Aminiya:
2025-06-06@16:26:21 GMT

Musulman Kudancin Kaduna sun yi taron addu’ar zaman lafiya

Published: 5th, June 2025 GMT

Al’ummar Musulmin yankin Kudancin Kaduna, sun shirya taron addu’a na musamman a sakatariyar karamar hukumar Sanga da ke Gwantu, Jihar Kaduna, kan neman zaman lafiya.

A yayin taron dai Babban Hafsan Tsaron Najeriya, Janar Christopher Gwabin Musa ya jaddada kudirin rundunar sojin Najeriya na dawo da zaman lafiya da tsaro a fadin kasar tare da yin kira ga ’yan kasa da su mara wa kokarin hadin kai da ci gaban kasa baya.

Janar Musa wanda Rear Admiral Ibrahim Aliyu Shettima ya wakilta, ya ce zaman lafiya shi ne ginshikin ci gaba da bunkasar kasa. Ya bukaci ’yan Najeriya baki daya, ba tare da la’akari da kabila ko addini ba, da su bayar da gudummawarsu wajen gina kasa.

Barazanar Yajin Aiki: Abuja da wasu jihohi 3 za su faɗa cikin duhu A shekara 25, na kashe tiriliyan 161 wajen inganta lafiya a Afirka – Bill Gates

Taron addu’ar dai an shirya shi ne da nufin karfafa zaman tare cikin fahimta da hadin kai tsakanin Musulmai da wadanda ba Musulmai ba daga kowace kabila a yankin, ya hada limamai da malamai daga kananan hukumomin Sanga, Kaura, Jema’a, Kachia, Kagarko, Kauru, Jaba, Kajuru da Chikun.

A jawabin sa, Babban Limamin Masallacin Juma’a na Jama’a kuma shugaban al’ummar Musulmin Kudancin Kaduna da suka gudanar da addu’ar, Sheikh Muhammad Kabir Qassim, ya nuna damuwarsa kan rikice-rikicen kabilanci da na addini da suka addabi yankin tsawon shekaru, lamarin da ya ce ya jawo asarar rayuka da dukiyoyi.

“Allah ya albarkaci Kudancin Kaduna da kasar noma mai albarka, wacce za a iya noma amfanin gona ba kawai don amfanin gida ba, har ma don fitar da shi kasashen waje. Amma babu wani ci gaba da za a samu idan babu zaman lafiya da tsaro,” in ji shi.

Ya yi kira ga daukacin mazauna yankin da su hade kai wajen dawo da martabar yankin da ta lalace tare da jaddada cewa hadin kai ne makamin jawo masu zuba jari da samar da damarmaki ga matasa.

Malamin ya nuna godiyarsa ga kokarin Janar Christopher Musa na dawo da zaman lafiya, yana mai cewa kudirinsa na tattaunawa da sulhuntawa zai taimaka wajen bude sabuwar hanyar ci gaba a Kudancin Kaduna da Najeriya baki daya.

Sauran masu jawabi a wajen taron sun jaddada muhimmancin hadin kan addinai da hadin gwiwar al’umma wajen magance matsalolin tsaro, tare da daukar alkawarin ci gaba da yin addu’o’i don samun zaman lafiya da hadin kai a fadin kasar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Zaman lafiya zaman lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

A shekara 25, na kashe tiriliyan 161 wajen inganta lafiya a Afirka – Bill Gates

Attajirin nan na duniya dan asalin kasar Amurka, Bill Gates, ya ce a shekara 25 da gidauniyarsa ta yi da kafuwa, ya kashe Dalar Amurka biliyan 100, kwatankwacin Naira tiriliyan 161 wajen inganta kiwon lafiya a nahiyar Afirka.

Attajirin ya bayyana hakan ne a Legas yayin wani taro da gidauniyarsa ta Gates Foundation ta shirya mai taken Goalkeepers, ranar Laraba.

Ya ce gidauniyar ta fara aiki ne a shekara ta 2000, kuma babban makasudinta shi ne ganin an rage samun mace-macen kananan yara a fadin duniya, musamman a Afirka.

Kotu ta aike da ɗan Tiktok gidan yari kan yin shigar mata a Kano NAJERIYA A YAU: Yadda Mayar Da Unguwa Mayanka Ke Shafar Lafiyar Al’umma

Bill Gates ya ce, “Ganin haka ne ya sa na yi nazari na ce shin mutane suna mayar da hankalinsu wajen ganin an samar wa da wasu ba’arin mutane magungunan da yankunansu ke bukata, alal misali a bangaren zazzabin cizon sauro (maleriya), sai na gano babu.

“Wannan ne ya kasance alkiblar gidauniyar Gates Foundation. Sama da kaso 70 cikin 100 na abin da nake kashewa, Dala biliyan 100, a bangaren lafiya na duniya suka tafi, kuma a tsawon wadannan shekaru 25, mun inganta alakarmu da kasashen Afirka da dama.

“A nan Najeriya muna da abokan hulda masu dadin mu’amala da suka fahimci hanyoyin da za mu bi wajen taimaka wa gwamnati,” in ji shi.

Ya kuma ce inganta harkar lafiya kan taimaka wa kasa wajen samun ci gaban tattalin arziki ta yadda za ta iya dogaro da kanta.

Mamallakin kamfanin Microsoft din ya kuma bayyana kyakkyawan fatan cewa za a samu raguwar yawan mace-macen kananan yara da kaso 50 cikin 100 daga adadin yara miliyan biyar din da yanzu haka ake samu a fadin duniya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sallah: Gwamna Inuwa ya yi kiran sadaukarwa da haɗin kai
  • Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba
  • A shekara 25, na kashe tiriliyan 161 wajen inganta lafiya a Afirka – Bill Gates
  • Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai
  • Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus
  • Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba
  • Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kai Hare-Hare Kan Yankunan Siriya Musamman Yankin Kudancin Kasar
  • Iran ta bukaci hadin kan al’ummar Lebanon wajen warware matsalolin kasar