Sanatocin jihar Kebbi guda uku da suka sauya sheka daga jam’iyyar PDP zuwa APC, tare da Ministan Kasafin Kudi da Tsare-tsaren Tattalin Arziki, Sanata Atiku Bagudu, sun bukaci hadin kai tsakanin mambobin jam’iyyar domin samun nasara a zaben 2027.

Sanata Adamu Aliero, wanda ya yi jawabi a madadin sauran sanatocin, ya bayyana haka a wani taron jiga-jigan jam’iyyar APC da reshen jihar ya shirya a Birnin Kebbi.

Sanata Aliero ya ce sauya shekar su daga jam’iyyar adawa PDP zuwa jam’iyya mai mulki APC, domin cigaban jihar ne gaba ɗaya.

A cewarsa, akwai ayyuka da dama da za a aiwatar a jihar Kebbi, amma saboda wakilan jihar a majalisa suna jam’iyyar adawa, aka hana jihar damar cin gajiyar wadannan ayyukan.

Game da matsalar tsaro a ƙasar, Sanata Aliero ya bayyana cewa gwamnati na kokarin shawo kan kalubalen tsaro da kuma rage talauci a ƙasar.

Ministan Kasafin Kudi da Tsare-tsaren Tattalin Arziki, Sanata Atiku Bagudu, ya bukaci magoya bayan APC da su mara wa Shugaba Bola Tinubu da Gwamna Nasiru Idris baya domin samun nasara a wa’adinsu na biyu a shekarar 2027.

Gwamnan jihar Kebbi, Nasiru Idris, ya nuna godiyarsa bisa yadda mambobin jam’iyyar da manyan baki suka halarci taron.

Ya kuma bukaci hadin kai daga mambobin jam’iyyar domin tabbatar da nasarar jam’iyyar daga matakin shugaban kasa har zuwa gwamnoni da ‘yan majalisun tarayya da na jiha a zaben 2027.

Cikin wadanda suka halarci taron akwai Ministan Kasafin Kudi da Tsare-tsaren Tattalin Arziki, Sanata Atiku Bagudu, Sanata Abdullahi Yahaya, Sanata Musa Maidoki, mambobin majalisar tarayya da na jiha, tsohon gwamnan Kebbi Sa’idu Nasamu Dakingari, Daraktan Hukumar NAMA da na HYPERDEC, Sakataren Tsare-tsaren Jam’iyyar APC,  da sauransu.

 

Daga Abdullahi Tukur 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Tsare tsaren jihar Kebbi

এছাড়াও পড়ুন:

ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe

Ƙungiyar shugabannin ƙananan hukumomin Jihar Yobe (ALGON) ta karrama Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, da lambar yabo ta karramawa bisa himmar ayyukan raya ƙasa da gwamnatinsa ke gudanarwa a faɗin jihar.

Karramawar, wacce aka bayyana a matsayin irinta ta farko a tarihin Jihar Yobe, shugabannin ƙananan hukumomi 17 na jihar suka ba da ita ga gwamna.

Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno

Da yake jawabi, shugaban ƙungiyar ALGON a Jihar Yobe, kuma shugaban ƙaramar hukumar Damaturu, Alhaji Bukar Adamu, ya yaba da yadda Gwamna Buni yake gudanar da harkokin mulki na bai ɗaya. Ya ce nasarorin da aka samu sun haɗa da fannoni na ilimi, noma, kiwon lafiya, kasuwanci, da samar da ababen more rayuwa.

“Babu wani sashe a jihar da aka bari a baya a cikin ayyukan ci gaban da Gwamna Mai Mala Buni ke aiwatarwa,” in ji Adamu.

A nasa martanin, Gwamna Buni, wanda mataimakinsa, Alhaji Idi Barde Gubana, ya wakilta, ya karɓi karramawar a matsayin “hanyar mayar da martani mai ƙarfi” da ke tabbatar da tasirin gwamnatinsa a matakin farko.

Ya kuma yi alƙawarin ci gaba da ƙoƙarin kai Yobe matsayin jiha da za ta iya gogayya da takwarorinta a fagen ci gaban ƙasa.

Wakilinmu ya ruwaito cewa taron ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, ’yan siyasa daga ciki da wajen jihar, da kuma sarakunan gargajiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kammala Ziyarar Yini 3 A Ma’aikatar Kananan Hukumomin Jihar
  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • An tattauna yadda za a inganta walwalar malamai a Gombe
  • Tinubu ya janye dokar ta-ɓaci da ya sanya a Ribas
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Iran da Saudiyya sun bukaci hadin Musulmi game da halin da ake ci a yankin
  • ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar