UNICEF Ya Kara Jan Hankalin Gwamnatin Najeriya Game Da Ilimin ‘Ya’ya Mata
Published: 27th, January 2025 GMT
Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya, UNICEF, ya bukaci gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki da su kara himma wajen yara mata na samun damar yin karatu.
Shugaban ofishin UNICEF na Kano, Mista Rahama Farah, ne ya yi wannan kiran a Kano a wani taron manema labarai na bikin ranar ilimi ta duniya ta 2025.
Ya kara da cewa alkaluma sun nuna cewa ‘yan mata miliyan 7 da 600 ba sa zuwa makaranta, inda shiyyar Arewa maso Yamma da arewa maso gabas ke da kashi 48 cikin 100 na adadin.
Ya danganta wannan kididdigar da abubuwan da suka hada da talauci da ka’idojin zamantakewa da nuna wariyar jinsi, wadanda ke dakile bai wa ‘ya’ya mata damar samun ilimi.
A lokacin da yake gabatar da bitar ayyukan UNICEF na inganta karatun yara mata da kuma ci gaba da karatu, shugaban ofishin kula da kananan yara na jihar Kano, Rahama Mohammed Farah, ya ce asusun ya samu hadin gwiwa da gwamnati da al’umma wajen magance matsalolin.
Ya ce UNICEF ta kuma yi amfani da tallafin kudi da sauran abubuwan karfafa gwiwa don karfafawa iyaye gwiwa, su yi rajistar ‘ya’yansu mata da tabbatar da ganin sun ci gaba da zuwa makaranta.
Ya yi bayanin cewa, “UNICEF ya yi kokari matuka a wannan fanni, ciki har da bayar da kudade domin karfafa musu gwiwa wajen tura ‘ya’yansu mata zuwa makaranta tare da tallafa musu zuwa matakin sakandare”.
Ya yi bayanin yadda asusun ya ke inganta fasahar rubutu da karatun ‘ya’ya mata ta hanyar cibiyoyin karatun ‘yan mata don ‘yan mata (G4G), inda kimanin ‘yan mata da ke zuwa makaranta miliyan 2 da 600 su ke samun ilimi ta hanyoyin sadarwa da suka hada da rediyo da talabijin a hakin yanzu.
“UNICEF ya kuma inganta kwazon malamai don ilmantar da ‘ya’ya mata, tare da kara yawan malamai a makarantun firamare 42,000“, inji Farah.
Ya yi bayanin cewa UNICEF ya kuma gina tare da gyara wuraren tsaftar ruwa a makarantu 33 a fadin jihohin Kano da Jigawa, wadanda ‘yan mata 19,622 ke amfani da su.
Ya ce asusun yana kuma aiki tare da masu tsara manufofi a fannin ilimi don tabbatar da ingantacciyar kariya ga yara da ayyukan makaranta ga yara mata, yayin da kuma yana inganta kwazon malamai da za su jagoranci yara mata.
Taron manema labaran ya samu halartar ‘yan jaridu daga jihohin Kano, da Jigawa da Katsina.
Usman Mohammed da Isma’il Adamu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Qolibaf: Barin HKI Ta Yi Abinda Taga Dama Ne Yana Karfafa Mata Giwa
Kakakin majalisar dokokin kasar Iran Mohammad Baqir Qalibaf ya bayyana cewa kyale HKI wanda kasashen duniya suka yi ne, ya ke bawa HKI karfin giwan ci gaba da abinda take yi a gaza.
Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kakakin majalisar dokokin kasar ta Iran yana fadar haka a taron shuwagabannin majalisun dokokin wanda ake gudanarwa a halin yanzu a birnin Geneva.
Wannan dai shi ne taron shuwagabannin majalusun dokoki na duniya karo na 6 wanda MDD take daukar nauyinta.
Dangane da hare-haren da HKI da Amurka suka kaiwa kasar Iran a cikin watan Yunin da ya gabata kuma ,Qalibof ya bayyana cewa manufarsu it ce lalata shirin Nukliyar kasar Iran ta zaman lafiya, kwata-kwata. Alhali hukumar makamashin Nukliya ta duniya wato IAEA tana sanya iado a kan ayyukan sarrafa uranium da kasar take yi.
Shugaban majalisar dokokin kasar Iran ya bayyana cewa hare-haren kwanaki 12 wanda wadan nan kasashe biyu wadanda basa son zaman lafiya a Iran sun kai mutane kimani 1100 ga shahada. Sannan sun sanya shirin nukliyar kasar Iran cikin hatsari, wanda ya tilasta mana daukar matakai don kare shi.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Yunwa Ta Kashe Karin Falasdinawa 7 A Gaza July 30, 2025 Malta Zata Amince da Samuwar Falasdinu a Cikin Watan Satumba Mai Zuwa July 30, 2025 Amurka Ta Ce HKI Ba Zata Fice Daga Kasar Lebanon Ba Sai An Kwance Damarar Hizbullah July 30, 2025 Siriya Da HKI Zasu Gudanar Da Taro A Baku July 30, 2025 Girgizar Kasa Mai Karfi Ta Kada Yankin Kamtashatka Na Kasar Rasha July 30, 2025 Yahudawa ‘Yan Share Wuri Zauna Sun Kutsa Cikin Masallacin Kudus July 30, 2025 Kasashen Yankin Caribbean Suna Son Bunkasa Alakarsu Ta Kasuwanci Da Nahiyar Afirka July 30, 2025 Shugaban Kasar Ivory Coast Ya Bayyana Shirinsa Na Sake Tsayawa Takarar Shugabanci Karo Na Hudu July 30, 2025 Kasashen Iran Da Rasha Sun Tattauna Batun Hadin Gwiwar Kafofin Watsa Labarai A Tsakaninsu July 30, 2025 MDD Zata Aiwatar Da Hanyar Warware Rikicin Falasdinawa Da Yahudawan Sahayoniyya July 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci