Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-05-01@08:01:13 GMT

Kasar Sin Za Ta Zuba Jari A Karamar Hukumar Birnin Kudu

Published: 31st, January 2025 GMT

Kasar Sin Za Ta Zuba Jari A Karamar Hukumar Birnin Kudu

Karamar Hukumar Birnin kudu ta jihar Jigawa ta bada tabbacin hada kai da duk wata hukuma ko kamfani dake da muradin cigaban yankin.

Shugaban karamar hukumar, Dr. Muhammad Uba Builder ya bada wannan tabbacin lokacin da wakilan rukunin kamfanonin kasar Sin wato China suka ziyarce shi a ofishinsa.

Yace karamar hukumar Birnin kudu tana sahun gaba wajen zaman lafiya da karbar baki a fadin jihar.

Mista Sheng ya shaidawa shugaban karamar hukumar niyyar sa ta kafa kamfanin sarrafa takin zamani a yankin domin bunkasa aikin gona.

Yana mai cewar zai samar da kamfanin yin kujeru da gado da sauran kayayyaki domin bunkasa al’amuran kasuwanci a yankin.

Yace zai kuma samar da sinadarin da zai taimakawa manoma wajen samun amfanin gona mai yawa a lokutan noman rani har ma da na damina.

Wakilinmu ya bamu rahoton cewar, a fanin lafiya kuwa, a zancen da ake yi yanzu, hukumar kula da lafiya matakin farko ta karamar hukumar Birnin kudu da hukumar kula da lafiya ta majalisar dinkin duniya sun yabawa shugaban karamar hukumar bisa kokarinsa na tallafawa al’amuran rigakafi a yankin.

Manajan hukumar Alhaji Bello Abdulkarim wanda ya jagoranci tawagar hukumomin biyu zuwa ofishin shugaban karamar hukumar, ya danganta nasarorin da ake samu bisa hadin kai da goyon bayan shugaban wajen gudanar da ayyukan rigakafi a yankin.

Da yake mai da jawabi, shugaban karamar hukumar Alhaji Muhammad Uba Builder, ya bada tabbacin ci gaba da tallafawa harkokin kiwon lafiya bisa la’akkari da muhimmacin ta.

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa Kasar Sin Zuba Jari shugaban karamar hukumar karamar hukumar Birnin

এছাড়াও পড়ুন:

Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok

Mayaƙan ƙungiyar Boko Haram sun kashe masu zaman makoki bakwai tare da jikkata wasu a ƙauyen Kopl da ke Ƙaramar Hukumar Chibok ta Jihar Borno.

Shugaban Karamar Hukumar, Honorabul Modu Mustapha, ya ce mayaƙan sun buɗe wa mutanen wuta ne a yammacin ranar Litinin, a yayin da suke shirin gudanar da addu’o’i ga ’yan uwansu da suka rasu.

Ya ce, “Sun taru ne domin yin addu’a lokacin da ’yan ta’addan suka sauka a kansu. Mun kwashe mutane da yawa da suka samu raunukan harsashi zuwa Babban Asibitin Mubi da ke maƙwabtaka da Jihar Adamawa.

“Adadin waɗanda suka mutu na iya ƙaruwa, saboda wasu sun tsere cikin daji da raunukan harsashi. Ana ci gaba da aikin nemowa da ceto waɗanda ke cikin daji,” in ji shi.

Bom ɗin Boko Haram ya kashe mutane 26 a Borno NAJERIYA A YAU: Dalilin karyewar farashin shinkafa a kasuwannin Najeriya Shugaban Majalisar Ƙoli ta Shari’ar Musulunci a Najeriya ya rasu

Sanatan Borno ta Kudu, Ali Ndume, ya ci gaba da yin Allah wadai da hare-haren, inda ya bayyana halin da ake ciki a matsayin abin da ya wuce tunanin dan Adam.

“Ko jiya ma, na samu kiran gaggawa cewa an kashe sama da ’yan banga 10 a wani yankin da ke tsakanin Karamar Hukumar Hawul ta Jihar Borno da garin Garkida a Jihar Adamawa.

“Al’ummata na fama da munanan asara ba tare da wani faɗa ba. A cikin wata guda da ya gabata kaɗai, an kashe sama da mutum dari a hare-hare da dama yankunan Sabon Gari da Izge da Kirawa da Pulka da Damboada Chibok da Askira Uba da wasu da yawa da ba zan iya lissafawa ba,” in ji Sanata Ndume.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Syria: Adadin Wadanda Aka Kashe A Rikicin Bangaranci Sun Kai 70
  • Tsoffin ma’aikatan NECO na neman a biya su bashin haƙƙoƙinsu
  • NEMA Ta Karɓi ‘Yan Nijeriya 203 Da Suka Maƙale A Libya
  • Za A Yi Allurar Rigakafi Ga Dabbobi Sama Da Miliyan Daya A Babura
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kutsa Cikin Quneitra Na Kasar Siriya Tare Da Kafa Shingen Bincike
  • Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China
  • Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok
  • Hajjin 2025: An Fara Yi Wa Maniyyata Allurar Rigakafi A Jigawa
  • Shugaban Kasar Yana Maraba Da Masu Zuba Hannun Jari A Kasarsa Daga Kasashen Waje
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Tattauana Da Shugaban Hukumar IAEA