Wani mutum ya mutu a cikin rijiya a Kano
Published: 5th, June 2025 GMT
Wani matashi dan shekara 33 mai suna Muhammad Sagir ya rasa ransa bayan ya fada rijiya a unguwar Kawon Alhaji Sani da ke karamar hukumar Nasarawa a Jihar Kano.
A cewar jami’in hulda da jama’a na hukumar kashe gobara ta Jihar Kano, mataimakin jami’in kashe gobara (ACFO) Saminu Yusif Abdullahi, ya ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 12:42 na rana a ranar Laraba, 4 ga watan Yuni, 2025.
Ya ce hukumar kashe gobara ta samu kiran gaggawa daga wani mai suna Sabi’u Muhammed, inda ya sanar da su lamarin.
“Nan da nan aka tattara tawagar ceto daga hedkwatar hukumar zuwa wurin.”
“Da isowar jami’an, ma’aikatan sun gano wani mutum guda mai suna Muhammad Sagir mai kimanin shekaru 33, wanda ya fada cikin busasshiyar rijiya, an ceto shi a sume kuma daga bisani aka tabbatar da mutuwarsa,” in ji shi.
Daga nan ne aka mika gawar marigayin ga hakimin Kawon Arewa, Alhaji Hamisu.
Hukumar kashe gobara ta jihar ta nanata kudurinta na daukar matakan gaggawa, sannan ta bukaci mazauna yankin da su tabbatar da killace budaddun rijiyoyi da makamantansu domin hana afkuwar ibtila’i a nan gaba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Hukumar Kashe gobara ta Kano rijiya kashe gobara
এছাড়াও পড়ুন:
Masu Garkuwa Da Mutane Sun Dira Jihar Kogi, Sun Sace Wani Basarake
Ƴansandan jihar Kogi sun tabbatar da sace wani basarake mai suna Samuel Ajayi Bello yayin da yake aikin gona a gidan gonarsa na Ponyan da ke kan titin Ponyan-Irele, a ƙaramar hukumar Yagba ta Gabas.
Mai magana da yawun ‘yansandan jihar, SP William Aya, ya bayyana cewa lamarin ya faru ne da ƙarfe 10 na safe a ranar Litinin. Ya kuma ce Kwamishinan ‘yansandan jihar ya tura rundunar ta musamman don taimakawa wajen gudanar da bincike da kuma ceto wanda aka sace.
Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Afirka Sun Yi Alkawarin Karfafa Alaka Ƴan Bindiga Sun Kai Farmaki Kwara, Sun Kashe Mutum 1, Sun Ƙona GidajeShugaban ƙungiyar ci gaban yankin Ponyan, Hon. Banjo Fabola, ya tabbatar da cewa an sace Ajayi ne tsakanin karfe 9 zuwa 10 na safe, inda ‘yansanda da ‘yan sa kai suka fara bincike a dazuzzukan yankin.
Akwai bayanin cewa wasu sassan jihar na fama da hare-haren ‘yan fashi a baya-bayan nan, inda wasu mutane suka mutu yayin da ake sace-sace. Duk da haka, Kwamishinan yaɗa labarai na jihar, Kingsley Fanwo, ya tabbatar da cewa gwamnati na ɗaukar matakai don magance wannan matsala.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp