Aminiya:
2025-06-14@13:08:22 GMT

Hajjin 2025: Kashi 79 na maniyyatan Najeriya sun isa Saudiyya – NAHCON

Published: 21st, May 2025 GMT

Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON), ta bayyana cewa ta yi jigilar maniyyatan Najeriya 32,549 zuwa Saudiyya don gudanar da Hajjin shekarar 2025.

Wannan adadi ya kai kashi 79.1 na jimillar waɗanda ake sa ran za su yi Hajji daga Najeriya.

DAGA LARABA: “Abba Al-Mustafa Ba Shi Da Hurumin Dakatar Da Fina-finanmu” Mun dakatar da sanya tallan magungunan gargajiya a fina-finai – Abba

Mai magana da yawun NAHCON, Fatima Sanda Usara, ta ce an kammala jigilar ne ta hanyar amfani da jirage 79 tun daga ranar 9 ga watan Mayu, 2025.

Rahoton Aminiya ya nuna cewa kimanin maniyyata 42,000 ne ake sa ran za su halarci Hajjin bana daga Najeriya.

Jihohi da dama kamar Adamawa da Filato sun kammala jigilar maniyyatansu baki ɗaya.

Jihohin Jigawa da Babban Birnin Tarayya, ana sa ran za su kammala jigilar nasu maniyyatan a yau.

Jihar Kwara, wadda ke da sauran maniyyata 137, za ta kammala kwashe su a a wani jirgi a Jihar Kano da yammacin yau.

Mahajjata daga Jihar Binuwai da yankin Kudu maso Kudu za su tashu tare a jirgi ɗaya da aka tanada da zai tashi a ranar 23 ga watan Mayu, wanda shi ne jirgi na ƙarshe daga yankin.

NAHCON, ta bayyana cewa ba a samu jirgi ko ɗaya da aka soke tashin ba tun da aka fara jigilar.

Sai dai an samu jinkirin tashin wasu jirage da gangan saboda bai wa otel-otel a Madina damar tsaftace ɗakunansu.

Wannan al’amari yana daga cikin tsare-tsaren gudanar da aikin Hajjin bana, musamman idan yawan mahajjatan ya ƙaru a lokaci ɗaya.

NAHCON, ta gode wa mahajjata da ɗaukacin al’ummar Najeriya bisa haƙuri, addu’o’i da goyon baya, tare da tabbatar da cewa za ta ci gaba da ƙoƙarin ganin an gudanar da aikin Hajjin cikin tsari da sauƙi ga kowa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: maniyyata Saudiyya

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Su A Najeriya

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Rashin aikin yi na daya daga cikin manyan kalubalen da najeriya ke fuskanta a wannan lokaci, musamman la’akari da yanda ake cigaba da samun matasa dake da karfi a jika amma babu aikin yi.

Hukumar kididdiga ta kasa ta fitar da bayanan dake baiyana cewa rashin aikin yi ya karu a najeriya da kaso 5.3 a farkon wannan shekarar, kazalika binciken ya baiyana cewa wadanda basu yi karatu mai zurfi ba sun fi wadanda suka yi karatu mai zurfi samun aikin yi.

NAJERIYA A YAU: 12 Ga Yuni: Me Ranar Dimokuraɗiyya Ke Nufi Ga Talakan Najeriya? DAGA LARABA: Dalilan Rashin Jituwa Tsakanin Marasa Lafiya Da Jami’an Kiwon Lafiya

Wadansu dalilai ne ke kara kawo rashin aikin yi a Najeriya?
Wadansu hanyoyi za’a bi wajen magance rashin aikin yi?
Wadannan da ma wasu tambayoyi na cikin batutuwan da Shirin Najeriya A Yau zai yi duba akai.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025
  • Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
  • Hajjin 2025: Yadda Alhazan Nijeriya 7 Suka Rasa Rayukansu A Saudi Arabiya
  • NAJERIYA A YAU: Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Su A Najeriya
  • Mutum ɗaya ya tsira da ransa cikin 242 a hatsarin jirgin India
  • De Bruyne Ya Kammala Komawa Napoli Bayan Barin Man City
  • Hajjin 2025: Jihohi 11 sun kashe N6.2bn wajen tallafa wa Alhazai
  • Yadda Kasar Sin Ta Zo Da Sabon Salon Zamanantar Da Sashen Jigilar Kayayyaki
  • Manchester City Ta Kammala Daukar Rayan Cherki Daga Lyon