Aminiya:
2025-05-18@01:23:44 GMT

Tinubu ya isa Rome don rantsar da sabon Fafaroma

Published: 17th, May 2025 GMT

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya isa birnin Rome na Ƙasar Italiya domin halartar bikin rantsar da sabon Fafaroma, Leo na XIV.

Za a gudanar da bikin ne a wajen wani taron addu’a da ake kira “solemn mass” a ranar Lahadi, 18 ga watan Mayu.

Crystal Palace ta lashe kofin FA na farko a tarihinta Ban sauya sheƙa ba, makircin siyasa da ƙarya ake min — Kwankwaso 

An tarbi Shugaba Tinubu a filin jirgin sojin Mario De Bernardo, inda jakadiyar Najeriya, Bianca Odumegwu-Ojukwu, da jami’an diflomasiyya daga Vatican da ofishin jakadancin Najeriya suka tarbe shi.

Tinubu ya samu gayyata ta musamman daga Sakatare Janar na Vatican, Cardinal Pietro Parolin.

A cikin wasiƙar gayyatar, Fafaroma Leo XIV ya bayyana cewa ya ga dacewar Shugaba Tinubu ya halarci bikin rantsar da shi.

Fafaaroma ya ƙara da cewa Najeriya tana da muhimmanci a gare shi domin ya taɓa aiki a ofishin jakadancin Vatican da ke Legas a shekarun 1980.

Shugaba Tinubu na tare da wasu manyan shugabannin cocin Katolika daga Najeriya ciki har da Archbishop Lucius Ugorji na Owerri, Archbishop Ignatius Kaigama na Abuja, Archbishop Alfred Martins na Legas, da Bishop Mathew Hassan Kukah daga Sakkwato.

Sun tafi Rome ne, domin nuna goyon baya da wakiltar Najeriya a bikin rantsar da sabon Fafaroma.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Bikin Rantsuwa Fafaroma Leo Sabon Fafaroma

এছাড়াও পড়ুন:

Mutum ɗaya ya rasu a rikicin manoma da makiyaya a Yobe

Wani rikici da ya ɓarke tsakanin manoma da makiyaya a ƙauyen Chikuriwa da ke Ƙaramar Hukumar Nangere a Jihar Yobe, ya yi sanadin mutuwar mutum ɗaya tare da jikkata wasu.

Rahotanni sun nuna cewa rikicin ya faru ne da yammacin ranar Litinin, 13 ga watan Mayu, 2025 bayan da wani makiyayi ya shigar da shanunsa cikin gonar wani manomi, abin da ya tayar da rikici.

Yajin aiki: Jami’ar KASU ta shiga rudani BUA ya yi alkawarin karya farashin shinkafa

A lokacin da rigimar ta ɓarke, an harbi wani manomi mai suna Babayo Maina Osi da kibiya a goshinsa, wanda hakan ya jikkata shi.

Wata majiya daga ƙauyen ta ce rikicin ya ƙazanta sosai har ya rikiɗe zuwa faɗa tsakanin manoma da makiyaya.

A lokacin wannan faɗa ne aka harbi wani mutum mai suna Usman Mohammed, mai shekara 35 da kibiya, wanda daga bisani ya rasu a Babban Asibitin Nangere.

Jami’an tsaro sun isa wajen domin daƙile rikicin da kuma hana ya ƙara rincaɓewa.

Rahoton ya bayyana cewa an ƙwato shanu biyu, awaki 29 da raguna daga hannun manoman da ake zargi sun ƙwace daga hannun makiyaya.

A yanzu haka, an gayyaci shugabannin ɓangarorin biyu domin tattaunawa da kuma tabbatar da cewa irin wannan rikici bai sake faruwa ba a nan gaba.

Duk ƙoƙarin da wakilin Aminiya ya yi don jin ta bakin kakakin ‘yan sandan jihar, DSP Dungus Abdulkareem, ya ci tura, domin bai daga wayarsa ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukuma Ta Haramta Bikin Ranar Kauyawa A Kano
  • Rikici Tsakanin Faransa Da Aljeriya Ya Shiga Wani Sabon Salo Na Koran ‘Yan Kasashen Juna Daga Kasashensu
  • Tinubu zai halarci rantsar da sabon Fafaroma Leo
  • Tinubu ya ƙaddamar da jirage 2, ya buƙaci a kawo ƙarshen matsalar tsaro
  • Mutum ɗaya ya rasu a rikicin manoma da makiyaya a Yobe
  • Layya: Farashin raguna na iya tashin gwauron zabo
  • NAJERIYA A YAU: Shin Jam’iyyar NNPP Za Ta Kai Labari A 2027?
  • Tsaro: Tinubu ya ƙaddamar da rundunar tsaron daji a faɗin Najeriya
  • NAJERIYA A YAU: Kuskuren JAMB Da Ya Haddasa Faduwar Ɗalibai A Jarabawa