HausaTv:
2025-05-05@14:22:27 GMT

Yau Kotun ICJ ke yanke hukunci kan zargin da Khartoum ke wa UEA

Published: 5th, May 2025 GMT

Yau Litinin ne kotun kasa da kasa ta ICJ za ta yanke hukunci kan karar da Sudan ta shigar kan Hadaddiyar Daular Larabawa.

Khartoum ta kai karar UAE a gaban kotun kasa da kasa da ke birnin Hague, inda ta zarge ta da hannu wajen kisan kiyashin da ake yi wa al’ummar Masalit, sakamakon zarginta da goyon bayan dakarun (RSF) da suka shafe shekaru biyu suna yaki da sojojin Sudan.

Khartoum na zarginsu da kasancewa masu goyan bayan kisan kare dangi” da ake ci gaba da yi wa al’ummar Massalit na Darfur, saboda zarginsu da goyon bayan dakarun gaggawa na Janar Hemedti (RSF).

Khartoum na fatan alkalan kotun su umurci Hadaddiyar Daular Larabawa da ta daina goyon bayan kungiyar RSF, da kuma cewa suna bukatar ta biya “diyya” ga wadanda rikicin ya rutsa da su.

Rahotanni da dama daga kungiyoyi masu zaman kansu da kwararru na Majalisar Dinkin Duniya sun yi nuni da goyon bayan da Hadaddiyar Daular Larabawa ke baiwa kungiyar RSF, musamman ta hanyar shigar da makamai.

Amma Masarautar ta musanta hannu a wannan rikicin.

rikicin na Sudan da ke gudana tun a ranar 15 ga Afrilu, 2023 tsakanin sojoji na yau da kullun, karkashin jagorancin Abdel Fattah al-Burhan, da FSR, karkashin jagorancin tsohon mataimakinsa Mohamed Hamdane Dogolo, wanda aka fi sani da “Hemedti,” ya yi sanadin mutuwar dubunnan mutane a Sudan, sannan ya raba mutane miliyan 13 da muhallansu, wanda ya haifar da “daya daga cikin mafi munin yanayi a duniya”.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: goyon bayan

এছাড়াও পড়ুন:

An Kama Wani Ɗan Ghana Bisa Zargin Kai Mata Hajji Ba Tare Da Lasisi Ba

Rundunar tsaron dake lura da aikin Hajji ta kama wani ɗan ƙasar Ghana bisa zargin ƙoƙarin fitar da mata huɗu daga ƙasashen waje zuwa Makkah ba tare da lasisin Hajj ba.

Matan, waɗanda ke cikin mota, an yi amfani da ɗakin kaya na motar domin ɓoye su don gujewa dokokin Hajj.

Gwamnatin Katsina Ta Sauya Masu Yi Wa Alhazai Hidima A Saudiyya Maniyyata Daga Turai Akan Dawakai Sun Isa Kasar Saudiyya Domin Yin Aikin Hajjin 2025

Rundunar tsaron ta kama direban motar tare da mata huɗun, sannan aka miƙa su ga hukumar da ta dace don aiwatar da hukuncin doka.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kotu za ta rataye matashi kan kisan karuwa
  • Umaru ’Yar’adua da shugabannin Najeriya da suka rasu a kan mulki
  • Iran ta watsi da zargin Isra’ila da Amurka cewa ta na da hannu a harin ramuwar gayya na Yemen
  • An Kama Wani Ɗan Ghana Bisa Zargin Kai Mata Hajji Ba Tare Da Lasisi Ba
  • Iran Ta Jaddada Cewa: Kungiyoyin Gwagwarmaya Ba Su Karbar Umarni Daga Wani Bangare, Gashin Kansu Suke Ci
  • Sojojin Sudan Da ‘Yan Tawayen Kasar Suna Ci Gaba Da Gwabza Fada A Wasu Saasan Kasar
  • Tsohon Shugaban NNPC, Kyari Ya Musanta Zargin Faɗawa Tarkon EFCC
  • Dakarun Kai Daukin Gaggawa Sun Kashe Fararen Hula Kusan 300 A Hare-Haren Baya-Bayan Nan A Sudan
  • Seyi Tinubu Ya Musunta Zargin Kamawa Da Bayar Da Cin Hanci Ga Shugaban NANS