Kasar Sin Za Ta Zuba Jari A Karamar Hukumar Birnin Kudu
Published: 31st, January 2025 GMT
Karamar Hukumar Birnin kudu ta jihar Jigawa ta bada tabbacin hada kai da duk wata hukuma ko kamfani dake da muradin cigaban yankin.
Shugaban karamar hukumar, Dr. Muhammad Uba Builder ya bada wannan tabbacin lokacin da wakilan rukunin kamfanonin kasar Sin wato China suka ziyarce shi a ofishinsa.
Yace karamar hukumar Birnin kudu tana sahun gaba wajen zaman lafiya da karbar baki a fadin jihar.
Mista Sheng ya shaidawa shugaban karamar hukumar niyyar sa ta kafa kamfanin sarrafa takin zamani a yankin domin bunkasa aikin gona.
Yana mai cewar zai samar da kamfanin yin kujeru da gado da sauran kayayyaki domin bunkasa al’amuran kasuwanci a yankin.
Yace zai kuma samar da sinadarin da zai taimakawa manoma wajen samun amfanin gona mai yawa a lokutan noman rani har ma da na damina.
Wakilinmu ya bamu rahoton cewar, a fanin lafiya kuwa, a zancen da ake yi yanzu, hukumar kula da lafiya matakin farko ta karamar hukumar Birnin kudu da hukumar kula da lafiya ta majalisar dinkin duniya sun yabawa shugaban karamar hukumar bisa kokarinsa na tallafawa al’amuran rigakafi a yankin.
Manajan hukumar Alhaji Bello Abdulkarim wanda ya jagoranci tawagar hukumomin biyu zuwa ofishin shugaban karamar hukumar, ya danganta nasarorin da ake samu bisa hadin kai da goyon bayan shugaban wajen gudanar da ayyukan rigakafi a yankin.
Da yake mai da jawabi, shugaban karamar hukumar Alhaji Muhammad Uba Builder, ya bada tabbacin ci gaba da tallafawa harkokin kiwon lafiya bisa la’akkari da muhimmacin ta.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa Kasar Sin Zuba Jari shugaban karamar hukumar karamar hukumar Birnin
এছাড়াও পড়ুন:
Wasu Yan Ta’adda Sun Kashe Dakarun Sa Kai 2 A Kudu Maso Gabashin Iran
Rahotanni da muka samu sun nuna cew wasu yan ta’adda sun kashe wasu dakarun sa kai guda biyu a kudu masu gabashin iran a yankin sisitan Baluchistan.
Jami’In huda da jama’a na dakarun kare juyi yayi karin harke game da harin da aka kai, yace an kashe mutane ne yayin da suke kokarin ketare da jami’an tsaro suna tafiya akan babbar hanyar da ta hada birnin kashsh dake lardin da kuma babban birnin zahidan
An bayyana cewa wanda abin ya shafa sun hada da Esma’il shavarzi da kuma mukhtar shahouze da kuma wadanda suka samu mummuan rauni a lokacin kai harin
Lardin sistan baluchestan na da iyaka da kasar Pakistan da ya dade yana fuskantar tashe tashen hankula kan fararen hula da kuma jami’an tsaro
Hukumomin yankin sun sha bin asalin tushen irin wadannan hare-hare zuwa cibiyoyin leken asirin na kasashen waje dake nuna goyon bayan yan’ taa’dda dake irin wadannan ayyukan a yankin.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Sojojin Amurka Na Kara Fuskantar Venezuwela Adaidai Lokacin da Trump Ke Musanta Batun Kai Hari November 2, 2025 Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon November 2, 2025 Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya November 2, 2025 Shugaban AmurkaTrump ya yi barazanar daukar matakin soji kan Najeriya November 2, 2025 Kamaru: Jagroan ‘Yan Hamayya Ya Yi Kira Da A Tsayar Da Harkoki A Fadin kasar November 1, 2025 MDD Tana Sa Ido Akan Kashe-kashen Da Ake Yi A Zaben Kasar Tanzania November 1, 2025 Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada November 1, 2025 Shugaban Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini November 1, 2025 Iran ta damu da halin da ake ciki a yankin El Fasher na Sudan November 1, 2025 Kwamitin Tsaron MDD ya goyi bayan shirin Morocco game da yankin Yammacin Sahara November 1, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci