Aminiya:
2025-06-14@01:51:14 GMT

ISWAP ta kashe manoma sama da 50 a Borno

Published: 18th, May 2025 GMT

Aƙalla manoma 50 ne suka rasu, sakamakon wani mummunan hari da ‘yan ta’addan ISWAP suka kai garin Malam Karanti da ke Ƙaramar Hukumar Kukawa, a jihar Borno.

Majiyoyi sun ce mayaƙan sun afka wa manoma yayin da suke noma da kamun kifi, duk da cewar suna biyan haraji kafin yin noma.

Tinubu ya isa Rome don rantsar da sabon Fafaroma Tsafta a gidan aure: Abubuwan da kowace mace ya kamata ta sani

“Sun mallaki takardun izini daga kwamandan ISWAP da ke kula da yankin Malam Karanti har zuwa Dawashi.

Sun jima suna samun kariya daga Amir Akilu, wanda shi ne kwamandan yankin,” in ji wani mazaunin yankin.

Sai dai harin ya faru ne a lokacin da kwamandan bai kasance a yankin ba, inda wasu daga cikin mayaƙan suka zargi manoman da leƙen asiri, inda suka ce suna taimaka wa abokan gabansu.

Wannan ne dalilin da ya sa suka kai harin.

Wani wanda ya tsallake rijiya da baya a harin ya ce: “Mun fara girbin wake ne lokacin da suka zo. Sun kewaye mu, suka ce duk wanda ya yi yunƙurin tserewa za su harbe shi.

“Wasu daga cikinmu sun yanke shawarar guduwa duk da hakan. Sun kashe sama da mutum 50, da yawa daga cikinsu an yanka su.

“Sannan sun kama wasu daga cikinmu. Yau ma sun je Dawashi sun kashe mutane, amma ba a san adadin waɗanda suka kashe ba tukuna.”

Gwamnati da hukumomin tsaro ba su fitar da wata sanarwa dangane da wannan mummunan hari ba.

Wannan hari ya zo cikin watanni biyar kacal bayan wani makamancin sa da aka kai ƙauyen Dumba, inda manoma aƙalla 40 suka rasa rayukansu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Boko Haram hari ISWAP

এছাড়াও পড়ুন:

Manchester City Ta Kammala Daukar Rayan Cherki Daga Lyon

Cherki ya buga wasansa na farko a Lyon yana da shekara 16 a watan Oktoban 2019 kuma ya bar kungiyar inda ya ci kwallaye 29 sannan ya taimaka aka jefa 45 a wasanni 185 da ya bugawa kungiyar ta Faransa. Cherki ya wakilci kasar Faransa kuma ya lashe lambar azurfa a gasar Olympics da aka gudanar a birnin Paris na kasar Faransa a bara.

 

Daraktan kwallon kafa na Manchester City, Hugo Viana ya ce, “Babu shakka a yanzu Cherki yazo inda ya dace kuma zai cigaba a karkashin jagorancin Guardiola, kuma na yi imani zai iya zama babban dan wasa a duniya tare da goyon bayan abokan wasa da masu horarwa”.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • Jagoran Juyin Musulunci Na Iran Ya Nada Sabbin Kwamandojin Soja Da Dakarun Kare Juyin Musulunci
  • Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci
  • Harin Isra’ila a kan Iran ya jefa yankin Gabas ta Tsakiya cikin zama dar-dar
  • Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara
  • An ciro gawarwaki sama da 200 daga jirgin Indiya da ya yi hatsari
  •   Bokoharam Ta Kashe Sojojin Kamaru Ta Hanyar Amfani Da Jirgin Sama Maras Matuki
  • Manchester City Ta Kammala Daukar Rayan Cherki Daga Lyon
  • Sojojin Yemen Sun Kai Farmakin Kan Tashar Jiragen Sama Na Bengerion A HKI
  • Rikicin Filato: An sake kone gidaje 96 a Mangu