Aminiya:
2025-09-18@02:19:24 GMT

Hajjin 2025: Kashi 79 na maniyyatan Najeriya sun isa Saudiyya – NAHCON

Published: 21st, May 2025 GMT

Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON), ta bayyana cewa ta yi jigilar maniyyatan Najeriya 32,549 zuwa Saudiyya don gudanar da Hajjin shekarar 2025.

Wannan adadi ya kai kashi 79.1 na jimillar waɗanda ake sa ran za su yi Hajji daga Najeriya.

DAGA LARABA: “Abba Al-Mustafa Ba Shi Da Hurumin Dakatar Da Fina-finanmu” Mun dakatar da sanya tallan magungunan gargajiya a fina-finai – Abba

Mai magana da yawun NAHCON, Fatima Sanda Usara, ta ce an kammala jigilar ne ta hanyar amfani da jirage 79 tun daga ranar 9 ga watan Mayu, 2025.

Rahoton Aminiya ya nuna cewa kimanin maniyyata 42,000 ne ake sa ran za su halarci Hajjin bana daga Najeriya.

Jihohi da dama kamar Adamawa da Filato sun kammala jigilar maniyyatansu baki ɗaya.

Jihohin Jigawa da Babban Birnin Tarayya, ana sa ran za su kammala jigilar nasu maniyyatan a yau.

Jihar Kwara, wadda ke da sauran maniyyata 137, za ta kammala kwashe su a a wani jirgi a Jihar Kano da yammacin yau.

Mahajjata daga Jihar Binuwai da yankin Kudu maso Kudu za su tashu tare a jirgi ɗaya da aka tanada da zai tashi a ranar 23 ga watan Mayu, wanda shi ne jirgi na ƙarshe daga yankin.

NAHCON, ta bayyana cewa ba a samu jirgi ko ɗaya da aka soke tashin ba tun da aka fara jigilar.

Sai dai an samu jinkirin tashin wasu jirage da gangan saboda bai wa otel-otel a Madina damar tsaftace ɗakunansu.

Wannan al’amari yana daga cikin tsare-tsaren gudanar da aikin Hajjin bana, musamman idan yawan mahajjatan ya ƙaru a lokaci ɗaya.

NAHCON, ta gode wa mahajjata da ɗaukacin al’ummar Najeriya bisa haƙuri, addu’o’i da goyon baya, tare da tabbatar da cewa za ta ci gaba da ƙoƙarin ganin an gudanar da aikin Hajjin cikin tsari da sauƙi ga kowa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: maniyyata Saudiyya

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar

Rahoton rashin fahimtar da aka fara yadawar, ya biyo bayan taron kwamitin zaman lafiya da kwantar da tarzoma na jihar, wanda Darakta Janar ya jagoranta a ranar 4 ga watan Satumba.

 

Rashin fahimtar sahihin sakamakon taron ya sa wasu suka rahoto cewa, kwamitin ya dakatar da Malamai daga yin wa’azi.

 

Sanarwar ta kara da cewa, “Hukumar ba ta da hurumin haramtawa Malaman Addinin Musulunci yin wa’azi sai dai in ya bayyana a fili an taka ƙa’idojin hukumar da ta shimfiɗa”.

 

A cewar Hukumar, an kira taron ne domin gabatar da fom din rijistar yin wa’azi ko Da’awah da kuma bin tsarin tantancewa.

 

Ta bayyana shirin a matsayin wani yunkuri na wayar da kan jama’a don “hana rashin fahimtar juna da kuma daƙile yaɗuwar wa’azin yaudara” a faɗin jihar Neja.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kammala Ziyarar Yini 3 A Ma’aikatar Kananan Hukumomin Jihar
  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa