Sojojin Yemen sun sanar da killace sararin samaniyar Falasdinawa da yahudawan sahayoniyya suka mamaye

Sojojin Yemen sun sanar a yammacin jiya Lahadi cewa: Za su kakaba wa haramtacciyar kasar Isra’ila cikakken takunkumi ta sama, yayin da kamfanonin jiragen sama na kasa da kasa suka yi gargadin hadarin da ke tattare da zirga-zirga daga filayen jiragen saman yankunan Falasdinawa da aka mamaye.

Wannan dai na zuwa ne a matsayin martani ga karuwar hare-haren da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ke kai wa a zirin Gaza.

Kakakin rundunar sojin Yemen, Birgediya Janar Yahya Sari’e, ya ce za su kakaba takunkumin ne ta hanyar kai hare-hare akai-akai kan filayen jiragen saman haramtacciyar kasar Isra’ila, musamman filin jirgin sama na Ben Gurion.

Sanarwar ta yi gargadi ga dukkan kamfanonin jiragen sama na kasa da kasa kan hadarin da ke tattare da hakan, inda ta yi kira gare su da su “soke dukkan tafiye-tafiyen jiragen da ke zuwa filayen jiragen sama na gwamnatin ‘yan mamaya masu tafka muggan laifuka domin kare lafiyar jiragensu da na kwastomominsu.”

Birgediya Janar Sari’e ya jaddada cewa: Kasar Yemen ba za ta amince da ci gaba da keta hurumin da makiya ke kokarin aiwatarwa ta hanyar kai wa kasashen larabawa irinsu Lebanon da Siriya hari ba, yana mai jaddada cewa “wannan al’ummar ba za ta ji tsoron bullar duk wani fada ba, kuma za ta ki mika wuya da rusuna wa azzalumai.”

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: jiragen sama

এছাড়াও পড়ুন:

Ba zai yiwu mu bar Khamenei a raye ba — Isra’ila

Ministan Tsaron Isra’ila, Israel Katz ya ce ba zai yiwu su bar jagoran addinin Iran, Ayatollah Ali Khamenei a raye ba.

Israel Katz ya yi barazana ga Ayatollah yana mai cewa ya zama tilas ya ɗauki alhakin hare-hare da makamai masu linzami da Iran ta yi a kan wata cibiyar lafiya da ke kusa da Tel Aviv.

Hisbah ta lalata katan 243 na barasa da wasu kayan maye a Yobe Guguwar ruwan sama ta yi ɓarna a Kwalejin Kimiyya da Fasaha a Kogi

Kafin harin an yi ƙoƙari kwashe marasa lafiya da dama, saboda a ceto rayukansu.

Tuni dai Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya ziyarci Cibiyar Lafiya ta Soroka da ke Beersheba da harin makami mai linzami na Iran ya faɗawa.

Sai dai ita kuma Iran din ta ce ta kai harin ne kan sansanin sojoji da ke kusa da asibitin.

Kalaman Mista Katz na nuna cewa sojojin Isra’ila a yanzu za su yi ƙoƙarin ganin sun kashe Ayatollah — bayan kashe kwamandojinsa na soji da dama.

A makon da ya gabata ne Isra’ila ta ƙaddamar da hare-hare ta sama kan babbar abokiyar gabarta a yankin Gabas ta Tsakiya Iran, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar manyan kwamandojin sojin ƙasar, tare da lalata wasu cibiyoyin nukiliyata da kuma kashe fararen hula da dama.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ba zai yiwu mu bar Khamenei a raye ba — Isra’ila
  • Sin Ta Fadada Matakin Rage Haraji Ga Kasashe Masu Raunin Tattalin Arziki
  • Guguwar ruwan sama ta yi ɓarna a Kwalejin Kimiyya da Fasaha a Kogi
  • Za a dawo da dukkan Alhazai gida ranar 28 ga Yuni – NAHCON
  • Sin Za Ta Samar Da Cibiyar Kasa Da Kasa Ta Gudanar Da Hada-hadar Kudin RMB Na Dijital
  • Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta
  • Tinubu Ya Kai Ziyara Benuwe Sakamakon Kisan Kiyashi Da Aka Yi Wa Jama’a
  • Sojoji sun raunata shugaban ISWAP na Najeriya, Albarnawi
  • An garzaya da ’yan Isra’ila 154 asibiti bayan harin Iran
  • Yaƙin Iran da Isra’ila: Amurka za ta tura jami’anta don tattaunawa da Tehran