Musulman Kudancin Kaduna sun yi taron addu’ar zaman lafiya
Published: 5th, June 2025 GMT
Al’ummar Musulmin yankin Kudancin Kaduna, sun shirya taron addu’a na musamman a sakatariyar karamar hukumar Sanga da ke Gwantu, Jihar Kaduna, kan neman zaman lafiya.
A yayin taron dai Babban Hafsan Tsaron Najeriya, Janar Christopher Gwabin Musa ya jaddada kudirin rundunar sojin Najeriya na dawo da zaman lafiya da tsaro a fadin kasar tare da yin kira ga ’yan kasa da su mara wa kokarin hadin kai da ci gaban kasa baya.
Janar Musa wanda Rear Admiral Ibrahim Aliyu Shettima ya wakilta, ya ce zaman lafiya shi ne ginshikin ci gaba da bunkasar kasa. Ya bukaci ’yan Najeriya baki daya, ba tare da la’akari da kabila ko addini ba, da su bayar da gudummawarsu wajen gina kasa.
Barazanar Yajin Aiki: Abuja da wasu jihohi 3 za su faɗa cikin duhu A shekara 25, na kashe tiriliyan 161 wajen inganta lafiya a Afirka – Bill GatesTaron addu’ar dai an shirya shi ne da nufin karfafa zaman tare cikin fahimta da hadin kai tsakanin Musulmai da wadanda ba Musulmai ba daga kowace kabila a yankin, ya hada limamai da malamai daga kananan hukumomin Sanga, Kaura, Jema’a, Kachia, Kagarko, Kauru, Jaba, Kajuru da Chikun.
A jawabin sa, Babban Limamin Masallacin Juma’a na Jama’a kuma shugaban al’ummar Musulmin Kudancin Kaduna da suka gudanar da addu’ar, Sheikh Muhammad Kabir Qassim, ya nuna damuwarsa kan rikice-rikicen kabilanci da na addini da suka addabi yankin tsawon shekaru, lamarin da ya ce ya jawo asarar rayuka da dukiyoyi.
“Allah ya albarkaci Kudancin Kaduna da kasar noma mai albarka, wacce za a iya noma amfanin gona ba kawai don amfanin gida ba, har ma don fitar da shi kasashen waje. Amma babu wani ci gaba da za a samu idan babu zaman lafiya da tsaro,” in ji shi.
Ya yi kira ga daukacin mazauna yankin da su hade kai wajen dawo da martabar yankin da ta lalace tare da jaddada cewa hadin kai ne makamin jawo masu zuba jari da samar da damarmaki ga matasa.
Malamin ya nuna godiyarsa ga kokarin Janar Christopher Musa na dawo da zaman lafiya, yana mai cewa kudirinsa na tattaunawa da sulhuntawa zai taimaka wajen bude sabuwar hanyar ci gaba a Kudancin Kaduna da Najeriya baki daya.
Sauran masu jawabi a wajen taron sun jaddada muhimmancin hadin kan addinai da hadin gwiwar al’umma wajen magance matsalolin tsaro, tare da daukar alkawarin ci gaba da yin addu’o’i don samun zaman lafiya da hadin kai a fadin kasar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Zaman lafiya zaman lafiya
এছাড়াও পড়ুন:
Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha
Ministan harkokin wajen Iran ya gana da takwarorinsa na Qatar, Turkiyya, Pakistan da Lebanon a Doha fadar mulkin kasar Qatar
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya gana da takwaransa na Qatar a gefen taron ministocin harkokin wajen kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC a birnin Doha.
Doha ta sanar da cewa, fira ministan kasar Qatar kuma ministan harkokin wajen kasar ya yi nazari kan al’amuran yankin na baya-bayan nan yayin ganawarsa da ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi.
A yayin wannan taro, harin da yahudawan sahayoniyya suka kaddamar a birnin Doha shi ne babban abin da ake tattaunawa akai.
Araqchi yayi Allah wadai da harin da gwamnatin mamayar Isra’ila ta kai, yana mai tabbatar da goyon bayan Jamhuriyar Musulunci ta Iran da kuma goyon bayan gwamnati ga al’ummar Qatar.
A cikin wannan yanayi, Araqchi ya gana tare da tuntubar ministan harkokin wajen Turkiyya Hakan Fidan da ministan harkokin wajen Pakistan Muhammad Ishaq Dar a gefen taron kasa da kasa a birnin Doha.
An gudanar da wadannan tarukan ne domin karfafa hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu da kuma tattauna batutuwan da suka shafi yankin.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kwamitin Kolin Tsron Kasar Iran Ya Amince Da Yarjejeniyar Da Aka Cimma Da Hukumar IAEA September 15, 2025 Jami’in Kasar Yemen Ya Aike Da Sako Ga Mahalarta Taron Birnin Doha Na Kasar Qatar September 15, 2025 Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000 September 15, 2025 Gwamnatin Sudan Ta Ce: Babu Sulhu Da ‘Yan Tawayen Kasar Na Kungiyar Rapid Support Forces September 15, 2025 Kasashen Larabawa da na Musulmi na taron gaggawa kan harin Isra’ila a Qatar September 15, 2025 Hamas ta bukaci kasashen musulmi da na Larabawa su dauki mataki mai tsari kan Isra’ila September 15, 2025 Rabin Sojojin Isra’ila da suka ji rauni a yakin Gaza na fama da ciwon damuwa September 15, 2025 Sudan ta soki takunkuman da Amurka ta kakaba mata September 15, 2025 Dakarun Sojin Yamen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Ramon Na Isra’ila. September 14, 2025 Isra’ila Za ta Gamu Da Mummunar Martani Idan Tayi Gigin Afkawa Iran September 14, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci