Tinubu ya isa Rome don rantsar da sabon Fafaroma
Published: 17th, May 2025 GMT
Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya isa birnin Rome na Ƙasar Italiya domin halartar bikin rantsar da sabon Fafaroma, Leo na XIV.
Za a gudanar da bikin ne a wajen wani taron addu’a da ake kira “solemn mass” a ranar Lahadi, 18 ga watan Mayu.
Crystal Palace ta lashe kofin FA na farko a tarihinta Ban sauya sheƙa ba, makircin siyasa da ƙarya ake min — KwankwasoAn tarbi Shugaba Tinubu a filin jirgin sojin Mario De Bernardo, inda jakadiyar Najeriya, Bianca Odumegwu-Ojukwu, da jami’an diflomasiyya daga Vatican da ofishin jakadancin Najeriya suka tarbe shi.
Tinubu ya samu gayyata ta musamman daga Sakatare Janar na Vatican, Cardinal Pietro Parolin.
A cikin wasiƙar gayyatar, Fafaroma Leo XIV ya bayyana cewa ya ga dacewar Shugaba Tinubu ya halarci bikin rantsar da shi.
Fafaaroma ya ƙara da cewa Najeriya tana da muhimmanci a gare shi domin ya taɓa aiki a ofishin jakadancin Vatican da ke Legas a shekarun 1980.
Shugaba Tinubu na tare da wasu manyan shugabannin cocin Katolika daga Najeriya ciki har da Archbishop Lucius Ugorji na Owerri, Archbishop Ignatius Kaigama na Abuja, Archbishop Alfred Martins na Legas, da Bishop Mathew Hassan Kukah daga Sakkwato.
Sun tafi Rome ne, domin nuna goyon baya da wakiltar Najeriya a bikin rantsar da sabon Fafaroma.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Bikin Rantsuwa Fafaroma Leo Sabon Fafaroma
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu Ya Ceto Nijeriya Daga Faɗawa Matsin Tattalin Arziƙi – Gwamna Namadi
A cewarsa, shuwagabancin Tinubu ya gina tubalin ci gaba mai ɗorewa ta hanyar yanke hukunci masu wahala amma masu amfani.
Dangane da sauyin jam’iyyun siyasa da ke faruwa, Namadi ya ce yawaitar sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC alama ce da ke nuna yadda jama’a ke ƙara amincewa da shugabancin Tinubu da kuma burin da yake shi ga ƙasar nan.
Ya ce masu barin jam’iyyunsu suna haka ne domin suna ganin makoma mai kyau a ƙarƙashin jagorancinsa.
Har ila yau, Namadi ya bayyana cewa ziyarar aikin da ya kai Indiya kwanan nan ta samar da muhimman yarjejeniyoyi da masu saka jari da ƙwararru don bunƙasa harkar noma a Jihar Jigawa.
Ya ce an cimma matsaya a fannoni irin su kiwon shanu, kiwon kaji da samar da ingantattun iri, wanda zai ƙara samar da ayyukan yi, tsaro na abinci, da kuma ɗora Jigawa zuwa cibiyar noma ta ƙasa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp