HausaTv:
2025-06-19@21:03:47 GMT

Yau Kotun ICJ ke yanke hukunci kan zargin da Khartoum ke wa UEA

Published: 5th, May 2025 GMT

Yau Litinin ne kotun kasa da kasa ta ICJ za ta yanke hukunci kan karar da Sudan ta shigar kan Hadaddiyar Daular Larabawa.

Khartoum ta kai karar UAE a gaban kotun kasa da kasa da ke birnin Hague, inda ta zarge ta da hannu wajen kisan kiyashin da ake yi wa al’ummar Masalit, sakamakon zarginta da goyon bayan dakarun (RSF) da suka shafe shekaru biyu suna yaki da sojojin Sudan.

Khartoum na zarginsu da kasancewa masu goyan bayan kisan kare dangi” da ake ci gaba da yi wa al’ummar Massalit na Darfur, saboda zarginsu da goyon bayan dakarun gaggawa na Janar Hemedti (RSF).

Khartoum na fatan alkalan kotun su umurci Hadaddiyar Daular Larabawa da ta daina goyon bayan kungiyar RSF, da kuma cewa suna bukatar ta biya “diyya” ga wadanda rikicin ya rutsa da su.

Rahotanni da dama daga kungiyoyi masu zaman kansu da kwararru na Majalisar Dinkin Duniya sun yi nuni da goyon bayan da Hadaddiyar Daular Larabawa ke baiwa kungiyar RSF, musamman ta hanyar shigar da makamai.

Amma Masarautar ta musanta hannu a wannan rikicin.

rikicin na Sudan da ke gudana tun a ranar 15 ga Afrilu, 2023 tsakanin sojoji na yau da kullun, karkashin jagorancin Abdel Fattah al-Burhan, da FSR, karkashin jagorancin tsohon mataimakinsa Mohamed Hamdane Dogolo, wanda aka fi sani da “Hemedti,” ya yi sanadin mutuwar dubunnan mutane a Sudan, sannan ya raba mutane miliyan 13 da muhallansu, wanda ya haifar da “daya daga cikin mafi munin yanayi a duniya”.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: goyon bayan

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisa ta aike wa Tinubu kudurorin dokar haraji domin ya rattaba musu hannu

Majalisar Dokoki ta kasa ta ce ta aike wa Shugaban Kasa Bola Tinubu kudurorin dokar harajin da ta amince da su a hukumance domin ya rattaba musu hannu su zama doka.

Shugaban Kwamitin Yada Labarai na Majalisar Dattawa, Sanata Yemi Adaramodu (APC, Ekiti) ne ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai ranar Talata a Abuja.

A bara ne dai Tinubu ya aike wa majalisar kudurorin domin su yi nazarinsu sannan su amince da su a matsayin doka.

Ambaliyar Mokwa: Har yanzu muna neman mutum 700 – Gwamnatin Neja DAGA LARABA: Ko Kare Kai Daga Harin ‘Yan Ta’adda Zai Kawo Karshen Matsalar Tsaro?

Kudurorin dai a baya sun yamutsa hazo sosai a zaurukan majalisun da ma a fadin kasa, kafin daga bisani majalisun na wakilai da dattawa su amince da su.

Sanata Yemi ya ce, “Eh, yanzu kudurin ya bar hannunmu, yana kan hanyarsa ta zuwa wajen Shugaban Kasa domin ya sanya masa hannu ya zama doka.

“Kudurorin haraji irin wadannan suna bukatar taja da tsifa sosai. Dole bangarorin masana shari’a na zaurukan majalisun biyu su tabbatar kudurorin sun yi daidai da dokokin da ake da su a kasa kafin su tura wa Shugaban Kasa.

“Ba aiki ba ne na kwana biyu ko uku. Bayan an kammala aikin daidaita su kuma Akwun Majalisar Dokoki ta Kasa zai mayar da su kundi daya. Bayan haka ne kawai Shugaban Majalisar Dattawa da ta Wakilai za su sa hannu a aike da su,” in ji Sanatan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Nan da mako biyu za mu yanke shawara kan shigar wa Isra’ila yaƙi — Trump
  • Gwamnatin Tarayya Ta Gurfanar Da Natasha A Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Akpabio Da Yahaya Bello
  • Kotu ta ba da belin Natasha kan N50m kan zargin bata sunan Akpabio
  • Kotun Amurka ta daure ’yan Najeriya 5 shekaru 159 kan aikata damfara
  • An ɗaure mutum 7 kan yi wa ɗan sanda rauni a Kano
  • Sin Za Ta Samar Da Cibiyar Kasa Da Kasa Ta Gudanar Da Hada-hadar Kudin RMB Na Dijital
  • EFCC Ta Kama Tsohon Kakakin Majalisar Filato Da Wasu ‘Yan Majalisa 14 Bisa Zargin Almundahana
  • Majalisa ta aike wa Tinubu kudurorin dokar haraji domin ya rattaba musu hannu
  • An Kama Mutane 26 Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Kogi
  • Rikicin ƙabilanci ya yi ajalin mutum 20 a Chadi