Gwamnatin Kasar Chadi Ta Maida Martani Kan Dokar Hana Yan Kasar Shiga Amurka
Published: 6th, June 2025 GMT
Shugaban kasar Chadi Muhammad Deby ya maida martani ga shugaban kasar Amurka kan hana yan kasar Chadi shiga kasar Amurka da hana a bawa Amurkawa visar shiga kasar.
Jaridar PREMIUM TIMES ta Najeriya ta bayyana cewa shugaban kasar Amurka a ranar Laraban da ta gaba ne ya sanya hannu a kan dokoki wadanda suka hana yan kasashe 12 shiga kasar Amurka sannan wasu 7 kuma za’a basu Visa shigar kasar tare da sharudda.
A jiya Alhamis ne shugaban Deby ya maida martani, da haka Amurkawa shiga kasarsa. Dokar dai ta hana kasashen Afirka guda 6 shiga kasar Amurka kuma sun hada da Chadin da kuma Congo, Equatorial Guinea, Eritrea, Libya, Somalia da kuma Sudan.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Amurka shiga kasar
এছাড়াও পড়ুন:
Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta
Ta hanyar inganta manufar yafe harajin kwastam a kai a kai, kasar Sin ta samar da yanayin kasuwanci mai karko a kasashen Afirka. Bugu da kari, kasar Sin tana kallon manufofinta na rangwame a matsayin matakan tabbatar da burin samun ci gaba, inda take kokarin kyautata tsarin cinikayyar waje na kasashen Afirka, da kuma ba da goyon baya wajen raya masana’antu, da habaka tsare-tsaren tattalin arziki a Afirka.
Dalilin da ya sa kasar Sin ke kokarin tabbatar da ci gabanta da kasashen Afirka na bai daya, shi ne domin ra’ayinta game da dangantakar dake tsakaninta da Afirka, wato al’ummar Sin da Afirka suna da makomar bai daya a nan gaba. A ganin kasar Sin, ita da Afirka suna da tarihi masu kama da juna, da kuma bukatun bai daya na raya kasa. Sa’an nan, a zamanin da muke ciki, yayin da ake fuskantar sauye-sauye a fannonin siyasa, da tattalin arziki, da kimiyya da fasaha, kasashe masu tasowa na cikin wani yanayi mai wuya ta fuskar raya tattalin arzikinsu. Saboda haka, Sin da Afirka ba za su iya cimma burinsu na samun ci gaban bai daya ba, sai dai ta hanyar hadin gwiwa da juna, a bangarorin tabbatar da adalci da gaskiya a duniya , da bude kofa, da tabbatar da moriyar kowa, da kyautata muhalli, da kuma kiyaye zaman lafiya. Bisa kokarin da ake na sauya nagartaccen tunani zuwa hakikanan matakai, ko shakka babu za mu shaida karin nasarorin da Sin da Afirka za su samu, a kokarinsu na zamanantar da al’ummunsu tare. (Bello Wang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp