Sharhin Bayan Labarai: Masar Ta Ki Amincewa Da Komarwa Falasdinawan Gaza Zuwa Kasarsa
Published: 29th, January 2025 GMT
Assalamu alaikum masu sauraro, sharhin bayan labarammu zai yi magana dangane da rashin amincewar kasashen masar da Jordan kan maida Falasdnawa cikin kasashensu wanda ni tahir amin zan karanta.
A makon da ya gabata ne shugaban kasar Amurka Donal Trump ya fadawa kafafen yada labarai a lokacinda yake cikin jirgin fadar shugaban kasa ko ‘Air Force 1, kan cewa yana duba yiyuwar kwasar Falasnidawa a Gaza zuwa kasar Masar sannan sauran falasdinawa a yankin yamma da kogin Jordan da kuma sauran wurare a kasar Falasdinu da aka mamaye zuwa kasar Jordan.
Wannan zancen dai ba sabuwa bace, a rikicin gabas ta tsakiya, shuwagabanin Amurka a baya, sun yi wannan maganar amma bata yuba.
A halin yanzun babu wata kasa, ya zuwa yanzu a duniya, wacce take goyon bayan ra’ayin shugaba Trump a kan wannan tunanin.
Shugaban kasar Masar Abdulfattah Assisi a wani jawabin da ya gabatar ya bayyana cewa kasarsa ba zata taba amincewa da kaurar Falasdinawa zuwa kasarsa ba, don yin haka zalunci ne a fili, banda haka hatsari ne ga kasar masar kanta.
Gwamnatin kasar Jordan ma ta ki amincewa da hakan, banda haka rikicin gabas ta tsakiya ta zama rikici ne wanda yake girgiza dangantaka tsakanin kasashen yankin da ma, tsakanin sauran kasashen duniya. Har iyala yau rikicin zai tama dokokin kasa da kasa kan al-amura da dama. Daga cikin har da dokokin kasa da kasa, wadanda suka yi magana dangane da yencin zama dan wata kasa, da kuma yadda kasashen duniya suke daukar mutane a tsakaninsu.
A halin yanzu miliyoyin Falasdinawa suna rayuwa a kasashen Jordan, Siriya da Lebanon da Masar, da ma wasu kasashe a duniya. Wadannan a saryar da hakkinsu na komawa kasarsu ta asali, a inda ba’a dauke su yan kasa ba. Suna rayuwa a sansanonin yan gudun hijira fiye da shekaru 76. Akwai wata al-umma wacce aka zalunta a doron kasa kamar Falasdinawa?.
Banda haka maida Falasdinawa zuwa kasashen Masar da Jordan, don tabbatarwa yahudawan sahyoniyya kasar Falasdinu, zai tabbatar da rashin adalcin gwamnatin Amurlka a fili. Duk da cewa tana ci gaba da zaluntar Falasniya tun da dadewa ta bayan fage sannan a zahri wasu lokuta. Sai dai a wannan fagen kowa a duniya sai ya fahinci hakan.
Banda haka wannan zai jawa matsalar yan gudun hijira a kasashe daban daban na duniya, misali yan gudun hijira na Rohinga, sai a ce dole su koma kasar Bagladesh don su musulmi ne, alhali su yan kasar Myanmar ne, al’adarsyu ta mutanen myan marne kuma harshensu harshen myan mar ne.
Daon haka wannan ra’ayin idan ya tabbata zai rikita al-amuran zamantakewa a kasashen duniya da dama, musamman inda ake da yan gudun hijira.
Shugaban Assisi a jawabinsa ya bayyana cewa, gwamnatin kasarsa tana ganin hanyar warware wannan matsalar itace samar da kasashe biyu a kasar Falasdinu, kuma zata taimaka don tabbatar da hakan.
Kasashen larabawa gaba daya, tun da dadewa sun fitar da batun zaman Falasdnbiawa a wasu kasashen larabawa ko kuma wani wuri daban, suna ganin dole ne a maidasu kasaru ko ba dade ko ba jima.
Sai dai dangane da samar da kasashe biyu wanda wasu kasashen larabawa suke ganin cewa itace hanya tilo wajen warware wannan matsalan. Da farko su yahudawan da suka mamaye kasar Falasdinu shekaru fiye da 70 da suka gabata basu amince da haka ba, banda haka suna ma neman kara kwace wasu kasashen larabawa makobta da su don kara yawan kasar da suka mamaye. Sannan Falasdinawa masu asalin kasa basu amince da haka. Sun ganin kasar Falasdinu ta Falasdinawa ne daga tekun medeteranin har zuwa gogin Jordan.
Don haka idan har wadanda ake magana a kansu gaba daya basu amince da haka ba, to ra’ayin samar da kasashen biyu a kan kasar Falasdinu da aka mamaye ma, tilastawa mutanen biyu abinda ba ra’ayinsu bane.
Yanzu dai sai mu jira mu gani abinda Trump zai yi don tabbatar da ra’ayinsa.
Masu sauraro karshen sharhin bayan labaran Kenan.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasashen larabawa yan gudun hijira kasar Falasdinu wasu kasashe
এছাড়াও পড়ুন:
Tawagar Iran Ta Fice A Taron Majalisun Dokokin Kasashen Duniya A Lokacin Jawabin Wakilin Isra’ila
Tawagar Iran ta fice daga taron majalisun dokokin kasashen duniya kafin fara jawabin jami’in gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila a zaman taron
A wata gagarumar nuna rashin amincewa da tushen zaluncin da ya addabi duniya, tawagogin kasashen Iran, Yemen, da Falasdinu sun fice daga zaman taron Majalisar Dinkin Duniya a Geneva, bayan da shugaban majalisar dokokin Isra’ila “Knesset” zai fara gabatar da jawabinsa mai kunshe da bayanai neman tunzura jama’a, wanda kuma bayanai suka haifar da cece-kuce a tsakanin wadanda suka zauna suka saurara.
A cikin jawabin shugaban majalisar dokokin Isra’ila “Knesset” ya bayyana cewa; Akwai yiwuwar samar da ‘yantacciyar kasar Falasdinu a wajen yankunan Falasdinu, musamman a biranen London da Paris na kasashen Birtaniya da Faransa.
Wannan matakin na nuna rashin amincewa da yadda yahudawan sahayoniyya suke adawa tare da yin watsi da hakikanin samuwar Falasdinawa da kuma kokarin tauyaye hakkin al’ummar Falasdinu.
Shugaban majalisar dokokin kasar Iran Mohammad Baqir Qalibaf ne ya jagoranci tawagar ‘yan majalisun dokokin kasar Iran zuwa wajen taron da ya hada shugabannin majalisun dokokin duniya karo na shida a birnin Geneva na kasar Switzerland.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kasar Iran Ta Bayyana Gushewar Hasashen Raunin Karfin Sojinta Kuma Ba Zai Dawo Ba July 31, 2025 Sojan Amurka Ya Bada Ruwayar Yadda Sojojin Sahayoniyya Suka Kashe Wani Yaro Balasdine July 31, 2025 Sojojin Yemen Sun Kai Zafafan Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila Guda Uku July 31, 2025 Qolibaf: Barin HKI Ta Yi Abinda Taga Dama Ne Yana Karfafa Mata Giwa July 30, 2025 Yunwa Ta Kashe Karin Falasdinawa 7 A Gaza July 30, 2025 Malta Zata Amince da Samuwar Falasdinu a Cikin Watan Satumba Mai Zuwa July 30, 2025 Amurka Ta Ce HKI Ba Zata Fice Daga Kasar Lebanon Ba Sai An Kwance Damarar Hizbullah July 30, 2025 Siriya Da HKI Zasu Gudanar Da Taro A Baku July 30, 2025 Girgizar Kasa Mai Karfi Ta Kada Yankin Kamtashatka Na Kasar Rasha July 30, 2025 Yahudawa ‘Yan Share Wuri Zauna Sun Kutsa Cikin Masallacin Kudus July 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci