Wani mutum ya mutu a cikin rijiya a Kano
Published: 5th, June 2025 GMT
Wani matashi dan shekara 33 mai suna Muhammad Sagir ya rasa ransa bayan ya fada rijiya a unguwar Kawon Alhaji Sani da ke karamar hukumar Nasarawa a Jihar Kano.
A cewar jami’in hulda da jama’a na hukumar kashe gobara ta Jihar Kano, mataimakin jami’in kashe gobara (ACFO) Saminu Yusif Abdullahi, ya ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 12:42 na rana a ranar Laraba, 4 ga watan Yuni, 2025.
Ya ce hukumar kashe gobara ta samu kiran gaggawa daga wani mai suna Sabi’u Muhammed, inda ya sanar da su lamarin.
“Nan da nan aka tattara tawagar ceto daga hedkwatar hukumar zuwa wurin.”
“Da isowar jami’an, ma’aikatan sun gano wani mutum guda mai suna Muhammad Sagir mai kimanin shekaru 33, wanda ya fada cikin busasshiyar rijiya, an ceto shi a sume kuma daga bisani aka tabbatar da mutuwarsa,” in ji shi.
Daga nan ne aka mika gawar marigayin ga hakimin Kawon Arewa, Alhaji Hamisu.
Hukumar kashe gobara ta jihar ta nanata kudurinta na daukar matakan gaggawa, sannan ta bukaci mazauna yankin da su tabbatar da killace budaddun rijiyoyi da makamantansu domin hana afkuwar ibtila’i a nan gaba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Hukumar Kashe gobara ta Kano rijiya kashe gobara
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Namadi Ya Jinjinawa Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Bisa Ayyukan Raya Kasa
Gwamnatin Jihar Jigawa ta nuna matukar gamsuwa tare da yabawa Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu, Dr Builder Muhammad Uba bisa kokarin sa na ayyukan raya kasa.
Gwamna Umar Namadi ya bayyana hakan ne a lokacin kaddamar da bude ofishin shugaban karamar hukumar da kuma dakin taro na karamar hukumar da aka gudanar a sakatariyar karamar hukumar ta Birnin Kudu.
Ya ce shugaban karamar hukuma, Dr Builder Muhammad Uba mutum ne mai kwazo da himma wanda ya zamto abin koyi a bangaren shugabanci.
A don haka, Malam Umar Namadi ya yi kira ga sauran shugabanin kananan hukumomin jihar da su tashi tsaye wajen gudanar da ayyukan kyautata rayuwar al’ummar su domin sharbar romon mulkin dimokradiyya.
A jawabinsa na godiya shugaban ƙaramar hukumar, Dr Builder Muhammad Uba ya godewa Gwamnan bisa samun damar bude ofishin da kuma dakin taro na karamar hukumar.
Wakilinmu ya ba mu rahoton cewar, Gwamnan ya sami rakiyar Mataimakinsa, Injiniya Aminu Usman Gumel da Shugaban Majalisar Dokokin Jihar, Alhaji Haruna Aliyu Dangyatun da Sakataren Gwamnati Alhaji Bala Ibrahim da Shugaban Jami’yya na Jihar Alhaji Aminu Sani Gumel da Kwamishinoni da sauran mukarraban gwamnatin jihar.
Usman Mohammed Zaria