jawo damuwa ta musamman”, bisa zargin cewa Mabiya addinin kiristanci suna fuskantar barazanar karewa, ya kuma yi alkawalin cewa Amurkan za ta ba su kariya.

Donald Trump ya ce; Kiristoci suna fuskantar barazanar karar da su a Nigeria, an kuma kashe dubban kiristoci a kasar.”

A yau Asabar, kwana daya daga wancan zancen na Tinibu ne dai shugaban kasar ta Nigeria Bola Ahamd Tinubu mayar da martanin da ya kunshi cewa:  Nageria kasa ce ta Demokradiyya, kuma tsarin mulkinta ya lamuncewa kowa ‘yancin yin addini.”

Har ila yau shugaban kasar ta Najeriya ya ce; Tun daga 2023 gwamnatinmu take mu’amala da hulda da dukkanin malaman kirista da musulmi, kuma tana ci gaba da magance matsalar tsaro da ta shafi dukkanin mutanen kasar daga kowane addini a cikin yankunan kasar.

Shugaba Tinubu ya kuma ce; Bayyana Nigeria a matsayin kasa wacce ake fada da addini, ba ya nuni da hakikanin yadda rayuwa take a kasar, kuma ba a yi la’akari da yadda gwamnati take aiki tukuru domin kare ‘yancin yin addini da akidun mutanen Nigeria ba.”

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran ta damu da halin da ake ciki a yankin El Fasher na Sudan November 1, 2025 Kwamitin Tsaron MDD ya goyi bayan shirin Morocco game da yankin Yammacin Sahara November 1, 2025 Samia Suluhu Hassan ta lashe zaben shugaban kasa a Tanzaniya November 1, 2025 Najeriya ta musanta ikirarin Trump, na cewa Kristoci na fuskantar babbar barazana a kasar November 1, 2025 Majalisar Dinkin Duniya ta damu da hare-haren Amurka a Caribbean da Pacific November 1, 2025 Israila Ta Kai Hari  Kan Ofishin kungiyar UNICEF Dake Gaza A November 1, 2025 Amurka Na Shirin Kai Hari Kan Kasar Venzuwela A Kowanne Lokaci November 1, 2025 Iran Ta Sanya  Da Ranar 30 Ga Watan Nuwamba A Matsayin Ranar Kasa Ta Tsibirai 3 October 31, 2025 Isra’ila Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza October 31, 2025 An Tube Yarima Mai Jiran Gado Na Birtaniya Bayan Da Aka Tabbatar Da Laifinsa October 31, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini
  • Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 
  • Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
  • Zaɓen Tanzania: Shugaba Samia Suluhu Hassan ta yi tazarce
  • Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari
  • NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa
  • Shugaban Lebanon Ya Umarci Sojoji Da Su Fuskanci Kutsen Na Isra’ila A Kudancin Kasar
  • Shugaban Lebanon Ya Umarci Sojoji Da Su Fuskanci Duk Wani Kutse Na Isra’ila A Kudancin Kasar
  • Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 
  • Trump Ya Umarci Ma’aikatar Yakin Amurka Ta koma gwajin makaman nukiliya