Ɗan shekara 43 ya auri mai shekara 88
Published: 23rd, February 2025 GMT
Ma’aurata da ke da tazarar shekaru 45 sun shawo kan masu zolayarsu da batun kiwon lafiya don samun farin ciki na musamman a baya kuma sun ce sun ki jin kunyar waɗansu ba su fahimci alakar aurensu ba.
Ma’auratan sun shawo kan matsalar da za ta iya shafan huldarsu da wadanda ke son raba aurensu – amma duk da haka sun nace za su yi iya kokarinsu don hana su farin ciki a rayuwar auren.
Adrián Narbáez, mai shekara 43 yanzu ya hadu da matarsa Delia Lúkuez mai shekara 88, a wani baje kolin fasaha a shekara ta 1998, tun yana dan shekara 16, ita kuma tana da shekara 61.
Da farko, ma’auratan abokai ne kawai, saboda sun hada kai a kan abubuwan da suke so kan kirkirar fasaha.
Malama Delia ta kasance kwararriya mai sha’awar fentin, yayin da Adrián yake son rubutun wakoki da tatsuniyoyi.
Bayan haduwarsu ta farko, Adrián da Delia sun ci gaba da tuntubar juna, suna musayar wasiku, wanda Adrián yake yi har yau.
Yayin da shekaru suka shige, abokantakarsu ta zama soyayya, kuma Adrián, wanda yake jin kamar an haife shi a lokacin da bai dace ba, ya fada wa Delia cewa yana son ta.
Dangantakarsu ta yi danko, amma tsawon wata 12, sun zabi su boye soyayyarsu—suna haduwa lokaci zuwa lokaci.
Ma’auratan, wadanda suke zaune a garin Ribadabia, Mendoza da ke Argentina, sun bi ka’idojin addininsu kuma ba su iya kadaita da juna a wani wuri ba.
Haka kuma sun ta cin karo da kalubale da zarar sun yanke shawarar fitowa fili da soyayyarsu.
Kamar yadda Delia ta bayyana wa manema labarai na gida, ba kowa ne ke farin ciki game da dangantakarsu ba.
Ta bayyana cewa: “Mahaifin mijina ya karbe ni nan da nan, amma mahaifiyarsa ba ta so.”
Adrián, wanda ya ce ya fi son tsofaffin samfuran mota da gidaje, ya kara da cewa: “Zolaya ce, ba su fahimci cewa, duk da bambancin shekaru, za mu iya son junanmu. Da farko, sun yi duk mai yiwuwa domin su raba mu.”
Amma duk da manyan matsalolin da suka fuskanta, kaunar junansu ta yi nasara a karshe.
Adrián, wanda kodayake matashi ne, bai taba sha’awar mata masu irin shekarunsa ba, inda ya bayyana wa kafar yada labarai ta Infobae cewa: “Ban taba jin kunyar bambancin shekarun ba.
“A gaskiya, ban lura da shi ba. Kuma kodayake akwai shekaru 45 a tsakaninmu, ina tafiya tare da ita ko’ina.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Adrián Narbáez
এছাড়াও পড়ুন:
Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
Sanata Sunday Marshall Katung, wanda ke wakiltar mazabar Kaduna ta Kudu a majalisar dattawa, ya sanar da hukuncin da ya yanke na komawa jam’iyyar All Progressives Congress (APC), yana mai cewa wannan mataki ne da ya dace domin inganta aikin wakilci da kuma tabbatar da ƙarin haɗin kai ga al’ummar mazabarsa.
A cikin wata sanarwa mai taken “Sabon Babin Rayuwa: Saƙon Haɗin Kai da Manufa Ɗaya,” Sanata Katung ya bayyana cewa wannan shawara ta biyo bayan dogon shawarwari da aka yi da mazauna mazabarsa, jagororin siyasa, iyalansa da abokan aikinsa.
Ya ce, “Wannan sauyin matsayi yana fitowa ne daga niyyar gaskiya ta yin wa mutanenmu hidima cikin inganci, da tabbatar da cewa muryarmu tana da ƙarfi kuma ana jin ta a manyan teburan yanke shawara da ke tsara makomar al’ummarmu.”
Ya ƙara da cewa wannan mataki ya zama dole ne bayan kiraye-kirayen da aka yi daga sassa daban-daban na mazabarsa, tare da yabawa irin sha’awar da Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, da Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, suka nuna wajen yin aiki tare da shi domin kawo “ci gaba mai tarihi da ban mamaki” a yankin.
Sanata Katung, yayin canza shekan tare da Hon. Daniel Amos da wasu abokansa a Majalisar Dokokin Jihar Kaduna, ya nuna gamsuwa da “ayukan ci gaban” jam’iyyar APC a yankin Kaduna ta Kudu, yana mai cewa suna nuna adalci, daidaito, da ci gaba.
Ya ce, “Zamanin warewa da nuna bambanci, musamman a baya-bayan nan, yana gushewa, kuma ana maye gurbinsa da gwamnatin da ke da manufa da haɗin kai.”
“Saboda haka muna matsawa gaba domin tabbatar da cewa waɗannan nasarori sun dore kuma sun yadu zuwa sauran al’ummomi da dama a yankin,” in ji shi.
Sanatan ya kuma roƙi abokai da abokan aiki da ba su goyi bayan wannan mataki nasa ba, da su mutunta ra’ayoyi daban-daban, tare da kaucewa barin siyasa ta kawo rarrabuwar kawuna a tsakaninsu.
Ya ambaci kalmar Thomas Jefferson da cewa, “Ban taɓa ɗaukar bambanci a ra’ayi na siyasa, addini ko falsafa a matsayin dalilin janye ƙauna daga aboki ba.”
“A tare, mu ci gaba da zama ɗaya a manufa, mu dage da fata, kuma mu mai da hankali wajen samar da makoma mafi kyau ga al’ummar Mazabar Kaduna ta Kudu.”
Sanata Katung ya tabbatar da ƙudurinsa na ci gaba da aiki don haɗin kai da cigaba.
Daniel Karlmax