Yau Kotun ICJ ke yanke hukunci kan zargin da Khartoum ke wa UEA
Published: 5th, May 2025 GMT
Yau Litinin ne kotun kasa da kasa ta ICJ za ta yanke hukunci kan karar da Sudan ta shigar kan Hadaddiyar Daular Larabawa.
Khartoum ta kai karar UAE a gaban kotun kasa da kasa da ke birnin Hague, inda ta zarge ta da hannu wajen kisan kiyashin da ake yi wa al’ummar Masalit, sakamakon zarginta da goyon bayan dakarun (RSF) da suka shafe shekaru biyu suna yaki da sojojin Sudan.
Khartoum na zarginsu da kasancewa masu goyan bayan kisan kare dangi” da ake ci gaba da yi wa al’ummar Massalit na Darfur, saboda zarginsu da goyon bayan dakarun gaggawa na Janar Hemedti (RSF).
Khartoum na fatan alkalan kotun su umurci Hadaddiyar Daular Larabawa da ta daina goyon bayan kungiyar RSF, da kuma cewa suna bukatar ta biya “diyya” ga wadanda rikicin ya rutsa da su.
Rahotanni da dama daga kungiyoyi masu zaman kansu da kwararru na Majalisar Dinkin Duniya sun yi nuni da goyon bayan da Hadaddiyar Daular Larabawa ke baiwa kungiyar RSF, musamman ta hanyar shigar da makamai.
Amma Masarautar ta musanta hannu a wannan rikicin.
rikicin na Sudan da ke gudana tun a ranar 15 ga Afrilu, 2023 tsakanin sojoji na yau da kullun, karkashin jagorancin Abdel Fattah al-Burhan, da FSR, karkashin jagorancin tsohon mataimakinsa Mohamed Hamdane Dogolo, wanda aka fi sani da “Hemedti,” ya yi sanadin mutuwar dubunnan mutane a Sudan, sannan ya raba mutane miliyan 13 da muhallansu, wanda ya haifar da “daya daga cikin mafi munin yanayi a duniya”.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: goyon bayan
এছাড়াও পড়ুন:
Za a kashe biliyan 712.26 don yi wa filin jirgin saman Legas garanbawul
Majalisar Zartarwa ta Kasa ta amince da kashe Naira biliyan 712.26 don yi wa wani sashe na filin jirgin saman a Murtala Muhammad da ke Legas garambawul.
Hakan dai ya biyo bayan zaman majalisar wanda Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya jagoranta a Abuja ranar Laraba.
NAJERIYA A YAU: Me dokar kasa ta ce kan karin wa’adin aiki da Shugaban Kasa ke yi? Za a fara yi wa ɗaliban jami’o’i gwajin ƙwaya — Gwamnatin NijeriyaAikin dai wani bangare ne na Naira biliyan 900 da aka ware domin inganta harkokin sufurin jiragen sama a fadin Najeriya.
Ministan Harkokin Sufurin Jiragen Sama, Festus Keyamo ne ya bayyana hakan jim kadan da kammala taron majalisar, inda ya ce tuni har an ba da kwangilar aikin ga kamfanin gine-gine na kasar China (CCECC).
A cewar Ministan, aikin ya kuma kunshi canza kayayyakin da ake amfani da su a wurin saukar jirage na filin daga na da zuwa na zamani.
Keyamo ya kuma ce majalisar ta kuma amince a kashe Naira biliyan 49.9 wajen aikin katange filin jirgin na Legas domin a inganta tsaro a cikin shi,
Katangar mai tsawon kilomita 14.6 wacce ta karfe ce, za kuma a saka mata na’urori a jikinta da kyamarorin CCTV da fitilu masu amfani da hasken rana da kuma tituna a gefenta.
“Duk wanda ko kuma duk abin da ya rabi katangar za mu gan shi cikin gaggawa sannan a nuna wajen da yake,” in ji Minista Keyamo.