Hajjin 2025: Kashi 79 na maniyyatan Najeriya sun isa Saudiyya – NAHCON
Published: 21st, May 2025 GMT
Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON), ta bayyana cewa ta yi jigilar maniyyatan Najeriya 32,549 zuwa Saudiyya don gudanar da Hajjin shekarar 2025.
Wannan adadi ya kai kashi 79.1 na jimillar waɗanda ake sa ran za su yi Hajji daga Najeriya.
DAGA LARABA: “Abba Al-Mustafa Ba Shi Da Hurumin Dakatar Da Fina-finanmu” Mun dakatar da sanya tallan magungunan gargajiya a fina-finai – AbbaMai magana da yawun NAHCON, Fatima Sanda Usara, ta ce an kammala jigilar ne ta hanyar amfani da jirage 79 tun daga ranar 9 ga watan Mayu, 2025.
Rahoton Aminiya ya nuna cewa kimanin maniyyata 42,000 ne ake sa ran za su halarci Hajjin bana daga Najeriya.
Jihohi da dama kamar Adamawa da Filato sun kammala jigilar maniyyatansu baki ɗaya.
Jihohin Jigawa da Babban Birnin Tarayya, ana sa ran za su kammala jigilar nasu maniyyatan a yau.
Jihar Kwara, wadda ke da sauran maniyyata 137, za ta kammala kwashe su a a wani jirgi a Jihar Kano da yammacin yau.
Mahajjata daga Jihar Binuwai da yankin Kudu maso Kudu za su tashu tare a jirgi ɗaya da aka tanada da zai tashi a ranar 23 ga watan Mayu, wanda shi ne jirgi na ƙarshe daga yankin.
NAHCON, ta bayyana cewa ba a samu jirgi ko ɗaya da aka soke tashin ba tun da aka fara jigilar.
Sai dai an samu jinkirin tashin wasu jirage da gangan saboda bai wa otel-otel a Madina damar tsaftace ɗakunansu.
Wannan al’amari yana daga cikin tsare-tsaren gudanar da aikin Hajjin bana, musamman idan yawan mahajjatan ya ƙaru a lokaci ɗaya.
NAHCON, ta gode wa mahajjata da ɗaukacin al’ummar Najeriya bisa haƙuri, addu’o’i da goyon baya, tare da tabbatar da cewa za ta ci gaba da ƙoƙarin ganin an gudanar da aikin Hajjin cikin tsari da sauƙi ga kowa.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan Najeriya sun fara begen Buhari saboda azabar Tinubu – Amaechi
Tsohon Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi, ya ce wahalhalu sun yi yawa a Gwamnatin Shugaba Bola Tinubu, wanda har ya sa mutane suka fara fatan dawowar tsohon Shugaba Muhammadu Buhari.
Yayin da yake magana a birnin Abuja, Amaechi ya ce Najeriya ta taɓarɓare matuƙa, inda ya ce sauyin gwamnati ne kawai zai magance matsaloli.
Gwamnatin Yobe ta rufe kasuwanni 3 saboda matsalar tsaro Ɗan wasan Liverpool, Diogo Jota, ya mutu a hatsarin mota“Farashi kayayyaki ya tashi sosai. Mutane ba za su iya siyan abinci ba. Babu kuɗi. Komai ya lalace,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa rayuwa ta yi tsanani har mutane sun fara tunawa da zamanin Buhari da muradin dawowarsa kan mulki.
“Yanzu mutane na so Buhari ya dawo. A Najeriya, kowace sabuwar gwamnati tana ƙara muni fiye da ta baya. Wannan shi ne dalilin da ya sa mutane ke ci gaba da tunanin gwamnatin da ta gabata,” in ji shi.
Amaechi ya bayyana cewa ya fice daga jam’iyyar APC a daren ranar Talata, inda yanzu ya koma jam’iyyar haɗaka ta ADC.
Ya ce tuni ya daina shiga harkokin jam’iyyar APC tun da daɗewa.
“Na fice daga APC jiya da daddare. Ban halarci taro ko guda ɗaha ba. Na taɓa gargaɗinsu, kuma na rubuta musu kada su sake gayyatata. Ba za ka zauna cikin ƙungiyar da yawancinsu suke satar dukiya ba, kai kuma ka yi shiru,” in ji shi.
Da aka tambaye shi me ya sa yake sukar gwamnatin da ya taɓa yi wa aiki, Amaechi ya ce matsalar Najeriya ba kawai shugabanci ba ne, sai an gyara tsarin gaba ɗaya.
Ya ce akwai bukatar fara shiri, ba kawai kafa jam’iyya ba, wanda zai haɗa ‘yan Najeriya su ƙwato ƙasarsu da hannunsu.
Amaechi ya kuma ce bai taɓa ganin Tinubu a matsayin mutum wanda ya cancanci ya mulki Najeriya ba.
“Na taɓa cewa Tinubu ba shi da ɗabi’u shugabanci. Har yanzu ra’ayina kenan,” in ji shi.
Ya soki yadda gwamnati ke tafiyar da tattalin arziƙi, musamman faɗuwar darajar Naira.
“Lokacin Buhari, dala tana kusa da Naira 460 ko Naira 500. Yanzu ta kai Naira 1580. Wannan ya fi kashi 100,” in ji shi.
Da aka tambaye shi ko wannan matsala ta Naira wata dabara ce ta gwamnati, Amaechi musanta hakan.
Ya ce, “Ko dabara ce ko akasin haka, duk wata gwamnati da ba ta damu da rayuwar mutane ba, ba za a ce dabara ce mai kyau ba.”
Tsohon Ministan Shari’a, Abubakar Malami, shi ma ya fice daga jam’iyyar APC, inda ya bu sahun Amaechi wajen komawa jam’iyyar ADC.
Ficewarsu da wasu manyan jiga-jigan siyasa na nuni da juyin juya hali kafin babban zaɓen 2027, yayin da jam’iyyar ADC ke neman zama sabuwar babbar jam’iyyar adawa a ƙasar.