Sharhin Bayan Labarai: Masar Ta Ki Amincewa Da Komarwa Falasdinawan Gaza Zuwa Kasarsa
Published: 29th, January 2025 GMT
Assalamu alaikum masu sauraro, sharhin bayan labarammu zai yi magana dangane da rashin amincewar kasashen masar da Jordan kan maida Falasdnawa cikin kasashensu wanda ni tahir amin zan karanta.
A makon da ya gabata ne shugaban kasar Amurka Donal Trump ya fadawa kafafen yada labarai a lokacinda yake cikin jirgin fadar shugaban kasa ko ‘Air Force 1, kan cewa yana duba yiyuwar kwasar Falasnidawa a Gaza zuwa kasar Masar sannan sauran falasdinawa a yankin yamma da kogin Jordan da kuma sauran wurare a kasar Falasdinu da aka mamaye zuwa kasar Jordan.
Wannan zancen dai ba sabuwa bace, a rikicin gabas ta tsakiya, shuwagabanin Amurka a baya, sun yi wannan maganar amma bata yuba.
A halin yanzun babu wata kasa, ya zuwa yanzu a duniya, wacce take goyon bayan ra’ayin shugaba Trump a kan wannan tunanin.
Shugaban kasar Masar Abdulfattah Assisi a wani jawabin da ya gabatar ya bayyana cewa kasarsa ba zata taba amincewa da kaurar Falasdinawa zuwa kasarsa ba, don yin haka zalunci ne a fili, banda haka hatsari ne ga kasar masar kanta.
Gwamnatin kasar Jordan ma ta ki amincewa da hakan, banda haka rikicin gabas ta tsakiya ta zama rikici ne wanda yake girgiza dangantaka tsakanin kasashen yankin da ma, tsakanin sauran kasashen duniya. Har iyala yau rikicin zai tama dokokin kasa da kasa kan al-amura da dama. Daga cikin har da dokokin kasa da kasa, wadanda suka yi magana dangane da yencin zama dan wata kasa, da kuma yadda kasashen duniya suke daukar mutane a tsakaninsu.
A halin yanzu miliyoyin Falasdinawa suna rayuwa a kasashen Jordan, Siriya da Lebanon da Masar, da ma wasu kasashe a duniya. Wadannan a saryar da hakkinsu na komawa kasarsu ta asali, a inda ba’a dauke su yan kasa ba. Suna rayuwa a sansanonin yan gudun hijira fiye da shekaru 76. Akwai wata al-umma wacce aka zalunta a doron kasa kamar Falasdinawa?.
Banda haka maida Falasdinawa zuwa kasashen Masar da Jordan, don tabbatarwa yahudawan sahyoniyya kasar Falasdinu, zai tabbatar da rashin adalcin gwamnatin Amurlka a fili. Duk da cewa tana ci gaba da zaluntar Falasniya tun da dadewa ta bayan fage sannan a zahri wasu lokuta. Sai dai a wannan fagen kowa a duniya sai ya fahinci hakan.
Banda haka wannan zai jawa matsalar yan gudun hijira a kasashe daban daban na duniya, misali yan gudun hijira na Rohinga, sai a ce dole su koma kasar Bagladesh don su musulmi ne, alhali su yan kasar Myanmar ne, al’adarsyu ta mutanen myan marne kuma harshensu harshen myan mar ne.
Daon haka wannan ra’ayin idan ya tabbata zai rikita al-amuran zamantakewa a kasashen duniya da dama, musamman inda ake da yan gudun hijira.
Shugaban Assisi a jawabinsa ya bayyana cewa, gwamnatin kasarsa tana ganin hanyar warware wannan matsalar itace samar da kasashe biyu a kasar Falasdinu, kuma zata taimaka don tabbatar da hakan.
Kasashen larabawa gaba daya, tun da dadewa sun fitar da batun zaman Falasdnbiawa a wasu kasashen larabawa ko kuma wani wuri daban, suna ganin dole ne a maidasu kasaru ko ba dade ko ba jima.
