Asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF ya bukaci masu tsara manufofi a fannin ilimi a Najeriya da su dauki kwararan matakai don magance gibin da ke tattare da zamantakewa da al’adu da ababen more rayuwa da manufofin da ke haifar da yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a kasar.

Shugabar ofishin UNICEF na Kano, Rahama Rihood Farah, ne ya yi wannan kiran a wani taron manema labarai na bikin ranar ilimi ta duniya ta shekarar 2025.

Ya yi nuni da cewa, Jihohin Kano, da Jigawa da Katsina suna da adadin yara miliyandaya da dubu dari takwas da sittin da uku, da dari biyu da bakwai (1,863,207) da ba sa zuwa makaranta a matakin firamare,  da kuma miliyan daya  da dubu dari daya da saba’in da shidd, da dari tara da goma sha takwas(1,176,918), a matakin kananan makarantun sakandare, wanda ya bayyana a matsayin abin ban tsoro.

Ya gano wasu kalubalen da ke ci gaba da faruwa a halin da ake ciki  baya ga makaranta, da suka hada da rashin isassun kudade, da rashin kula da al’adu, da rashin isassun kayayyakin more rayuwa a makarantu, da karancin ma’aikata da gudun hijira sakamakon ambaliyar ruwa da sauran illolin sauyin yanayi.

“Yayin da Arewa maso Yammacin Najeriya ta kasance ta biyu a kasar da ba a zuwa makaranta, lamarin da ake fama da shi a jihohin Kano da Jigawa da Katsina yana da ban tsoro.

“Abin da ya kara ta’azzara shi ne sakamakon rashin ingantaccen ilimi ga yaran da suka yi sa’ar shiga makaranta.

“A halin yanzu akwai kimanin yara miliyan goma da dari biyu a matakin firamare da ba sa zuwa makaranta a Najeriya, inda kashi 16 cikin 100 sun fito ne daga jihohin Kano, da Jigawa da Katsina, a cewar rahoton MICS  na shekarar 2021.

“Kusan yara miliyan daya ne ba sa zuwa makaranta a jihar Kano da jimillar mutane 989,234, yayin da a Jigawa ana da jimillar 337,861 sai  jihar Katsina da ke da yara 536,112 da ba sa zuwa makaranta.”

Mr Farah ya bukaci gwamnatocin jihohin Kano, da Jigawa da Katsina da su daidaita kasafin  kudi tare da fitar da su a zahiri ga bangaren ilimi daidai da abin da ake bukata na Manufofin Ci Gaba Mai Dorewa na SDG da ma’aunin Hukumar kula da Ilimi, da Kimiyya da Al’adu ta Majalisar Dinkin Duniya (UNESCO) don ingantacciyar sakamako a fannin.

Ya kuma yi kira ga gwamnatocin wadannan jahohin da su tunkari kalubalen samun ilimi ta hanyar fadada abubuwan more rayuwa a makarantu da daukar kwararrun malamai da shigar da makarantun kur’ani a cikin tsari na yau da kullun.

 

Daga Isma’il Adamu

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An hana hawa babur da daddare a fadin jihar Gombe

A yayin da ake tsaka da bikin Ranar Dimokradiyya a Najeriya, al’ummar jihar Gombe sun wayi gari da sabuwar dokar takaita zirga-zirgar babura daga ƙarfe 7:00 na yamma zuwa ƙarfe 6:00 na safe a duk faɗin jihar.

Sanarwar da ta fito ne daga hannun Jami’in Hulɗa da Jama’a na Rundunar ’Yan Sanda ta jihar, DSP Buhari Abdullahi, ranar Alhamis, a madadin kwamishinan ’yan sandan jihar Bello Yahaya.

Sanarwar ta ce an kafa dokar ne don rage ayyukan ta’addanci a fadin jihar.

Guguwa ta hallaka mutum 6, ta jikkata 30 a Taraba An kashe mutum 41 cikin mako ɗaya a Filato 

Kafa dokar na zuwa ne kwana uku bayan wasu matasa da ba a tantance su wane ne ba suka kashe wani magidanci mai suna Ahmad Aliyu, wanda aka fi sani da Amadi Kasiran, a unguwar Hammadu Kafi da ke Gombe, a daren Lahadi.

Sanarwar ta ƙara da cewa duk wanda aka kama ya karya dokar zai fuskanci hukunci mai tsauri, ciki har da gurfanar da shi a gaban kotu.

Kazalika, sanarwar ta ce dokar ta haramta ɗaukar mutum fiye da ɗaya a kan babur domin rage matsalar rashin tsaro a jihar.

“Dokar hana hawa babur da goyon biyu ta fara aiki ne daga yau, Alhamis, ranar bikin Dimokradiyya, har sai wani lokaci da ba a kayyade ba,” in ji Kakakin ’yan sandan.

Rundunar ’yan sandan ta ce an ɗauki wannan mataki ne don magance matsalar bata-gari na ‘’yan kalare’ da sauran ayyukan ta’addanci.

A lokacin da wakilinmu ya kai ziyara kwaryar birnin Gombe, filin wasa na Pantami ya kasance a rufe ba tare da alamar wani biki ba.

Sai dai ya gane wa idanunsa cewa an jibge jami’an tsaro a sassa daban-daban, ciki har da ’yan sanda, jami’an tsaro na farin kaya (DSS), da kuma ’yan banga.

Wannan sabuwar doka ta ja hankalin mutane da dama a jihar, musamman mazauna yankunan da aka fi samun matsalar tsaro.

Sai dai wasu na gani za ta kara jefa jihar cikin kuncin talauci sakamakon rufe shaguna da kasuwanni da wuri saboda rashin abun hawa wanda dama can baburan aka fi hawa saboda tsadar rayuwa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe
  • HKI Ta Rufe Filin Saukar Jiragen Sama Na Ben Gorion Tare Da Dauke Jiragenta  Zuwa Waje
  • Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai
  • Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya
  • An kama ’yar Najeriya da laifin safarar ɗalibai 15 a Australia
  • Matsin Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Sun Rage Zuwa Kasashen Waje
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
  • NAJERIYA A YAU: Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Su A Najeriya
  • 12 ga Yuni: Najeriya na bikin ranar dimokuraɗiyya
  • An hana hawa babur da daddare a fadin jihar Gombe