Jigajigan Jihar Kebbi Sun Bukaci Hadin Kan ‘Ya’yan Jam’iyyar APC
Published: 21st, May 2025 GMT
Sanatocin jihar Kebbi guda uku da suka sauya sheka daga jam’iyyar PDP zuwa APC, tare da Ministan Kasafin Kudi da Tsare-tsaren Tattalin Arziki, Sanata Atiku Bagudu, sun bukaci hadin kai tsakanin mambobin jam’iyyar domin samun nasara a zaben 2027.
Sanata Adamu Aliero, wanda ya yi jawabi a madadin sauran sanatocin, ya bayyana haka a wani taron jiga-jigan jam’iyyar APC da reshen jihar ya shirya a Birnin Kebbi.
Sanata Aliero ya ce sauya shekar su daga jam’iyyar adawa PDP zuwa jam’iyya mai mulki APC, domin cigaban jihar ne gaba ɗaya.
A cewarsa, akwai ayyuka da dama da za a aiwatar a jihar Kebbi, amma saboda wakilan jihar a majalisa suna jam’iyyar adawa, aka hana jihar damar cin gajiyar wadannan ayyukan.
Game da matsalar tsaro a ƙasar, Sanata Aliero ya bayyana cewa gwamnati na kokarin shawo kan kalubalen tsaro da kuma rage talauci a ƙasar.
Ministan Kasafin Kudi da Tsare-tsaren Tattalin Arziki, Sanata Atiku Bagudu, ya bukaci magoya bayan APC da su mara wa Shugaba Bola Tinubu da Gwamna Nasiru Idris baya domin samun nasara a wa’adinsu na biyu a shekarar 2027.
Gwamnan jihar Kebbi, Nasiru Idris, ya nuna godiyarsa bisa yadda mambobin jam’iyyar da manyan baki suka halarci taron.
Ya kuma bukaci hadin kai daga mambobin jam’iyyar domin tabbatar da nasarar jam’iyyar daga matakin shugaban kasa har zuwa gwamnoni da ‘yan majalisun tarayya da na jiha a zaben 2027.
Cikin wadanda suka halarci taron akwai Ministan Kasafin Kudi da Tsare-tsaren Tattalin Arziki, Sanata Atiku Bagudu, Sanata Abdullahi Yahaya, Sanata Musa Maidoki, mambobin majalisar tarayya da na jiha, tsohon gwamnan Kebbi Sa’idu Nasamu Dakingari, Daraktan Hukumar NAMA da na HYPERDEC, Sakataren Tsare-tsaren Jam’iyyar APC, da sauransu.
Daga Abdullahi Tukur
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Tsare tsaren jihar Kebbi
এছাড়াও পড়ুন:
An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkuku
’Yan sanda a jihar Legas sun kama wani tsohon fursuna tare da wasu mutum biyu bisa zargin hannu a jerin laifukan fashi da yankan aljihu a jihar kwana biyar da fitowa daga kurkuku.
Tsohon fursunan mai shekaru 25 da haihuwa, Segun Kolawole, an kama shi ne bayan kwana biyar da aka sako shi daga cibiyar gyaran hali ta Kirikiri, a jihar Legas.
Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure Juventus ta ɗauki tsohon kociyan Italiya, Luciano SpalletiSauran wadanda aka kama tare da shi sun haɗa da Sodiq Isa mai shekaru 27 da Adekanmbi Ganiu mai shekaru 21.
Rahotanni sun nuna cewa an kama waɗanda ake zargin ne bisa laifukan yankan aljihun mutane da sauran laifukan sata a sassa daban-daban na jihar.
Mai magana da yawun ’yan sandan jihar, SP Abimbola Adebisi, ta tabbatar da cafke Kolawole, inda ta ce an kama shi da misalin ƙarfe 8 na safiyar Talata a kasuwar Oshodi, bayan jami’ai sun lura da motsinsa da ya zama abin zargi.
Adebisi ta ce an same shi da tsabar kuɗi ₦80,000 da wayar Infinix Note 40 Pro, waɗanda aka gano daga wani fashi da ya aikata a Opebi, inda ake zargin ya saci ₦200,000 da wayar daga hannun wani ɗan kasuwa da ke barci.
“Bincike ya ƙara tabbatar da cewa ya riga ya sayi sabbin kaya da takalma da wani ɓangare na kuɗin da ya sata, waɗanda suma aka kwato su daga hannunsa,” in ji ta.
Haka kuma, a wani samame daban da aka gudanar da misalin ƙarfe 5 na yamma a ranar Juma’a, jami’an RRS sun kama Sodiq Isa da Adekanmbi Ganiu bisa zargin yunkurin satar wayoyin hannu daga hannun fasinjoji a sassa daban-daban na Legas.