Aminiya:
2025-09-18@01:15:35 GMT

ISWAP ta kashe manoma sama da 50 a Borno

Published: 18th, May 2025 GMT

Aƙalla manoma 50 ne suka rasu, sakamakon wani mummunan hari da ‘yan ta’addan ISWAP suka kai garin Malam Karanti da ke Ƙaramar Hukumar Kukawa, a jihar Borno.

Majiyoyi sun ce mayaƙan sun afka wa manoma yayin da suke noma da kamun kifi, duk da cewar suna biyan haraji kafin yin noma.

Tinubu ya isa Rome don rantsar da sabon Fafaroma Tsafta a gidan aure: Abubuwan da kowace mace ya kamata ta sani

“Sun mallaki takardun izini daga kwamandan ISWAP da ke kula da yankin Malam Karanti har zuwa Dawashi.

Sun jima suna samun kariya daga Amir Akilu, wanda shi ne kwamandan yankin,” in ji wani mazaunin yankin.

Sai dai harin ya faru ne a lokacin da kwamandan bai kasance a yankin ba, inda wasu daga cikin mayaƙan suka zargi manoman da leƙen asiri, inda suka ce suna taimaka wa abokan gabansu.

Wannan ne dalilin da ya sa suka kai harin.

Wani wanda ya tsallake rijiya da baya a harin ya ce: “Mun fara girbin wake ne lokacin da suka zo. Sun kewaye mu, suka ce duk wanda ya yi yunƙurin tserewa za su harbe shi.

“Wasu daga cikinmu sun yanke shawarar guduwa duk da hakan. Sun kashe sama da mutum 50, da yawa daga cikinsu an yanka su.

“Sannan sun kama wasu daga cikinmu. Yau ma sun je Dawashi sun kashe mutane, amma ba a san adadin waɗanda suka kashe ba tukuna.”

Gwamnati da hukumomin tsaro ba su fitar da wata sanarwa dangane da wannan mummunan hari ba.

Wannan hari ya zo cikin watanni biyar kacal bayan wani makamancin sa da aka kai ƙauyen Dumba, inda manoma aƙalla 40 suka rasa rayukansu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Boko Haram hari ISWAP

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet

Hukumar kula da al’adun gargajiya ta kasar Sin ta sanar a yau cewa, an gano wani dutsen da aka yi sassaka kan sa a kan tsaunin Qinghai-Tibet, wanda ya kasance irinsa daya tilo na daular Qin da har yanzu ke mazauninsa na asalin, kuma a wuri mafi tsawo.

Dutsen wanda ke arewacin bakin tabkin Gyaring na gundumar Maduo, dake arewa maso yammacin lardin Qinghai, na wuri mai tsawon mita 4,300.

Gano dutsen na tattare da wata muhimmiyar daraja ga tarihi da fasaha da kimiyya. Sarki Qinshihuang na daular Qin ne ya fara hada kan kasar Sin. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 
  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • Iran Ta Bukaci IAEA Tayi Tir Da Harin Da Isra’ila Ta Kai A Tashoshin Nukiyarta.
  • ’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote
  • Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara