HausaTv:
2025-07-05@17:45:00 GMT

Gaza : Birtaniya ta dakatar da tattaunawar cinikayya da Isra’ila

Published: 21st, May 2025 GMT

Birtaniya ta dakatar da tattaunawar cinikayya cikin ‘yanci da Isra’ila, bayan firaminista Keir Starmer ya ce ya kadu da yadda Isra’ila ke ci gaba da yakin Gaza.

Sakataren harkokin wajen Birtaniya, David Lammy ya bayyana matakin jingine batun ciniki tsakanin Birtaniya da Isra’ila, ya kuma nemi jakadan Isra’ila a Birtaniya ya bayyana a gaban Ofishin Lamurran Cikin Gidan kasar domin ya amsa tambayoyi game da yakin da kasarsa ke ci gaba da yi a Gaza.

Mista Lammy ya ce ministan da ke lura da lamurran da suka shafi gabas ta tsakiya na Birtaniya, Hamish Falconer, zai sanar da Hotovely cewa, “hana shigar da kayan agaji zuwa Gaza har na tsawo makonni 11 mugunta ce kuma babu hujjar yin hakan” .

” A yanzu muna ci gaba da shiga wani mummunan yanayi game da wannan yaki” in ji shi.

Lammy ya kara da cewa yakin da ake yi a Gaza ya haifar da nakasu ga alakar da ke tsakanin Birtaniya da Isra’ilan, sannan ya ce gwamnatin Birtaniya za ta sa takunkumi ga mutane uku ‘yan Isra’ilan wadanda ke da hannu wajen tayar da mazauna Gaza daga muhallansu.

Wannan na zuwa ne bayan da rundunar sojin Isra’ila ta sanar a makon da ya gabata cewa za ta zafafa kai hare-hare a Gaza.

A wani lamari da za’a ce irinsa ne na farkoA ranar Litinin, a cikin wata sanarwar hadin gwiwa, kasashen Canada, Faransa, da Birtaniya sun yi Allah wadai da fadada yakin da Isra’ila ke yi a Gaza tare da yin kira ga gwamnatin kasar da ta dage takunkumin da ta hana shigar da kayayyakin jin kai a Zirin.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: da Isra ila

এছাড়াও পড়ুন:

 Sheikh Na’im Kassim:  Ba Za Mu Taba Mika Makamanmu Ga Makiya Ba

Babban magatakardar kungiyar Hizbullah ta kasar Lebanon ya bayyana cewa; Batun makamin kungiyar ta Hizbullah na cikin gida ne, don haka ba za su taba mika makamansu ga abokan gaba HKI ba.

 Sheikh Na’im Kassim Wanda ya gabatar da jawabi a jiya Laraba da dare a yayin tarukan Ashura, ya bayyana cewa; Ba za mu taba lamunta da a sa mu cikin kaskanci ba, ba kuma za mu mika kasarmu ba, ko kuma mu aminta da barazana daga wani mahaluki akan mu ja da baya.

Sheikh Na’im Kassim ya kuma ce; Tattaunawar da ake yi akan makaman Hizbullah wani sha’ani ne na cikin gida, za kuma a warware batun ne a cikin gida, don ba shi da alaka da Isra’ila, ko kuma ta zama mai tsoma baki a tattaunawar da ake yi.

Babban magatakardar kungiyar ta Hizbullah ya kara da cewa: Isra’ila ce, mai wuce gona da iri, kuma ta keta tsagaita wuta fiye da 3700,don haka wajibi ne a tilasta mata ta yi aiki da yarjejeniyar da ta kulla da gwamnatin Lebanon.”

Sheikh Na’im Kassim ya yi ishara da cewa; Isra’ila babbar barazana ce kuma hatsari ga musulmi, da kiristoci da kuma Yahudawa a Palasdinu, Lebanon, Masar, Syria, Jordan da wannan yankin da ma duniya baki daya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Iran Ta Jaddada Wajabcin Hukunta Gwamnatin Mamayar Isra’ila Dangane Da  Ta’addancinta Kan Iran
  • Kungiyar Hamas Ta Sanar Da Matsayinta Kan Shirin Dakatar Da Bude Tsakaninta Da Gwamnatin Mamayar Isra’ila
  • Ma’aikatan MDD Masu Kula Da Ayyukan Makamashin Nukliya Na Kasar Iran Su Fice daga Kasar
  • Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Kashe Masu Neman Karbar Kayan Agaji A Gaza
  • Ben Gafir Ya Bukaci Gwamnatin HKI Ta Mamaye Yankin Gaza Gaba daya
  •  Sheikh Na’im Kassim:  Ba Za Mu Taba Mika Makamanmu Ga Makiya Ba
  • Mujallar “Foreign Policy”Ta Amurka: Isra’ila Ba Ta Yi Nasara A Yaki Da Iran Ba
  • Amurka ta dakatar da bai wa Ukraine tallafin makamai
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Yi Luguden Bama-Bamai Kan Falasdinawa Da Suka Janyo Shahada Da Jikkata