Aminiya:
2025-06-06@16:23:15 GMT

Wani mutum ya mutu a cikin rijiya a Kano

Published: 5th, June 2025 GMT

Wani matashi dan shekara 33 mai suna Muhammad ​​Sagir ya rasa ransa bayan ya fada rijiya a unguwar Kawon Alhaji Sani da ke karamar hukumar Nasarawa a Jihar Kano.

A cewar jami’in hulda da jama’a na hukumar kashe gobara ta Jihar Kano, mataimakin jami’in kashe gobara (ACFO) Saminu Yusif Abdullahi, ya ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 12:42 na rana a ranar Laraba, 4 ga watan Yuni, 2025.

Tsohon Ministan Ilimi, Farfesa Jibril Aminu, ya rasu

Ya ce hukumar kashe gobara ta samu kiran gaggawa daga wani mai suna Sabi’u Muhammed, inda ya sanar da su lamarin.

“Nan da nan aka tattara tawagar ceto daga hedkwatar hukumar zuwa wurin.”

“Da isowar jami’an, ma’aikatan sun gano wani mutum guda mai suna Muhammad ​​Sagir mai kimanin shekaru 33, wanda ya fada cikin busasshiyar rijiya, an ceto shi a sume kuma daga bisani aka tabbatar da mutuwarsa,” in ji shi.

Daga nan ne aka mika gawar marigayin ga hakimin Kawon Arewa, Alhaji Hamisu.

Hukumar kashe gobara ta jihar ta nanata kudurinta na daukar matakan gaggawa, sannan ta bukaci mazauna yankin da su tabbatar da killace budaddun rijiyoyi da makamantansu domin hana afkuwar ibtila’i a nan gaba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hukumar Kashe gobara ta Kano rijiya kashe gobara

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Kashe Falasdinawa Wadanda Suke Jin Yunwa A Gaza

Gwamnatin kasar Amurka wacce ta bude cibiyoyin rarraba kayakin Agaji a Gaza, ta ce zata rufe cibiyoyin zuwa ranar Alhamis mai zuwa don sake tsara ayyukan Rabomn.  Majiyar gwamnatin Amurka ta bayyana cewa ta dauki wannan matakin ne saboda sojojin yahudawan suna kashe falasdinawa wadanda suke fama da yunwa a lokacinda suka iso cibiyoyin raba abincin ko kuma suka hau kan hanyar zuwa karban abincin.

Labarin ya kara da cewa a jiya Talata kadai sojojin yahudawan sun kashe Falasdinawa mayunwata 27 a kokarinsu na karban abinci.

Sannan a yau Laraba ya zuwa lokacin bada wannan labarin sojojin yahudawan sun kashe Falasdinawa 32 a hare-haren da suka kai kan yankuna daban-daban a Gaza.

Majiyar ta kara da cewa Palasdinawa 95 ne sojojin yahudawan suka kai ga shahada a cikin sa’o’I 24 da suka gabata a gaza, sannan wasu 440 kuma suka ji rauni.

Tun ranar 7 ga watan Octoban shekara ta 2023 ya zuwa yanzu Falasdina 54,607 ne suka yi shahada a Gaza, kuma tana ci gaba da kara kashewa ba wanda ya isa ya yi magana a duniya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsohon Alkalin Alkalan Najeriya, Lawal Uwais ya rasu
  • Mun gurfanar da mutum 29 a kotu kan zargin kashe DPO a Kano – ’Yan sanda
  • Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano
  • Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Kashe Falasdinawa Wadanda Suke Jin Yunwa A Gaza
  • Mutum 7 Sun Rasu Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Sakkwato 
  • Jami’an DSS sun kashe ’yan bindiga 45 a Neja
  • Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Ta Yi Tanadi Na Musamman Ga Alhazanta A Mina
  • Kasa ta danne almajirai 11 sun mutu a Kaduna
  • DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja