A yau Alhamis, ma’aikatar ciniki ta kasar Sin ta bayyana cewa, kasar Sin ta bukaci kasar Amurka da ta yi watsi da amfani da batun tsaron kasa barkatai wadda ta mayar da shi mai gamewa gaba daya da kuma wuce gona da iri, kana ta hada kai da dukkan bangarori wajen kiyaye tsarin cinikayya tsakanin sassa daban-daban.

A wani taron manema labarai da aka saba yi a-kai-a-kai, mai magana da yawun ma’aikatar, He Yongqian, ta bayyana hakan a lokacin da aka bukaci ta tofa albarkacin bakinta game da matakin da Amurka ta dauka na kara haraji kan karafa da holoko da kayayyakin da ake sarrafawa da su wadanda ake kaiwa kasar, daga kashi 25 zuwa 50 cikin dari. Ya ce irin wannan yunkuri na Amurka ba wai yana cutar da wasu da ita kadai ba ne, har ma zai kawo cikas ga sha’anin tafiyar da masana’antu cikin lumana da samar da kayayyaki a duniya.

Lokacin da take tsokaci kan sabbin takunkumai da Amurka ta sanya ga kasar Sin bayan tattaunawar tattalin arziki da cinikayya da aka yi a Geneva cikin watan Mayu, mai magana da yawun ma’aikatar ta ce, kasar Sin ta sauke hakkokinta, tare da tabbatar da aiki da matsayar da aka cimma a tattaunawar.

Sai dai kuma, duk da haka, Amurka ta kakaba wasu sabbin takunkumai kan kasar Sin, tare da yin watsi da matsayar da aka cimma, kuma ta yi mugun tauye hakkoki da muradun kasar Sin. Ta kara da cewa, kasar Sin tana matukar nuna rashin gamsuwa da kuma adawa da hakan, inda ta bukaci Amurka da ta dakatar lamarin nan take. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: kasar Sin ta

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka na iya kashe jagoran addini na Iran don mun san inda yake — Trump

Shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana cewa ya san inda jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei yake “boye”, kuma ya yi gargadi cewa Washington na iya halaka shi, amma za su dakata a halin yanzu.

Wannan na zuwa ne yayin da Trump din ya gargadi Iran kan da kada ta kai harin makamai masu linzami kan fararen hula ko kuma sojojin Amurka, yana mai cewa hakurinsu na karewa.

Iran ta kai hari hedikwatar hukumar leƙen asirin Isra’ila Rikicin ƙabilanci ya yi ajalin mutum 20 a Chadi

A wani sakon da ya wallafa a shafinsa na Truth mintuna kadan bayan wannan sako, Trump ya rubuta cewar Iran din ta mika wuya ba tare da wani sharadi ba kawai.

Rahotanni a bayan nan sun ce Trump ya ƙi amincewa da shirin Isra’ila na kashe jagoran Iran, Ayatollah Ali Khamenei, kamar yadda majiyoyi uku suka shaida wa kafar yaɗa labarai ta CBS News.

Bayanan sun ce Shugaba Trump ya shaida wa Firaiministan Isra’ila Benjamin Netanyahu cewa kashe Khamenie “ba shawara ce mai kyau ba.”

Tattaunawar ta faru ne bayan harin da Isra’ila ta ƙaddamar kan Iran a ranar Juma’a.

A lokacin wata tattaunawa da kafar yaɗa labarai ta Fox News, Netanyahu bai fayyace kai-tsaye ko Trump ya ƙi amincewa da shawarar kashe Ayatollah ba, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito.

“Akwai rahotannin da dama kan tattaunawar da ake cewa an yi amma kuma ba gaskiya ba ne, ba zan shiga cikin irin wannan maganar ba,” in ji Firaiminstan Isra’ila.

Tun tsawon kwanaki biyar, Isra’ila ke kai hare-hare a cikin Iran, da suka shafi wuraren nukiliya da manyan kwamandojin soji da masana kimiyya da cibiyoyin tsaro da birane da ma cibiyoyin mai da iskar gas.

Iran dai ta mayar da martani da makamai masu linzami gami da jirage masu sarrafa kansu a kan Isra’ila, lamarin da ke kara fargabar cewa Amurka za ta iya shiga cikin rikicin kai tsaye, wanda kuma zai iya haifar da sabon babi mai hadari a rikicin.

A gefe guda kuma, babban hafsan tsaron Iran ya yi gargadi ga mazauna Isra’ila “musamman ma na biranen Tel Aviv da Haifa da su gaggauta barin wurarensu don tsira da rayukansu.

Janar Abdolrahim Mousavi, ya ce ayyukan da aka gudanar zuwa yanzu sun kasance gargadi ne kan abin da ke tafe, kuma za a gudanar da wani aiki na ladabtarwa nan ba da jimawa ba daga Iran.

Koda yake hare-haren Iran sun kashe akalla Isra’ilawa 24 tun a ranar Juma’a, galibin makaman Iran din dai Isra’ila ta dakatar da su ta hanyar tsarin kariyarta ta sama.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Fadada Matakin Rage Haraji Ga Kasashe Masu Raunin Tattalin Arziki
  • Sin Na Son Taka Rawar Gani Wajen Maido Da Kwanciyar Hankali A Yankin Gabas Ta Tsakiya Cikin Sauri
  • Kotun Amurka ta daure ’yan Najeriya 5 shekaru 159 kan aikata damfara
  • Kar a kuskura a shiga cikin yaƙin Iran da Isra’ila — MDD
  • Dan Wasan Gaban Chelsea, Murdyk Ka Iya Shafe Shekaru 4 Ba Tare Da Ya Buga Wasa Ba
  • Sin Za Ta Samar Da Cibiyar Kasa Da Kasa Ta Gudanar Da Hada-hadar Kudin RMB Na Dijital
  • Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta
  • Amurka na iya kashe jagoran addini na Iran don mun san inda yake — Trump
  • Kaftin Din Super Eagles, Ahmed Musa Ya Bukaci A Gaggauta Kawo Karshen Kashe-kashen Rayuka A Benuwe
  • Sin Ta Fatattaki Laifukan Zamba Ta Shafin Intanet 294,000 A Bara