Sojojin Sudan Da ‘Yan Tawayen Kasar Suna Ci Gaba Da Gwabza Fada A Wasu Saasan Kasar
Published: 5th, May 2025 GMT
Ana ci gaba da gwabza kazamin fada a yammacin Sudan tsakanin sojojin Sudan da dakarun kai daukin gaggawa na kasar
Jiragen saman yaki marasa matuki ciki na dakarun kai daukin gaggawa sun kai hare-hare kan sansanin sojin sama na Osman Digna da ke gabashin Sudan, inda suka janyo bullar gobara a ma’ajiyar harsasai.
A yammacin Sudan na ci da wuta tare da hare-haren jiragen saman yaki marasa matuka ciki da kuma luguden harsasai, kuma sojojin sun janye daga yankin Nahud da ke yammacin Kordofan, kafin nan gaba su sake dawowa, kamar dai yadda suka yi a jihar Al-Jazirah da ke tsakiyar Sudan, a cewar wata majiyar soji.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kungiyar AU Ta Yi Watsi Da Kafa Gwamnatin Adawa Da Kungiyar RSF Ta Yi A Sudan
Jim kadan bayan da kungiyar kai Dauki Gaggawa ta kasar Sudan ta sanar kafa gwamnatin mai mambobi 15, kungiyar tarayyar Afirka ta mayar da martanin kin amincewa da ita.
Bugu da kari kingiyar ta tarayyar Afirka ta kira yi kasashen da suke mambobi a cikinta da kuma kungiyoyin kasa da kasa da kar su amince da halarci wannan gwamnatin.
Har ila yau kungiyar ta tarayyar Afirka ta kuma yi gargadin cewa matakin da kungiyar ta RSF ta dauka zai iya tarwatsa Sudan ya kuma rusa Shirin zaman lafiya wanda dama yana tangal-tangal.
Kungiyar ta RSF ta bayyana Muhammad Hassan al-Ta’aysh a matsayin Fira ministan, sai kuma Janar Muhammad Dagalo a matsayin shugaban kasa.
Kasar Sudan ta fada cikin yaki ne tun a 2023 a tsakanin sojoji da rundunar kai daukin gaggawa RSF.
Sojojin kasar dai su ne ke iko da babban birnin kasar Khartum da kuma mafi yawancin yankin Arewacin kasar, gabashinta da kuma tsakiyarta. Ita kuwa kungiyar RSF tana iko da yankin Darfur da wani sashe na Kurdufan.
Kungiyar ta tarayyar Afirka ta bayyana cewa, kafa gwamnatin adawa a Sudan zai kara zurfin matsalar da ake fama da ita, kuma baranza ce ga fatan da ake da shi na kawo karshen rikicin.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Shugaban Kasar Iran Zai Ziyarci Pakistan A Gobe Asabar August 1, 2025 Habasha Ta Kaddamar Da Shirin Shuka Bishiyoyi Miliyan 700 A Rana Daya August 1, 2025 Sayyid Abdulmalik Husi: Taimakon Da Ake Jefawa Gaza Ta Sama Yaudara Ce August 1, 2025 Amurka Ta Kakabawa Jami’an Gwamnatin Falasdinawa Takunkuman Hana Shiga Amurka July 31, 2025 Ministan Harkokin Wajen Siriya Yana Rasha Don Bude Sabon Shafi Tsakaninsu July 31, 2025 Kananan Yan Wasan Dabben Gargajiya Na Iran Sun Zama Zakara A Gasar Wannan Shekara July 31, 2025 Canada Zata Amince Da Samuwar Kasar Falasdinu A Taron MDD July 31, 2025 Shugaban Kasar Lebanon Aun Ya Ce Mun Aike Wa Amurka Sakwanni Akan Dakatar Da Hare-haren HKI July 31, 2025 Sojojin Mamaya Suna Ci Gaba Da Kisan Kiyashi A Gaza July 31, 2025 Kassim: Duk Wanda Yake Neman Hizbullah Ta Ajiye Makamanta Yana Yi Wa Isra’ila Aiki July 31, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci