Aminiya:
2025-09-17@23:08:59 GMT

An harbe masu garkuwa da mutane 3 a Kebbi

Published: 24th, August 2025 GMT

’Yan sanda sun samu nasarar kashe wasu mutum uku da ake zargin masu garkuwa da mutane ne, tare da ƙwato bindigar AK-47 bayan musayar wuta da su a yankin Shanga na Jihar Kebbi.

Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, CSP Nafiu Abubakar, ya fitar.

Mutum 6 sun rasu yayin tsere wa ’yan bindiga a Sakkwato An tsinci gawar saurayi a gefen kudiddifi a Kalaba

Sanarwar ta bayyana cewa lokacin da lamarin ya faru, DPO na Shanga ya gaggauta haɗa jami’an ‘yan sanda da ‘yan sa-kai waɗanda suka fafata da ‘yan bindigar, inda aka kashe uku daga cikinsu, sauran kuma suka tsere cikin daji.

Kakakin ’yan sandan ya ce wannan nasara na da nasaba da bayanan sirrin da suka tattara cewa wata tawagar masu garkuwa da mutane ta ɓulla a dajin da ke kan hanyar Tungargiwa zuwa Saminaka, suna shirin yin garkuwa da matafiya.

A wani lamari daban, sanarwar ta ce wasu gungun masu garkuwa ɗauke da makamai masu haɗari sun afka garin Kesan a Ƙaramar Hukumar Shanga, inda suka yi garkuwa da wani matashi mai suna Abdulmumini Alhaji Ahmadu, mai shekaru 25.

Shi ma dai bayan samun rahoton ne, DPO na yankin ya tura tawagar jami’an tsaro wadda ta bi sawun masu garkuwan har suka ceto matashin da aka sace.

Sai dai yayin aikin ceton, an harbi matashin a ƙafarsa ta hagu, inda yanzu haka yana samun kulawa a wani asibiti da ke yankin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: garkuwa da mutane Jihar Kebbi masu garkuwa

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

 

Danja ya ce, sojojin a yayin da suke aiki da sahihan bayanan sirri dangane da shirin kai hari kan al’ummar Chanchangi da kungiyar ta’adda ta Bojo ke shirin yi a ranar 15 ga Satumba, 2025, sun yi artabu da ‘yan ta’addan a kan hanyar Demeva zuwa Chanchangi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
  • An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba
  • Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi