Aminiya:
2025-07-24@03:45:00 GMT

Bukukuwan sallah tare da Malta Guinness a Birnin Kano

Published: 6th, June 2025 GMT

A yayin da al’ummomi a fadin Najeriya ke shirin Sallar Idi, daya daga cikin manya-manyan bukukuwan Musulunci,

Kano, cibiyar al’adun arewacin Najeriya, na shirin gudanar da wani biki Mai kayatarwa wanda Malta Guinness, ɗaya daga cikin samfuran kayan sha Mai dandanon Dadi da yayi fice a ƙasar nan, zai ƙaddamar da wannan biki na kwanaki uku da nufin zurfafa ruhin al’umma ta hanyar raba alheri da kyaututtuka ga masu rabo.

An tsara shirin ba a matsayin nunin tallace-tallace ba amma a matsayin taron nunin al’adu da ke tattaro irin kade-kade, da wasan kwaikwayo na gargajiya don nishadantarwa.

Za’ayi wannan ruguntsumi ne, a Dakin taro na Ado Bayero Hall, dake Kano, daga ranar 7 zuwa 9 ga watan Yuni, 2025.

A lokacin wannan shagali akwai gasar Mai rabo ka samu wato na raffle inda wasu iyalai zasu samu damar samun kyautar Ragon Layya a lokacin wannan ruguntsumi na Bikin baje kolin al’adun gargajiya don nishadantarwa da raya aladu alokacin Bikin Sallar babba.

Wannan gangami dai zai kunshi fitattun jaruman fina-finai irinsu Ali Nuhu, wanda ake yi wa kallon wata gada ta yaukaka al’ada atsakanin mutanen arewa, akwai kuma fitattun jaruman da suka hada da Chef Maah da Ali Nurudeen da zasu kasance awajen wannan shagali.

Shigarsu wannan ruguntsumi yana nuna mahimmancin shirin da dacewa da al’adu da kuma faɗakarwa yayin da suke ƙarfafa saƙon haɗin kai ga jama’a.

Malta Guinness’ yana ba da wani hoto ba kawai a matsayin masu tallafawa ba amma a matsayin mahalarta taron bunkasa al’adu yayin da Kano ke cikin bukukuwan murnar Idi,

Kar ku manta kyawawan abubuwan da aka raba – zasu zama abin farin ciki da kuma tunawa da alherin da Malta Guinness a tsawon lokaci.

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

 Kungiyar Malaman Musulmi Ta Yi Fatawar Wajabcin Kawo Karshen Killace Gaza

Kungiyar ta malaman musulumi ta fitar da fatawa da a ciki ta bukaci gwamnatoci da al’ummar musulmi da su yunkura cikin gaggawa domin kawo karshen killace yankin Gaza da aka yi, da kuma wajabcin kai musu abinci da magunguna.

Kungiyar malaman musulmin ta kuma bayyana abinda HKI take yi na killace mutanen Gaza fiye da miliyan biyu da haka su abinci da magani,musamman mata, yara da manya,wani babban laifi ne da ba shi da tamka a cikin tarihi, tana mai yin kira ga al’ummu da gwamnatoci da su motsa saboda su taimaki raunana.

Kwamitin fatawa da yake a karkashin wannan kungiyar ta malaman musulmi, ya dogara da ayoyin alkrur’ani da hadisan ma’aiki ( s.a.w) da manufofi na shari’a da ka’idoji na fikihu da su ka wajabta taimakawa wadanda aka zalunta da kawar da zaluncin da ake yi masa.

Fatawar ta kuma bayyana cewa, kin taimakawa wajen taimakawa alhali da akwai dama, yana daidai da yin tarayyar a cikin laifukan yaki.

A wani gefen, bayanin da ya fito daga kungiyar malaman musulmin ya kuma yi kira ga al’ummu da su fito domin yin zanga-zanga da zaman dirshan a gaban ofisoshin jakadancin kasashen Amurka da turai.

Har ila yau fatawar ta bukaci kasar Masar da ta dauki nauyin da ya rataya a wuyanta na tarihi da addini, ta bude mashigar Rafaha, saboda a shigar da kayan abinci da dukkanin bukatun yau da kullum. Har ila yau ta ce, yin shiru akan wannan batun shi ne;yin shiru akan wannan bala’in bai dace da ma’abota ilimi da addini.”

Wani bangare na sakon kungiyar ta malaman musulunci ya shafi yin kira ga ma’abota tunani da alkalami da su rika aikewa da sakwanni ta shafukansu domin yin matsyin lamba saboda a kawo karsehn wannan bala’in da yake faruwa a Gaza.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jihar Kano Za Ta Hada Gwiwa FMBN Don Samar Da Gidaje Masu Saukin Kudi
  • Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa
  • NEDC ta raba wa mutanen da ambaliya ta shafa kayan gini a Yobe
  • Allah Ya Yi Wa Wakilin Sadarwan Bauchi,  Jafaru Ilelah, Rasuwa
  • Pezeshkian: Tunanin Kawo Karshen Shirin Nukiliyar Iran Ya Yi Kama Da Tabuwa
  •  Kungiyar Malaman Musulmi Ta Yi Fatawar Wajabcin Kawo Karshen Killace Gaza
  • UNICEF na zargin Gwamnatin Nijeriya da cin zarafin ƙananan yara
  • An rufe masana’antu 1,724 bisa rashin bin dokokin aiki a Guinea
  • Gwamna Namadi Ya Jinjinawa Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Bisa Ayyukan Raya Kasa
  • Ministocin Tsaron kasashen Rasha Da JMI Sun Hadu A Birnin Mosco