Jihar Jigawa da Babban Birnin Tarayya su ma za su kammala nasu a yau.

Jihar Kwara na da sauran mahajjata 137 kuma za su tashi a jirgin Max Air a Kano da rana.

Mahajjatan daga Jihar Binuwai za su haɗe da waɗanda ke yankin Kudu maso Kudu domin tafiya tare a jirgi guda da zai tashi a ranar 23 ga watan Mayu, wanda zai zama jirgi na ƙarshe daga wannan yanki.

A cewar Fatima Sanda Usara, Babbar Daraktar Watsa Labarai a NAHCON, ba a soke jirgi ko ɗaya ba tun lda aka fara jigilar maniyyatan.

NAHCON ta gode wa mahajjata da al’ummar Nijeriya baki ɗaya bisa haƙuri, addu’o’i da goyon baya, tare da tabbatar da cewa za ta ci gaba da aiki tuƙuru domin ganin an gudanar da aikin Hajji cikin tsari da sauƙi ga kowa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Saudiyya

এছাড়াও পড়ুন:

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

Kungiyar Kananan Hukumomin Nijeriya (ALGON) reshen Jihar Kaduna, ta mika sakon taya murna ga Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, bisa lambar karramawa ta CON da shugaban kasa ya yi masa ado da ita, wacce ke matsayin wata alamar girmamawa a Jamhuriyyar Nijeriya ta Hudu. Wannan karramawar, wata alama ce a sarari ga sadaukarwar mai girma gwamna, da gagarumin nasarorin da ya samu a hukumance, da kuma jagoranci mai tsari da yake kai domin ci gaba da tsara tafiyar dimokuradiyyar kasa. Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8) Wannan na kunshe ne a cikin wata takarda dauke da sa hannun sakataren yada labarai na ALGON, Muhammad Lawal Shehu a ranar Juma’a 4 ga watan Yulin 2025. Sanarwar ta kara da cewa, a lokacin da yake Sanata mai wakiltar Kaduna ta tsakiya, ya taka muhimmiyar rawa inda ya dauki nauyin kudirori masu muhimmanci wadanda suka karfafa tsaron kasa, inganta yaki da cin hanci da rashawa, da kuma sabunta muhimman tsare-tsare na doka. Ta hanyar ba da fifikon ci gaban karkara, farfado da aikin noma, fadada hanyoyin samar da lafiya mai inganci, inganta rayuwar al’umma, da baiwa kananan hukumomi damar gudanar da ayyukansu yadda ya kamata, Gwamna Uba Sani ya nuna jagoranci mai hangen nesa wanda ke daukaka rayuwar al’umma a fadin jihar Kaduna. ALGON reshen jihar Kaduna tana taya al’ummar jihar Kaduna da Nijeriya baki daya wajen murnar wannan gagarumin nasara da aka samu tare da addu’ar Allah ya kara basira da nasara a kan hidimar da yake yi wa jihar da kasa baki daya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Ana raɗe-raɗin Sanata Lamiɗo zai fice daga APC zuwa ADC
  • ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa
  • Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
  • Mutanen unguwa sun kama masu ƙwacen waya a Kano
  • Shirin Tinubu Kan Kiwon Dabbobi Zai Samar Da Ayyukan Yi Miliyan 5 Ga Matasa – Jega
  • Haɗarin Da Ke Ƙunshe Da Jin Ɓangare Ɗaya Na Labari
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato
  • Shugaban Amurka Yace Yana Jirin Hamas Cikin Sa’o’i 24 Masu Zuwa Don Tsagaita Wuta Na Kwanaki 60
  • Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC
  • Gwamnatin Yobe ta rufe kasuwanni 3 saboda matsalar tsaro