Aminiya:
2025-06-18@03:02:35 GMT

Musulman Kudancin Kaduna sun yi taron addu’ar zaman lafiya

Published: 5th, June 2025 GMT

Al’ummar Musulmin yankin Kudancin Kaduna, sun shirya taron addu’a na musamman a sakatariyar karamar hukumar Sanga da ke Gwantu, Jihar Kaduna, kan neman zaman lafiya.

A yayin taron dai Babban Hafsan Tsaron Najeriya, Janar Christopher Gwabin Musa ya jaddada kudirin rundunar sojin Najeriya na dawo da zaman lafiya da tsaro a fadin kasar tare da yin kira ga ’yan kasa da su mara wa kokarin hadin kai da ci gaban kasa baya.

Janar Musa wanda Rear Admiral Ibrahim Aliyu Shettima ya wakilta, ya ce zaman lafiya shi ne ginshikin ci gaba da bunkasar kasa. Ya bukaci ’yan Najeriya baki daya, ba tare da la’akari da kabila ko addini ba, da su bayar da gudummawarsu wajen gina kasa.

Barazanar Yajin Aiki: Abuja da wasu jihohi 3 za su faɗa cikin duhu A shekara 25, na kashe tiriliyan 161 wajen inganta lafiya a Afirka – Bill Gates

Taron addu’ar dai an shirya shi ne da nufin karfafa zaman tare cikin fahimta da hadin kai tsakanin Musulmai da wadanda ba Musulmai ba daga kowace kabila a yankin, ya hada limamai da malamai daga kananan hukumomin Sanga, Kaura, Jema’a, Kachia, Kagarko, Kauru, Jaba, Kajuru da Chikun.

A jawabin sa, Babban Limamin Masallacin Juma’a na Jama’a kuma shugaban al’ummar Musulmin Kudancin Kaduna da suka gudanar da addu’ar, Sheikh Muhammad Kabir Qassim, ya nuna damuwarsa kan rikice-rikicen kabilanci da na addini da suka addabi yankin tsawon shekaru, lamarin da ya ce ya jawo asarar rayuka da dukiyoyi.

“Allah ya albarkaci Kudancin Kaduna da kasar noma mai albarka, wacce za a iya noma amfanin gona ba kawai don amfanin gida ba, har ma don fitar da shi kasashen waje. Amma babu wani ci gaba da za a samu idan babu zaman lafiya da tsaro,” in ji shi.

Ya yi kira ga daukacin mazauna yankin da su hade kai wajen dawo da martabar yankin da ta lalace tare da jaddada cewa hadin kai ne makamin jawo masu zuba jari da samar da damarmaki ga matasa.

Malamin ya nuna godiyarsa ga kokarin Janar Christopher Musa na dawo da zaman lafiya, yana mai cewa kudirinsa na tattaunawa da sulhuntawa zai taimaka wajen bude sabuwar hanyar ci gaba a Kudancin Kaduna da Najeriya baki daya.

Sauran masu jawabi a wajen taron sun jaddada muhimmancin hadin kan addinai da hadin gwiwar al’umma wajen magance matsalolin tsaro, tare da daukar alkawarin ci gaba da yin addu’o’i don samun zaman lafiya da hadin kai a fadin kasar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Zaman lafiya zaman lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaro 4 Da Manoma A Katsina

Jaridar LEADERSHIP ta ruwaito cewa gwamnatin Jihar Katsina na ƙoƙarin sasantawa da wasu ƙungiyoyin ‘yan bindiga a wasu yankunan jihar.

Wasu daga cikin ‘yan bindigar da ke Jibia, Batsari da DanMusa sun amince da zaman lafiya tare da miƙa makamansu.

Sai dai wannan hari na baya-bayan nan ya sa al’umma sun fara shakkar ko zaman lafiyar zai ɗore.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Buni ya bai wa manoma 1,000 tallafin aikin gona
  • Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakin Soke Haraji Kan Kayayyakin Kasashen Afirka 53
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaro 4 Da Manoma A Katsina
  • Yaƙin Iran da Isra’ila: Amurka za ta tura jami’anta don tattaunawa da Tehran
  • Sin Ta Yi Kira Ga Iran Da Isra’ila Su Dauki Matakan Dakile Ruruwar Wutar Rikicinsu Nan Da Nan
  • Shugabannin Duniya Za Su Gudanar Da Taron Sanya Hannun Jarin Bunƙasa Ƙudurorin Muradun Ƙarni A Sifaniya
  • KADSEMA da IOM sun fara tantance ɓarnar da ambaliya ta yi a Kaduna
  • PLA Reshen Kudancin Kasar Ta Yi Sintiri Na Hadin Gwiwa A Tekun Kudancin Sin
  • Wang Yi Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Ministocin Harkokin Wajen Iran Da Isra’ila
  • Martanin sojojin Iran ga Isra’ila zai zama mafi muni idan aka ci gaba da kai hari (Pezeshkian)