Sharhin Bayan Labarai: Masar Ta Ki Amincewa Da Komarwa Falasdinawan Gaza Zuwa Kasarsa
Published: 29th, January 2025 GMT
Assalamu alaikum masu sauraro, sharhin bayan labarammu zai yi magana dangane da rashin amincewar kasashen masar da Jordan kan maida Falasdnawa cikin kasashensu wanda ni tahir amin zan karanta.
A makon da ya gabata ne shugaban kasar Amurka Donal Trump ya fadawa kafafen yada labarai a lokacinda yake cikin jirgin fadar shugaban kasa ko ‘Air Force 1, kan cewa yana duba yiyuwar kwasar Falasnidawa a Gaza zuwa kasar Masar sannan sauran falasdinawa a yankin yamma da kogin Jordan da kuma sauran wurare a kasar Falasdinu da aka mamaye zuwa kasar Jordan.
Wannan zancen dai ba sabuwa bace, a rikicin gabas ta tsakiya, shuwagabanin Amurka a baya, sun yi wannan maganar amma bata yuba.
A halin yanzun babu wata kasa, ya zuwa yanzu a duniya, wacce take goyon bayan ra’ayin shugaba Trump a kan wannan tunanin.
Shugaban kasar Masar Abdulfattah Assisi a wani jawabin da ya gabatar ya bayyana cewa kasarsa ba zata taba amincewa da kaurar Falasdinawa zuwa kasarsa ba, don yin haka zalunci ne a fili, banda haka hatsari ne ga kasar masar kanta.
Gwamnatin kasar Jordan ma ta ki amincewa da hakan, banda haka rikicin gabas ta tsakiya ta zama rikici ne wanda yake girgiza dangantaka tsakanin kasashen yankin da ma, tsakanin sauran kasashen duniya. Har iyala yau rikicin zai tama dokokin kasa da kasa kan al-amura da dama. Daga cikin har da dokokin kasa da kasa, wadanda suka yi magana dangane da yencin zama dan wata kasa, da kuma yadda kasashen duniya suke daukar mutane a tsakaninsu.
A halin yanzu miliyoyin Falasdinawa suna rayuwa a kasashen Jordan, Siriya da Lebanon da Masar, da ma wasu kasashe a duniya. Wadannan a saryar da hakkinsu na komawa kasarsu ta asali, a inda ba’a dauke su yan kasa ba. Suna rayuwa a sansanonin yan gudun hijira fiye da shekaru 76. Akwai wata al-umma wacce aka zalunta a doron kasa kamar Falasdinawa?.
Banda haka maida Falasdinawa zuwa kasashen Masar da Jordan, don tabbatarwa yahudawan sahyoniyya kasar Falasdinu, zai tabbatar da rashin adalcin gwamnatin Amurlka a fili. Duk da cewa tana ci gaba da zaluntar Falasniya tun da dadewa ta bayan fage sannan a zahri wasu lokuta. Sai dai a wannan fagen kowa a duniya sai ya fahinci hakan.
Banda haka wannan zai jawa matsalar yan gudun hijira a kasashe daban daban na duniya, misali yan gudun hijira na Rohinga, sai a ce dole su koma kasar Bagladesh don su musulmi ne, alhali su yan kasar Myanmar ne, al’adarsyu ta mutanen myan marne kuma harshensu harshen myan mar ne.
Daon haka wannan ra’ayin idan ya tabbata zai rikita al-amuran zamantakewa a kasashen duniya da dama, musamman inda ake da yan gudun hijira.
Shugaban Assisi a jawabinsa ya bayyana cewa, gwamnatin kasarsa tana ganin hanyar warware wannan matsalar itace samar da kasashe biyu a kasar Falasdinu, kuma zata taimaka don tabbatar da hakan.
Kasashen larabawa gaba daya, tun da dadewa sun fitar da batun zaman Falasdnbiawa a wasu kasashen larabawa ko kuma wani wuri daban, suna ganin dole ne a maidasu kasaru ko ba dade ko ba jima.
Sai dai dangane da samar da kasashe biyu wanda wasu kasashen larabawa suke ganin cewa itace hanya tilo wajen warware wannan matsalan. Da farko su yahudawan da suka mamaye kasar Falasdinu shekaru fiye da 70 da suka gabata basu amince da haka ba, banda haka suna ma neman kara kwace wasu kasashen larabawa makobta da su don kara yawan kasar da suka mamaye. Sannan Falasdinawa masu asalin kasa basu amince da haka. Sun ganin kasar Falasdinu ta Falasdinawa ne daga tekun medeteranin har zuwa gogin Jordan.
Don haka idan har wadanda ake magana a kansu gaba daya basu amince da haka ba, to ra’ayin samar da kasashen biyu a kan kasar Falasdinu da aka mamaye ma, tilastawa mutanen biyu abinda ba ra’ayinsu bane.
Yanzu dai sai mu jira mu gani abinda Trump zai yi don tabbatar da ra’ayinsa.
Masu sauraro karshen sharhin bayan labaran Kenan.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasashen larabawa yan gudun hijira kasar Falasdinu wasu kasashe
এছাড়াও পড়ুন:
Duniya na tir da sabon farmakin Isra’ila kan Gaza
Kasashen duniya na ci gaba da yin tir da sabon farmakin soji da Isra’ila ta kaddamar kan Gaza.
Kasashen Biritaniya, Faransa, Italiya, Masar, Jordan, Qatar, Spain, duk sun yi tir da farmakin kan Gaza suna masu cewa zai kara dagula halin kunci da ake ciki.
Kungiyar tarayyar Turai, ta bakin Jami’ar kula da harkokin wajen ta, Kaja Kalas, ta yi kira da a sanyawa Isra’ila takunkumi domin matsa wa gwamnatin lamba ta kawo karshen hare-haren da take kaiwa Gaza, tana mai gargadin cewa al’amuran jin kai na kara ta’azzara.
“Hare-haren da Isra’ila ta kai a Gaza zasu haifar da mummunan sakamako game da halin da ake ciki da karin hasarar rayuka, da barna & hijira na jama’a,” in ji Kalas a kan X.
A jiya ne Sojojin Isra’ila suka kaddamar da sabon farmakin ta kasa mai manufar mamaye birnin Gaza bayan shafe makwanni ana kai hare-haren bama-bamai ba kakkautawa ba a kan wasu manyan gine-gine domin tilastawa Falasdinawa kauracewa gidajensu.
Farmakin ya zo ne jim kadan bayan da sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio ya gana da firaminista Benjamin Netanyahu a kusa da masallacin Al Aqsa da ke gabashin birnin Kudus da aka mamaye.
Tun da farko dai, wakiliyar Majalisar Dinkin Duniya ta musamman kan yankunan Falasdinawa da ke mamaye, Francesca Albanese ta yi Allah wadai da hare-haren da Isra’ila ke kai wa birnin Gaza, tana mai cewa wani bangare ne na shirin Isra’ila na shafe Gaza.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran da Saudiyya sun bukaci hadin Musulmi game da halin da ake ci a yankin September 17, 2025 Akalla Falasdinawa 78 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila a Gaza September 17, 2025 Akalla Falsdinawa 78 Ne Suka Yi Shahada A Yau A Gaza. September 16, 2025 Isra’ila Ta Kai Hari A Tashar Jirgin Ruwan Hudaida Dake Yamen September 16, 2025 Iran Ta Gabatar Da Sabbin Kayayyaki 5 A Wajen Taron kere-kere . September 16, 2025 Iran Ta Bukaci IAEA Tayi Tir Da Harin Da Isra’ila Ta Kai A Tashoshin Nukiyarta. September 16, 2025 Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana September 16, 2025 Pezeshkian: Saudiyya Na Iya Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Samar Da Hadin Kan Kasashen Musulmi September 16, 2025 Pezeshkian: Ta’addancin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Kan Kasar Qatar Zalunci Ne Ga Diflomasiyya September 16, 2025 Baqa’i: Kowace Kasa A Duniya Tana Da Hakkin Mallakar Makamashin Nukiliya Na Zaman Lafiya September 16, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci