Sojojin Sudan Da ‘Yan Tawayen Kasar Suna Ci Gaba Da Gwabza Fada A Wasu Saasan Kasar
Published: 5th, May 2025 GMT
Ana ci gaba da gwabza kazamin fada a yammacin Sudan tsakanin sojojin Sudan da dakarun kai daukin gaggawa na kasar
Jiragen saman yaki marasa matuki ciki na dakarun kai daukin gaggawa sun kai hare-hare kan sansanin sojin sama na Osman Digna da ke gabashin Sudan, inda suka janyo bullar gobara a ma’ajiyar harsasai.
A yammacin Sudan na ci da wuta tare da hare-haren jiragen saman yaki marasa matuka ciki da kuma luguden harsasai, kuma sojojin sun janye daga yankin Nahud da ke yammacin Kordofan, kafin nan gaba su sake dawowa, kamar dai yadda suka yi a jihar Al-Jazirah da ke tsakiyar Sudan, a cewar wata majiyar soji.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun ‘Yan Bindiga
Sun bayyana cewa akwai hatsarin ganin wasu daga cikin waɗanda suka tuba su koma yin laifi, idan gwamnati ba ta yi hattara ba.
Sun kuma jaddada cewa dole ne a tallafa wa iyalan da suka rasa ‘yan uwa da dukiyoyinsu a harin ‘yan bindiga, domin ka da su ji kamar gwamnati na goyon bayan masu laifi.
Jihar Katsina na daga cikin jihohin Arewa Maso Yamma da ke fama da hare-haren ‘yan bindiga, wanda ya haddasa mutuwar mutane da dama da kuma salwantar dukiya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp