Sanatocin jihar Kebbi guda uku da suka sauya sheka daga jam’iyyar PDP zuwa APC, tare da Ministan Kasafin Kudi da Tsare-tsaren Tattalin Arziki, Sanata Atiku Bagudu, sun bukaci hadin kai tsakanin mambobin jam’iyyar domin samun nasara a zaben 2027.

Sanata Adamu Aliero, wanda ya yi jawabi a madadin sauran sanatocin, ya bayyana haka a wani taron jiga-jigan jam’iyyar APC da reshen jihar ya shirya a Birnin Kebbi.

Sanata Aliero ya ce sauya shekar su daga jam’iyyar adawa PDP zuwa jam’iyya mai mulki APC, domin cigaban jihar ne gaba ɗaya.

A cewarsa, akwai ayyuka da dama da za a aiwatar a jihar Kebbi, amma saboda wakilan jihar a majalisa suna jam’iyyar adawa, aka hana jihar damar cin gajiyar wadannan ayyukan.

Game da matsalar tsaro a ƙasar, Sanata Aliero ya bayyana cewa gwamnati na kokarin shawo kan kalubalen tsaro da kuma rage talauci a ƙasar.

Ministan Kasafin Kudi da Tsare-tsaren Tattalin Arziki, Sanata Atiku Bagudu, ya bukaci magoya bayan APC da su mara wa Shugaba Bola Tinubu da Gwamna Nasiru Idris baya domin samun nasara a wa’adinsu na biyu a shekarar 2027.

Gwamnan jihar Kebbi, Nasiru Idris, ya nuna godiyarsa bisa yadda mambobin jam’iyyar da manyan baki suka halarci taron.

Ya kuma bukaci hadin kai daga mambobin jam’iyyar domin tabbatar da nasarar jam’iyyar daga matakin shugaban kasa har zuwa gwamnoni da ‘yan majalisun tarayya da na jiha a zaben 2027.

Cikin wadanda suka halarci taron akwai Ministan Kasafin Kudi da Tsare-tsaren Tattalin Arziki, Sanata Atiku Bagudu, Sanata Abdullahi Yahaya, Sanata Musa Maidoki, mambobin majalisar tarayya da na jiha, tsohon gwamnan Kebbi Sa’idu Nasamu Dakingari, Daraktan Hukumar NAMA da na HYPERDEC, Sakataren Tsare-tsaren Jam’iyyar APC,  da sauransu.

 

Daga Abdullahi Tukur 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Tsare tsaren jihar Kebbi

এছাড়াও পড়ুন:

Gini ya kashe Ba’indiye a Zariya

Wani ɗan ƙasar Indiya, Harpal Singh, ya rasa ransa bayan katangar rumbun ajiya ta kamfanin ATCO da ke Zariya ta rushe a kansa ranar Talata.

Mutumin dai daya ne daga cikin ma’aikatan kamfanin da ke unguwar Cikaji a karamar hukumar Sabon Gari ta jihar Kaduna.

Hajjin 2025: Jihohi 11 sun kashe N6.2bn wajen tallafa wa Alhazai Ana shirin mayar da rantsar da Shugaban Nijeriya zauren majalisa

Wani ma’aikacin kamfanin da ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyanawa Aminiya cewa Ba’indiyen ya gamu da ajalinsa ne da misalin ƙarfe 10:30 na daren Talata, bayan tashin guguwa gabanin a fara ruwan sama.

Ma’aikacin ya ce sai dai ba a san musabbabin rushewar katangar ba, sakamakon lokacin da lamarin ya faru ba lokacin aiki ba ne kuma ba a san abin da ya kai mamacin wurin ba.

Tuni dai aka garzaya da gawar marigayin Harpal ɗakin adana gawarwaki na Asibitin Koyarwa na Jami’ar Ahmadu Bello da ke Shika Zariya.

Sai dai wakilin namu ya yi ta ƙokarin tuntuɓar Kakakin Rundunar ’Yan Sandar jihar Kaduna DSP Mansur Hassan kan lamarin, amma wayarsa ba ta shiga.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya
  • Iran : harin da Isra’ila ta kai ‘ ayyana yaki’ ne_ Araghchi
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
  • Hajjin 2025: Yadda Alhazan Nijeriya 7 Suka Rasa Rayukansu A Saudi Arabiya
  • Sojoji Sun Kashe Auta, Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda Da Wasu 13 a Jihar Zamfara
  • Zamfara: APC Za Ta Maka PDP A Kotu Kan Zargin Matawalle Da Hannu A Satar Mutane
  • An kashe jaririn wata 9 da wasu 3 a Filato
  • Gini ya kashe Ba’indiye a Zariya
  • Birnin Los Angeles Na Amurka Ya Rikice Yadda Ake Dauki Ba Dadi Tsakanin Al’ummar Jihar Da Jami’an Tsaro
  • He Lifeng Ya Bukaci Amurka Da Ta Warware Takaddamar Cinikayya Da Sin Ta Hanyar Tattaunawa Da Hadin Gwiwa