Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai
Published: 6th, June 2025 GMT
A yau Alhamis, ma’aikatar ciniki ta kasar Sin ta bayyana cewa, kasar Sin ta bukaci kasar Amurka da ta yi watsi da amfani da batun tsaron kasa barkatai wadda ta mayar da shi mai gamewa gaba daya da kuma wuce gona da iri, kana ta hada kai da dukkan bangarori wajen kiyaye tsarin cinikayya tsakanin sassa daban-daban.
A wani taron manema labarai da aka saba yi a-kai-a-kai, mai magana da yawun ma’aikatar, He Yongqian, ta bayyana hakan a lokacin da aka bukaci ta tofa albarkacin bakinta game da matakin da Amurka ta dauka na kara haraji kan karafa da holoko da kayayyakin da ake sarrafawa da su wadanda ake kaiwa kasar, daga kashi 25 zuwa 50 cikin dari. Ya ce irin wannan yunkuri na Amurka ba wai yana cutar da wasu da ita kadai ba ne, har ma zai kawo cikas ga sha’anin tafiyar da masana’antu cikin lumana da samar da kayayyaki a duniya.
Lokacin da take tsokaci kan sabbin takunkumai da Amurka ta sanya ga kasar Sin bayan tattaunawar tattalin arziki da cinikayya da aka yi a Geneva cikin watan Mayu, mai magana da yawun ma’aikatar ta ce, kasar Sin ta sauke hakkokinta, tare da tabbatar da aiki da matsayar da aka cimma a tattaunawar.
Sai dai kuma, duk da haka, Amurka ta kakaba wasu sabbin takunkumai kan kasar Sin, tare da yin watsi da matsayar da aka cimma, kuma ta yi mugun tauye hakkoki da muradun kasar Sin. Ta kara da cewa, kasar Sin tana matukar nuna rashin gamsuwa da kuma adawa da hakan, inda ta bukaci Amurka da ta dakatar lamarin nan take. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: kasar Sin ta
এছাড়াও পড়ুন:
Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta
Ofishin yada labarai na majalisar gudanarwar Sin ya gudanar da taron manema labarai da misalin karfe 10 na safiyar yau Litinin, inda kakakin hukumar kididdiga ta kasar, kuma babban masanin tattalin arziki, kana daraktan sashen kididdigar tattalin arziki na kasar, Fu Linghui ya yi karin haske kan ayyukan tattalin arzikin kasar cikin watan Agustan bana, tare da amsa tambayoyin manema labarai.
A cewar bayanan da aka gabatar a yayin taron, ayyukan tattalin arzikin kasar a watan Agusta sun samu ci gaba ba tare da tangarda ba. Kuma hakan ya bayyana ne ta hanyoyi daban-daban kamar haka: masana’antu sun habaka cikin sauri, masana’antar kera kayayyakin aiki da masana’antar fasaha sun samu ci gaba mai kyau. Kana ayyukan bayar da hidima su ma sun bunkasa cikin sauri. Baya ga haka, an samu ci gaba mai kyau a bangaren bayar da hidimomi na zamani. Harkokin kasuwanci sun samu ci gaba cikin natsuwa, inda harkokin sayar da kayayyaki ga masu sayayya suka kara habaka. Har ila yau, kadarorin jari sun ci gaba da karuwa, jarin masana’antu ya habaka cikin sauri, harkokin fice da shigen kayayyaki sun ci gaba da girma, tsarin kasuwanci ya ci gaba da ingantuwa, kana yanayin samar da guraben aikin yi, ya kasance kan wani mataki mai daidaito. Sai dai kuma saboda yanayin da ake ciki, adadin marasa aikin yi a birane ya karu, ma’aunin Core CPI ya ci gaba da hauhawa, kana faduwar farashin kayayyakin masana’antu ya ragu.
Bayanan sun kara da cewa, akwai bukatar lura da cewa, ana fuskantar yanayin rashin tabbas a waje, kuma tattalin arzikin kasar Sin yana fuskantar kalubale da hadari da yawa. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp