Masu Zanga-zanga Sun Farmawa Ofisoshin Jakadancin Amurka Da Na Faransa A DR Congo
Published: 29th, January 2025 GMT
Masu zanga-zanga sun kai hari kan ofisoshin jakadancin kasashen waje da dama hari a Kinshasa, babban birnin Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo (DRC).
An bayar da rahoton cewa, fusatattun masu zanga-zangar sun kai wa ofisoshin jakadancin Amurka, Faransa, Belgium, Rwanda, Uganda, Kenya da Afirka ta Kudu hari.
Masu zanga-zangar dai na neman hadin kan kasashen waje da yunkurin kasa da kasa na shiga tsakani na soji da kuma dakatar da ‘yan tawayen M23 da ke ci gaba da mamaye wasu sassan yankin gabashi.
‘Yan sanda sun harba barkonon tsohuwa amma masu zanga-zangar sun samu damar shiga sassan harabar, inda suka yi banka wuta.
Rikicin da aka kwashe shekaru da dama ana yi da kungiyar ta M23 ya yi Kamari a baya bayan nan, inda suka kwace iko da Goma babban birnin gabashin Congo, ko da yake rundunar sojin Congon ta ce har yanzu tana iko da kashi 80 na birnin.
Masu zanga-zangar a Kinshasa sun bukaci kasashen duniya su matsa lamba kan kasar Rwanda kan ci gaban da dakarun ‘yan tawayen suka yi.
Tashin hankali a yankin da ake fama da rikicin kabilanci ya haifar da daya daga cikin manyan matsalolin jin kai a duniya.
A shekara ta 2012, ‘yan tawayen M23 sun mamaye birnin na Goma na wani dan lokaci kafin a tilasta musu janye dakarunsu a karkashin matsin lamba daga kasashen duniya.
A shekara ta 2021, dakarun ‘yan tawayen sun sake haduwa bisa tallafin da suke samu daga kasar Rwanda, a cewar gwamnatin Kinshasa da kwararrun MDD, saidai gwamnatin Kigali na mai musanta hakan.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Masu zanga zangar
এছাড়াও পড়ুন:
MDD za ta yi zaman gaggawa kan yunƙurin ƙwace Gaza
Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya kira taron gaggawa a wannan Lahadin domin tattauna ƙudirin Isra’ila na ƙwace iko da Zirin Gaza.
Wannan shirin, wanda Majalisar Tsaron Isra’ila ta amince da shi a ranar Juma’a, ya jawo suka daga ƙasashen duniya.
Al-Hilal ta ɗauki Nunez daga Liverpool Sojoji sun kashe Kwamandan Boko Haram a BornoSakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya, António Guterres ya kwatanta shirin da abin da zai ƙara dagula lamura a fadan da aka kwashe watanni 22 ana yi.
Kasashen Turai da ke cikin Kwamitin Sulhun da suka hada da Denmark da Faransa da Girka da Burtaniya da Slovenia ne suka kira wannan zaman gaggawan a birnin New York na Amurka.
DW ya ruwaito cewa, dukkan mambobin Kwamitin Sulhun banda Amurka sun goyi bayan wannan zaman na yau Lahadi wanda zai dubi abinda ya dace a yi a kan yunkurin na Isra’ila.
Za a fara zaman ne da misalin ƙarfe 10 na safe wato ƙarfe biyu kenan agogon GMT da Ghana.