HausaTv:
2025-10-14@11:52:27 GMT

Masu Zanga-zanga Sun Farmawa Ofisoshin Jakadancin Amurka Da Na Faransa A DR Congo

Published: 29th, January 2025 GMT

Masu zanga-zanga sun kai hari kan ofisoshin jakadancin kasashen waje da dama hari a Kinshasa, babban birnin Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo (DRC).

An bayar da rahoton cewa, fusatattun masu zanga-zangar sun kai wa ofisoshin jakadancin Amurka, Faransa, Belgium, Rwanda, Uganda, Kenya da Afirka ta Kudu hari.

Masu zanga-zangar dai na neman hadin kan kasashen waje da yunkurin kasa da kasa na shiga tsakani na soji da kuma dakatar da ‘yan tawayen M23 da ke ci gaba da mamaye wasu sassan yankin gabashi.

‘Yan sanda sun harba barkonon tsohuwa amma masu zanga-zangar sun samu damar shiga sassan harabar, inda suka yi banka wuta.

Rikicin da aka kwashe shekaru da dama ana yi da kungiyar ta M23 ya yi Kamari a baya bayan nan, inda suka kwace iko da Goma babban birnin gabashin Congo, ko da yake rundunar sojin Congon ta ce har yanzu tana iko da kashi 80 na birnin.

Masu zanga-zangar a Kinshasa sun bukaci kasashen duniya su matsa lamba kan kasar Rwanda kan ci gaban da dakarun ‘yan tawayen suka yi.

Tashin hankali a yankin da ake fama da rikicin kabilanci ya haifar da daya daga cikin manyan matsalolin jin kai a duniya.

A shekara ta 2012, ‘yan tawayen M23 sun mamaye birnin na Goma na wani dan lokaci kafin a tilasta musu janye dakarunsu a karkashin matsin lamba daga kasashen duniya.

A shekara ta 2021, dakarun ‘yan tawayen sun sake haduwa bisa tallafin da suke samu daga kasar Rwanda, a cewar gwamnatin Kinshasa da kwararrun MDD, saidai gwamnatin Kigali na mai musanta hakan.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Masu zanga zangar

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Takunkumin Da Amurka Ta Sanyawa Masana’antunta 

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Yanayin Sashen Samar Da Gidaje Na Sin Ya Kara Inganta Tsakanin 2021 Zuwa 2025 October 11, 2025 Daga Birnin Sin Tarihin Hassan Usman Katsina (1) October 11, 2025 Daga Birnin Sin An Gudanar Da Taron Hadin Kai Na Raya Albarkatun Kasa Tsakanin Sin Da Mozambique October 11, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Gudanar Gagarumar Zanga Zangar Goyon Bayan Falasdinawa A Australia Da Indonasia
  • Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba
  • Ana Gudanar Da Taron Masu Mukamin Magajin Gari Na Kasa Da Kasa A Birnin Dunhuang Na Sin
  • Shugaban Amurka Ya Yi Barazanar Aikewa Ukraine Makamai Masu Linzami Kirar Tomahawk
  • Wata Kotu a Faransa ta yi watsi da rufe wata makarantar musulmi a birnin Nice  
  • Rashin Amincewa Da Kasashen Yamma Yana Haifar Da Sabon Tunani Kan Huldar Kasa Da Kasa
  • An Yi Musayar Wuta A Tsakanin Masu Tsaron Iyakokin Kasashen Afghanistan Da Pakistan
  • Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Takunkumin Da Amurka Ta Sanyawa Masana’antunta 
  • Sarkin Morocco Ya yi Magana Tun Bayan Barkewar Zanga-zanga A Kasar .
  • Li Qiang Ya Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Koriya Ta Arewa