Sai dai dangane da samar da kasashe biyu wanda wasu kasashen larabawa suke ganin cewa itace hanya tilo wajen warware wannan matsalan. Da farko su yahudawan da suka mamaye kasar Falasdinu shekaru fiye da 70 da suka gabata basu amince da haka ba, banda haka suna ma neman kara kwace wasu kasashen larabawa makobta da su don kara yawan kasar da suka mamaye. Sannan Falasdinawa masu asalin kasa basu amince da haka. Sun ganin kasar Falasdinu ta Falasdinawa ne daga tekun medeteranin har zuwa gogin Jordan.
Don haka idan har wadanda ake magana a kansu gaba daya basu amince da haka ba, to ra’ayin samar da kasashen biyu a kan kasar Falasdinu da aka mamaye ma, tilastawa mutanen biyu abinda ba ra’ayinsu bane.
Yanzu dai sai mu jira mu gani abinda Trump zai yi don tabbatar da ra’ayinsa.
Masu sauraro karshen sharhin bayan labaran Kenan.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasashen larabawa yan gudun hijira kasar Falasdinu wasu kasashe
এছাড়াও পড়ুন:
A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?
Duk da cewa suna da karfi a fannin aikin soja, amma harinsu zai zama tamkar amfani da igwa ne wajen kashe sauro. Duk wani fifikon da suke da shi ba zai dore ba. Saboda haka, a zahiri wannan tambayar da wani mai amfani da yanar gizo ya yi, ta nuna rashin hankali cikin kalaman shugaban Amurka.
Sai dai kalaman sun dace da halayya, da salon musamman na shugaba Donald Trump. Wani lokaci, da gangan ya kan yi amfani da kalmomi, da aikace-aikace marasa ma’ana wajen samar da yanayi na rashin tabbas, ta yadda zai samu damar matsawa wani lamba, don tilasta masa ya yi wani aiki. Wannan dabara ce da wasu masanan kasar Amurka ke kira da “ka’idar mahaukaci”, watakila ta dace da halayyar shugaba Trump, abun da ya sa yake ta amfani da ita wajen kula da harkokin waje.
Kana wannan batu na yin barazanar kai hari ya dace da halayyar kasar Amurka. Kasa ce wadda ba ta mai da hankali a kan neman gano gaskiya ba, balle ma la’akari da bayanan da Nijeriya ta gabatar dangane da zargin da aka yi mata. Kai tsaye an yi fatali da ikon mulkin kai na Najeriya, da dokokin kasa da kasa, da ra’ayoyin kasashen yankin da ake ciki. A ganin kasar Amurka, tana iya tsoma baki a duk wani aiki, da aikata yadda ta ga dama, kuma idan za ta iya yin amfani da karfin tuwo wajen tilasta wani, to ba za ta taba tattaunawa da shi ba. Kawai kasar tana kokarin aiwatar da mulkin danniya ne a duniya.
Amma, a cewar wasu masana, “ka’idar mahaukaci” ba ko yaushe take yin tasiri ba. Saboda idan wani ya dade yana kwaikwayon mahaukaci, to, ba za a ci gaba da tsoronsa ba. Kana mulkin danniya na kasar Amurka shi ma ba zai dore ba, idan aka yi la’akari da yadda kasashe masu tasowa ke tasowa cikin sauri a zamanin da muke ciki.
Ko ta yaya ya kamata Amurka ta daidaita kalamanta da ayyukanta? Kuma ta wace hanya ya kamata kasashe daban daban su yi mu’ammala da juna?
Na farko, ya kamata mu tabbatar da daidaito tsakanin mabambanta kasashe, da kuma bin dokokin kasa da kasa. Na biyu, ya kamata mu daukaka ra’ayin kasancewar bangarori masu fada-a-ji da yawa a duniya, da neman daidaita harkoki ta hanyar yin shawarwari, maimakon tayar da rikici. Na uku, ya kamata mu dora muhimmanci kan jin dadin jama’a, ta yadda ba za a tsaya ga kula da mutanen gida kadai ba, wato a hada da al’ummun sauran kasashe. Ya kamata a lura da hakkinsu da bukatunsu. Wadannan abubuwa suna cikin shawarar da kasar Sin ta gabatar, dangane da inganta jagorancin duniya.
Watakila kasar Amurka ba ta yarda da wadannan ka’idoji ba tukuna, amma tabbas wata rana za ta amince da su. (Bello Wang)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA