HausaTv:
2025-06-15@03:37:40 GMT

Sharki: Takaitaccen Rayuwar Sayyid Shahid Hassan Nasarallah (r)

Published: 23rd, February 2025 GMT

Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka, sharhin bayan labarammu zai yi magana dangane da ‘Sayyid Haassan Nasarallah’ shahidin Al-umma’ wanda aka yi jana’izar sa a ranar lahadin da ta gabata. Wanda ni tahir amin zan karanta.

A ranar lahadi 23  ga watan Fabrayrun shekara ta 2025 ne aka gudanar da Jana’izar babbsan sakataren kungiyar Hibullah, sayyid Hassan nasaralla, da kuma magajinsa na tsawon kwanaki 6 Sayyid Hashim safiyyuda deen, kafin haka shi ne shugaban majalisar zartarwa na kungiyar Hizbullah.

 

An haifi sayyid Hassan nasaralla (r ) a ranar 31 ga watan Augustan shekara ta 1960  a wani kauye a kudancin kasar Lebanon, Sayyid ya tashi a cikin gida mai saukin rayuwa, ya fara karatu kamar yadda ko wani yaro yake tashi a gidajensu a kudancinsu a kudancin kasar Lebanon.  Sannan ya fara karatu addinin a gida, daga bayana ya je birnin Najaf na kasar Iraqi inda yayi karatun a gaban malaminsa nafarko Sayyid Shahid Abbas Al-musawi, amma a gwamnatin Iraki a lokacin wacce ta shiga yaki da kasar Iran ta  kori malaman addina da dama daga kasar ta Iraki daga ciki har da shi Shaida Nasarallah da kuma malaminsa Sayyida Abbas Almusawi.

Bayan sun dawo gida Lebalon Sayyid Hassan Nasarallah ya koma birnin Qom na kasar Iran inda ya ci gaba da karatunsa na addinin. Amma a gwagwarmayan da kungiyar Hizbullah ta kasar Lebanon ta fara da sojojin HKI wadanda a shekara ta 1982 suka mamaye kasar Lebanon daga ciki har da birnin Beirut na kasar, gwagwarmayan ta gaiga sojojin HKI sun kashe malaminsa kuma shugaban kungiyar wato Abbas Almusawi a shekara ta 1992.

Shahasar Sayyida Abbas Almusawi ya sa kungiyar ta ga cewa ba wanda ya dace da shugabancin kungiyar ta kuma ci gaba da shugabancin sayyid Abbas Musawi sais hi sayyid Hassan nasaralla. Sayyida Hassan Nasarallah ya karbi wannan matsayin a ranar 16, ga watan Fabarairu shekara 1992, kuma tun lokacin ne yake jagorantar wannan kungiyar daga nasara zuwa nasarori.

Da farko kungiyar ta sami nasarar korar sojojin HKI daga kasar Lebanon a shekara ta 2000. Wannan nasarar ta fitar da kungiyar a fili a kasar Lebanon da kuma yankin. Da kuma duniya gaba daya.

Don haka Amurka tare da HKI sun yi shirin shafe kungiyar daga doron kasa, wanda ya kai ga yakin da ake kira “yakin kwanaki 33′ a shekara ta 2006 dakarun Hizbullah karkashin  sayyid Hassan Nasarallah, suka basu mamaki, a yakin, inda ta halaka sojojin HKI da dama, suka lalata tankunan yakin ‘samfurin Mirkava’ kirar kasar Amurka. Don haka a aka tsagaita wuta da HKI, ba tare da sojojin HKI sun shiga kasar Lebanon ba, ballanta na su shafe kungiyar hizbulla daga doron kasa. A dole HKI ta amince da kudurin kwamitin tsaro na MDD mai lamba 1701.

Sannan Sayyid Hassan Nasarallah, ya sami nasar musayar fursinoni na HKI, inda yahudawan suka mika fursinonin 5 masu rai wadanda take tsare da su, daya daga cikinsu Samir Qantar yayi shekaru 30 a cikin gidan yari na HKI, da kuma daruruwan gawakin larabawa musamman Falasdinawa da take rike da su. Sanan kungiyar ta mikawa yahudawan gawakin yahudawa biyu da suke tsare da su.

Wannan ma ya kara fitarb da kungiyar ga duniya gaba daya da kuma gano irin kwakwalwan da shugaban wannan kungiyar yake da shi.

Sannan yakin da kungiyar ta shiga don tallafawa Falasdinawa a Gaza, a ranar 8 ga watan Octoban shekara ta 2023, ya kara fitar da irin karfin da kuma ci gaban da kungiyar Ta tayi, inda a cikin watanni kusan 12 na farkon na yakin ta sami nasara korar yahudawa daga arewacin kasar Falasdinu da aka mamaye, ta lalata na’urorin leken asiri HKI da dama a yankin, sannan ta sami nasar amfani da jiragen yakin leken asirinta mai suna Hud-hud wajen saukar hotunan wurare masu muhimmanci a cikin HKI. Da kuma daga karshe bayan da jiragen yahudan suka sauke ton 85 na makaman a kan gine gine guda 6 wadanda suka tabbatar yana cikinsu, sun kashe Sayyid Hassan nasaralla a ranar 27-ga watan Satumba -2024.

Amma kungiyar ta nuna karfta na makamai masu linzami da kuma makamai wasu wargaza tankunan yaki na mirkava, da kuma halaka sojojin HKI, na tsawon kwanaki 60. Wanda ya tilastawa HKI bukatar a tsagaita wuta., amma ba’a sami damar ya masa da kuma Sayyid shafiyyud deen jana’iza ba sai ranar Lahadi 23-02-2025.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Sayyid Hassan nasaralla sayyid Hassan nasaralla Hassan Nasarallah a kasar Lebanon a shekara ta kungiyar ta da kungiyar

এছাড়াও পড়ুন:

Kamfanonin Waje Sun Ce Dole Ne Su Shiga A Dama Da Su A Cikin Kasuwar Kasar Sin

Yayin taron shekara-shekara na tattaunawar CBD na shekarar 2025 da aka rufe a yau Juma’a 13 ga wata, mashawarci kana kwararre a hukumar kasuwancin kasar Sin ta kasar Birtaniya, kuma shugaban cibiyar bunkasa kasuwanci tsakanin Birtaniya da Sin mista John Mclean, ya bayyana yayin da yake hira da wakilin CMG cewa, kasuwar kasar Sin tana cike da damammaki, don haka dole ne ya shiga a dama da shi a cikinta. A ganinsa, yayin da ake tinkarar tashe-tashen hankula da rashin tabbaci a duniya, babbar baiwar da Sin take da ita, da muhalli mai aminci da bude kofa ga kowa, sun samarwa kamfanonin Birtaniya da ma duniya baki daya damammaki.

Tun bayan kafuwarsa a shekarar 2000 zuwa yanzu, taron ya kasance dandali da kasar Sin ke tattaunawa da kasashen duniya. A yayin taron bana, wakilai fiye da 6000 daga sassan siyasa, da kasuwanci, da ilimi da suka fito daga kasashe da yankuna fiye da 40 sun halarta. A lokacin gudanar da taron, wasu mahalartansa sun yi nuni da cewa, kasar Sin na da babbar juriya wajen raya tattalin arziki, da kuma babbar baiwar raya kasa. Haka kuma, gwamnatin Sin ta gaggauta raya sabon karfin samar da hajoji da hidimomi masu karko, lamarin da ya zuba sabon kuzari ga kamfanonin kasashen waje, ta yadda suke shiga a dama da su wajen yin ciniki a kasar Sin.

A yayin bikin bude taron, mahalartansa sun yi kira da a gina duniya mai tsabta, da kyawu, da dorewa cikin hadin gwiwa, duba da ganin kasar Sin ta ba da babbar gudummawa, ta kuma yi iyakacin kokari a fannin raya kasa ba tare da gurbata muhalli ba, da kuma rage fitar da sinadarin carbon. Alkaluma sun nuna cewa, yanzu haka kasar Sin tana daya daga cikin kasashen da suka fi saurin rage yawan makamashi mai dumama yanayi da suke amfani da shi da samun kyautatuwar iska, ta kuma dasa yawan bishiyoyi, da ciyayi da fadinsu ya kai rubu’i bisa jimillar fadin sabbin bishiyoyi da ciyayi na duniya baki daya, tare da kafa tsarin makamashin da ake sake amfani da shi mafi girma, kuma mafi saurin ci gaba a duniya, baya ga kafa tsarin masana’antu na sabbin makamashi mafi girma kuma cikakke a duniya. (Tasallah Yuan)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •   Iran  Kakkabo Wani Jirgin Yakin HKI Samfurin F-35  Karo Na 3 Tare Da Kama Matukinsa
  • Dimokuradiyya A Shekara 26: Ba Yabo Ba Fallasa
  • Dakarun Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Kakkabo Jiragen Yakin Isra’ila Biyu Kirar F-35
  • Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci
  • Jagora: “Yan Sahayoniya Su Saurari Ukuba Mai Tsanani
  • Kamfanonin Waje Sun Ce Dole Ne Su Shiga A Dama Da Su A Cikin Kasuwar Kasar Sin
  • Leroy Sane ya koma Galatasaray
  • Hamas : Ziyarar ministan Isra’ila Ben-Gvir a masallacin al-Aqsa kan iya tayar da yakin addini
  •   Bokoharam Ta Kashe Sojojin Kamaru Ta Hanyar Amfani Da Jirgin Sama Maras Matuki
  • Kasashen Iran Masar Da Kuma Omman Sun Gudanar Da Taro A Oslo